← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 83 OF 160

Sashe 83

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Anas ya   k'arasa  maganar
a lokacin da  zahra  Ke k'okarin  kai   hannunta  qirjin jaguwa
yay saurin    rike hannunta  had'e da tureta  ya duro da  sauri  ya  qarasa  bakin kofa   ,ya  murda  handle  ga mamakinsa  kofar  a bud'e take,  ya  murda  key  ya  zare   ya   juyo  ya  tsura mata rikitattun idanunshi  yana dubanta   zuciyarsa na buguwa da karfi tare da karkarwa   .
cike  da  faduwar gaba ya
dauke  kwayar idanunshi akanta ya k'arasa  jikin  bangon d'akin  ya  manne  domin  'bacewa .
hankalin zahra yayi matukar tashi    domin   tasan  bacewa zai yi  da zarar ya bace kuma shikenan ta rasa damarta km  bata san sanda zata sake samu  wata damar ba, sai dai ganin  ya  gagara ' bacewa yasa tayi sanyaye murmushi a boye   dadi ya kamata Kenan har yanzu tana da sauran dama ,dan haka  duk yadda zatai sai tayi ta  yaudaresa ya shiga hannu taso ma su samesa yana  bacci amman Ko yanzu bata  baci ba zata yi iya yinta tunda ya kasa bacewa ."

da  sauri  ya shiga bathroom rike da key ya ajiye ya fara sakarwa kansa ruwa had'e da wanka tsarki zuciyarsa na cigaba da tsinkewa    da faduwa  ,haushin kansa ya kamashi "me yasa   ya   biyewa son zuciyarsa  har ya sake kusantar zahra a rayuwarsa  ? " yayiwa Kansa tmbyr cikin tsananin jin haushin kansa tsaki   yaja yana furzar da iska mai zafi  daga bakinsa yana tunanin   hanyar  da zai bi ya kubuta kafin rutsa shi .
Cike da matsanancin tashin hankali ya sake  manna jikinsa da bangon bayi amman  bango  yaki amsar   tsantsar  jikinsa,   yayi  yayi  ya kasa 'bacewa  "matsala ta fara  faruwa Kenan ya furta a fili yana sake gyara tsayuwarsa ya tsaya saitin shawa ruwa na sauka ajikinsa . "lallai lokaci nemo  yarinya  mai  taurari  yayi dan  dole  na ajiye  wasu abubuwana  na shiga gari nemanta , yana   tsaye ruwa na sauka ajikinsa zahra  ta shigo cike da karairaya tana  karewa sansar jikinsa kallo most especially  joystick dinsa data fi qauna   tana  lasar lips dinta na kasa Kamar wata tsohuwar mayya.
bata tsaya wata wata ba ta shiga cikin  bathtub din ta shige jikinsa ,finciketa yayi ta karfi  amman ta makale ajikinsa yayi baya kad'an , ta kwanto jikinsa tasa hannu ta tallafo fuskarsa tana furta "me yasa kake wanka nifa ban  koshi  ba"? tayi mgnr cikin salo da tsigar yaudara .
tsaki  ya ja ya damke hannunwanta duka ya turata baya har sai data buge kugunta  ta  saki   qara  mai sauti tana Kiran ouchi ..."
  Yaja dogon tsaki  "idan kika sake kuskuren fad'a min cewar baki koshi ba  ko wani  abu mai kama da  shirmen haukanki  din nan  zaki ga yadda zanyi dake very stupid Kawai ".  ya k'arasa maganar tare da d'aukar key ya fito ya  soma goge jikinsa .
ta fito rike da kugunta tana shafa daidai inda  ta buge , da kyar ta zauna tana dubansa Kamar zata cinyesa amman rashin son da bai mata yasa ita kuma sai taga karshensa.
sautin muryar yaji a hankali tana cewa "ni bana wani shirmen hauka ,ka kwana kana cina ka juyani son ranka duk baka ji haushi ba sai yanzu dan nace bankoshi ba ?" ai haushin kanka ya kama kaji ba haushina ba tunda ba d'aure ka nayi ba da ka ..."enough zahra karki tunzira zuciyata na miki wulakanci ya fad'a a tsawace ya juya mata baya yana k'okarin saka kayansa ,ita kuma ta koma ta kwanta ruf da ciki  tana tunanin abun yi  ."

ganin bata da niyyar  fita  ta barshi yasan yadda zai tsere yace  "ki  tashi  ki kama gabanki  ta  juyo a hankali  ta  kalleshi ranta a bace  kmr  zatayi kuka tace "Ai  ni  na kama  d'akin". "okay  ni  ya  kamata Kenan  na fita na  bar miki ba"?  ya fad'a  yana maida  botiran gaban rigrsa a hankali ta mike  still babu kaya ajikinta ta sauko  tana dubansa ,   jikin  window  d'akin  ya  Koma  ya yaye labule  dakin  yana kallon haraban hotel din  "tabbas maganar Anas gsky ne  police  da security  da yan jarida ne  cike  da  haraban   hotel  din,
ya  furzar da iska mai zafi daga bakinsa  tare da rike  kugunsa da hannunsa d'aya  yana mata kallon tunhuma sannan   yasa   kai  zai fita daga  d'akin tace   " dan Allah  minti  biyu Kawai ".  ya tsaya batare  daya  juyo ba.

a natse ta dawo gabansa suna fuskantar  juna  "me yasa  Adnan  "? me yasa baka sona "?
"Kawai bana sonki  "ya fad'a a takaice cikin tsananin bacin rai . ta runtse idanunta tana jin wani irin zafi aranta, Idan akwai abinda ta tsana bai wuce ya furta mata baya sonta ba ,haka nan taji hawaye  na bin kuncinta murya a sanyaye ta fara mgn ". gani  ni  kuwa  Ina mutuwar sonka ina maka son da   ..." .
Saurin daga mata hannu yayi ta hanyar dakatar daita yana cewa
"dan Allah malam ki barni haka kina damuna da surutu ya fad'a yana sake jan tsaki yasa hannu ya tureta gefe yana cewa "duk abinda kika yi dan ki cutar dani  kice  zaki kwana aciki dan bazaki ci riba ba, ya  kai hannunsa ya rike handle yana Shirin murda key  ya ji muryarta cikin kunnensa ".

"ka dan jirkirta  karka  fita yanzu  domin  fitarka yanzu akwai  damuwa "ta fada  batare data shirya fad'a hkn  ba ,haka nan ta tsinci Kanta da fadar haka  , bama ta san ya'akayi kalmar damuwa tazo bakinta ba .
ya juyo gbdy ya tsura mata rikitattun idanunshi yana kallonta "me  kika ce ?" take jikinta ya kama rawa da kafafunta ganin yadda yake kallonta gbdy ta rikice ta dimauce tayi data sani "
a sukwane ya dawo suna fuskantar juna "uhmmm ina jinki "tayi shiru ta kasa mgn dan bata san me zatace ba dan tana bud'e baki zata fad'a masa komai saboda ita kam bata iya karya ba .
"Bazakiyi magana ba ya fad'a tare da damkar makoshinta nan take idanunta suka yi kulu kulu tsabar matsa ,da kanta ta dinga masa alamar zata fada.
ya sakar mata wuya yana filinging daita tayi taga taga ta dafe bangon d'akin ta tsaya bisa kafafunta tana huci da kyar ta
d'aga  hannuta  tana  cewa "uhm ...uhmm akwai  damuwa banason  ka fuskanci matsala  idan ka fita yanzu  police zasu iya attacking  dinka."
"Uhmmm ai ya  kamata  kiso  hakan ,tunda  shine burinki   na wulakanta   ?"
"wallahi  a'a,  kullum  Ina  maka addua   Allah ya tsareka  ". ta fad'a a rude muryarta na rawa .

"akan me Kenan  kike min addua ? "akan alqalla fashin  da  kake  ta sake subutar baki  dan sam bata iya karya ba ,koda ake cewa duk wanda yabi maza zai yi karya ,zai yi sata zahra bata iya karya ba sannan bata sata barta dai da bin maza suma masu lasisi manya mutune manyan yan siyasa da manyan kusoshin gwanati " .
yayi shiru  Kawai  yana cigaba da sauraronta tare da nemna Karin bayani  "shiru tayi jikinta na sake d'aukar  rawa gbdy ta daburce ta dawo tamkar wawiya  agabansa "na  shiga  uku meye haka nake yi  ? "
"me yasa na fad'a masa nasan sana'arsa  ,ba abinda ya kawoni Kenna ba , dan dole na nemawar kaina mafuta tun kafin ya sake shakeni  na mutu .
Kamar tsohon maye yake kallonta kafin a hankali yace "Kafarki ba a kasa take ba ki ajiyeta a kasa da kyau kiyi min bayani  a ina kika san alqallata?

Muryarta cike da in Inna tace "Uhmmm ...ammm  sai Kuma tayi shiru ta kasa cigaba da magana wata hadadiyar tsawa ya buga mata yana sake tambayeta jikinta na rawa ta soma mgn " nasan kana  yi sana'ar   fashi ne  agurin  dcp   ,nan  ta kwashe komai  ta zayane  masa  a karshe tace "yanzu nasan   bibiyeta  suke domin  su samu damar  kamaka".ta hada da Karya dan kar ya fahimci komai ..
"Ke ya'akayi kikasan suna  waje  yanzu"?  "wayar da kayi  da anas  naji  komai gbdy sai  tunanina ya bani ni suke  bibiya domin su samu damar kamaka  .
kallonta  yayi  a d'age yana ta'be baki ,bani zaki rainawa hankali ba ,kanki zaki rainawa hankali an hada baki dake ba, dan Akamani Shine Allah ya matsi bakinki Ko?"
"To kisani bani da bakin uwa yadda na shigo lafiya haka zan fita lfy , "a'a ka tsaya ka fahimceni na yita  kiranka domin na fad'a  maka  komai dake faruwa kasan matakin da zaka d'auka  amman kaki d'aukar wayata ."to yanzu  ya ake ciki malama zahra ?ya sake  tambayeta a d'age   yana sauke numfashi a boye dan gbdy ya gama ganota itace ma tabasu number wayarsa da yake zargin abokansa da yaransa ne."
  "burinsu su kamaka  dan  Allah ka fahimceni  Ina sonka zan  iya   auranka da wannan  sana'ar da kake  zan  taimaka maka akan sana'arka  ta  yadda  zaka  cigaba  da  samun nasarori   sannan kayi nasara  akan polisawa dake son ganin bayanka ."
  tsaki  yaja  yana cewa "baki  da  hankali,  Karki d'auka dan  kinsan Ko ni waye  zai sa ki samu abinda  kike so  agurina a'a babu wannan damar Idan kin  ga dama ki had'a kai   dasu ,Ko kuma ince ki qara hada kai dasu ba damuwata bace zasuyi amfani dake ne abanza akarashe kece zaki kwana ciki    ya karasa magana  yana  sake juyawa   yasa  kai zai   ya fita  daga d'akin ."
"Wayyolhhly  Allah Adnan  why please wallahi  Ina sonka ka taimakeni  bazan iya cigaba da rayuwa babu kai ba na bar zunzurutun miliyoyi kudinn saboda qaunar da nake   ..."

"Karya kike munafukar Allah
"Ba dai saboda qaunar da kike min ba yasa kika bar damarki Allah ne ya tona asirinki ",karka ce haka please Ina sonka
"bani kike so ba kinsan abinda kike so ajikina ,me zai hana ki hakura dani , jijiyar  mazaje  nawa kika ci  duk  baki samu wacce tayi daidai  dake ba sai nawa  zaki  makalewa?" kudi Kuma ki Koma ki karba abunki idan zasu baki kenan ,domin yaudara acikin police kmr tare suka zo duniya ya  k'arasa  fita daga d'akin gbdy .
Hawaye take har sanda police suka banko kofar dakin suka shigo  tana  durkuahe a tsakiyar  d'akin tasa hannu ta janyo zanin gado ta rufe  jikinta tana zubar da ruwan hawaye.
Chapter 83 · 0% Book details