Sashe 120
Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
“babu amfanin iri irinku da ba’a amfana daku a kasarku sannan baku da adalci da kishin kasarku mutuwa ce tafi dacewa da kai domin kai kadai duniya ke son ganin mutuwarka dan haka ka kula da rayuwarka kamil ya karasa maganar yana daura masa bakin bindiga a daidai saitin qirjinsa inda kadan ya rage zuciyar alhji tajudeeni bata buga ba dan firgici.”
gbdy suka zagayesa suka sakashi a tsakiya jikinsa banda tsuma babu abinda yake wani gumi ya shiga tsatsafo masa a goshinsa da kan hancinsa “lallai yau ya dauko ruwan dafa kansa sannan ya hadu da gamonsa bai taba cin karo da rudani da firgici irin wannnan ba ,yau tazo masa da rikincin da bai taba tsintar kanshi aciki ba, iya girmansa daya samu karfin iko bai taba cin karo da tsagiran tantira irinsu ba sai yau .
“Ina karfin ikon naka yake? “ashe baka da ikon komai da karfi ka sanyo kafafunka cikin gidana? kamar yadda kake ganin kana da kwakwaluwa da baseera kashe wanda baka so,ko halaka wanda baka so ,ko batar da wanda baka son gani kasani tamu ta zarta naka ,idan kuma ka tsaya akan cewar karfin ikon da kake dashi zai kareka akoina to kayi babban kuskure domin zaka kasance mai yawon shiga rudani kuma babu abinda karfin ikon naka zai maka kamar yadda kake gani a yanzu saboda an fika da kaifin baseera .”
“Idan kuma da zuciyarka kawai ka dogara kasani nasararka ragaggiya ce saboda ita zuciya abinda yayi mata dadi kawai take aiyanawa a yanzu ma zan iya kasheka waye zai sani ? jaguwa ya tambayesa yana goge bakin bindigarsa tare da yi masa kallon kaskanci alhj tajudeeni yayi shiru jikinsa na wani irin karkarwa “Kasani mutane ire irenku basa amfanar da kansu da komai agaban irinmu idan kaje ka tambayi amininka zai maka qarin bayani akaina yanzu yanzu ka kama hanya ka fice min da gani ban san ganinka jeka…” ya fada tare da juyawa ya nufi ciki gbdy duk suka dare suka barshi tsaye cike da tsananin tashin hankali ya juya ya soma tafiya da kyar zuciyarsa na tafarfasa “. da sauri ajuwon ya biyo bayansa har suka kai bakin get ,bai tsaya jiran a bude masa murfin kofa ba ya bude ya shiga ya zauna yana huci .”
kwalkwaluwarsa ta toshe kansa ya cunkushe ya dinga zurfafa tunaninsa duk abinda suka fada babu wanda yafi tsaya masa a zuciya kamar ta mutumin da yaji ajuwon yace shine anas dashi kanshi jaguwa maganganunsu sunfi cakar masa zuciya da kwakwaluwa, ya rufe idanunshi ya jingina bayansa yana jujuya maganganunsu yana yin filla filla dasu yana neman wa kansa abinda zai musu ya halakasu “sam sam bazan barsu ba ,bazasu sha a banza ba ,sai na gina musu wani rami da zasu afka aciki amman bazan barsu ba har sai naga bayansu daya bayan daya har ya karasa office da wannan tunani ya karasa zuciyarsa kamar zata buga“.
Bayan tafiyar alhji tajudeeni jaguwa ya sauya kaya ya zauna ya janyo pillow ya rungume a qirjinsa yana nazarin maganar alhj tajudeeni yana son yatantance tabbacin abinda zai iya yi acikin maganganunsa wani bangaren na zuciyarsa yaji ya yarda alhji tajudeeni zai iya yin wani abu domin yaga bayansu yayinda wani zuciyar ke karfafa masa gwiwar cewar babu abinda zai yi nan take yayi accept da maganar kyakkyawar zuciyarsa babu
abinda zai yi .”
A natse anas ya turo kofar dakinsa ya shigo bai san ya shigo sai da ya dafashi sannan ya waigo yana sauke numfashi “karka takura kanka da tunani fa bazai iya komai ba zuciyarsa zataita tunanin abinda zai yi mana amman bazai iya komai ba ,wannnan gaskiy ne bazai iya ba amman duk da haka zamu sa hankalinmu akanshi shiyasa kullum da kake cewa mu ajiye makamammu nake cewa da kai aa nasan gaskiya kake fada min amman a yanzu bazan yarda da ita ba “ ya kamata ka yarda mu bari zan yi iyakar kokarina mu canza gbdynmu kuma inshaallahu zanyi nasara “ka kasa fahimtata ne anas barin wannan aiki yana da matukar hatsari sai muyi matukar shiri wanda bazai ruguje mana ba sannan ma idan zamu bari ya karasa mgnr yana cewa “ ya kake jin kan naka yanzu? ya fad’a ta hnayar katse maganar gbdy “har cikin kwayar idanuna nake ji ciwon kan amman maganr wancan banzar mutumin tasa na nemi ciwon kan na rasa jaguwa yayi murmushin gefen baki yana kokarin bude baki yaji ana knowking din kofa yasan cikin yaransa ne ya bada umarnin shigowa eku ya shigo rike da wayoyinsa daya na ringing aciki .
ya mika masa wacce take ringing din ya amsa yana dubawa number ya gani babu suna yana yawo akan screen din wayar shi kuma eku ya juya ya fice daga dakin ya dafe kanshi batare daya daga wayar ba anas ya matso kusa dashi “ka daga mana ko kiran ba mai mahimanci bane ? “number babu suna ! ya fad’a yana lumshe ido knowking suka sake ji anas yace “waye ?
“Nice !
Da saurin ya bude idanunshi sakamakon jin sautin muryarta ya kalli anas shima din kallonsa yake “na fad’a mata karta sake zuwa gidan nan me kuma ya kawota ?“Oho ai ka hadu da gamonka dan wannan yarinyar wallahi bazata koro ba kamar sauran matan daka saba kora ,ta zame maka karfen kafa mutu ka raba ya fad’a yana masa dariya kafin yayi wani hanzari har ta murda handle din kofar ta shigo ta tsaya tana dubansa da lulu eye’s dinta sanye take cikin doguwar rigar abaya yellow wanda akayiwa ado da flower ‘s baki haka yar cikinta baki ne ,hand bag da takalmi har ma da agogon dake daure a tsintsiyar hannunta baki ne tayi kyau matuka gbdy kamshin turarenta ya hade danashi ya gauraye dakin kamar ya tashi ya sureta yayi bedroom dinsa daita.”
kallonsa ta cigaba da yi wanda ya rigada ya saba da irin wannan kallon nata in dai tana tare dashi tô fa dukkanin idanunta na kanshi ya fahimci kallonsa ba qaramin jefata cikin nishadi yake ba .
bai damu da yadda ta tsare shi da idanunta ba saboda hasalima jin dadin hakan yake dan yana sa shi jin farinciki ,yanzu ma hakan ce ta kasance domin kuwa ya nemi dukkanin damuwarsa ya rasa .”
Anas ya kallesa ya girgiza kai yana dubansa dan yasan babu macen data isa ya tsaya yana kallonta haka sai ita data cire tuta .”
ya mike tsam zai fita daga dakin sai lokacin tanwer ta dauke idanunta akan jaguwa ta maida kanshi “anas ina yini ?
“Lafiya lau tanwer ya kwana biyu ?
“Lafiya gsky mun jima bamu ga juna ba tun a asibiti fa gashi har na warke “ ,alhamdulillah mun godewa allah dan da wani abu ya sameki ban san yadda wannan abokin nawa zai yi react ba ina ganin ma zare mana zai yi yayi maganr cikin zolaya yana murmushi yana kallon jaguwa murmushi tayi “ai sai yana sona ne zai zare muku inda wani abu ya faru dani “kinga ni nayi waje bazaa yi tone tone dani ba ya sa kai ya fice daga dakin ya rufo musu kofa .”
gbdy suka zagayesa suka sakashi a tsakiya jikinsa banda tsuma babu abinda yake wani gumi ya shiga tsatsafo masa a goshinsa da kan hancinsa “lallai yau ya dauko ruwan dafa kansa sannan ya hadu da gamonsa bai taba cin karo da rudani da firgici irin wannnan ba ,yau tazo masa da rikincin da bai taba tsintar kanshi aciki ba, iya girmansa daya samu karfin iko bai taba cin karo da tsagiran tantira irinsu ba sai yau .
“Ina karfin ikon naka yake? “ashe baka da ikon komai da karfi ka sanyo kafafunka cikin gidana? kamar yadda kake ganin kana da kwakwaluwa da baseera kashe wanda baka so,ko halaka wanda baka so ,ko batar da wanda baka son gani kasani tamu ta zarta naka ,idan kuma ka tsaya akan cewar karfin ikon da kake dashi zai kareka akoina to kayi babban kuskure domin zaka kasance mai yawon shiga rudani kuma babu abinda karfin ikon naka zai maka kamar yadda kake gani a yanzu saboda an fika da kaifin baseera .”
“Idan kuma da zuciyarka kawai ka dogara kasani nasararka ragaggiya ce saboda ita zuciya abinda yayi mata dadi kawai take aiyanawa a yanzu ma zan iya kasheka waye zai sani ? jaguwa ya tambayesa yana goge bakin bindigarsa tare da yi masa kallon kaskanci alhj tajudeeni yayi shiru jikinsa na wani irin karkarwa “Kasani mutane ire irenku basa amfanar da kansu da komai agaban irinmu idan kaje ka tambayi amininka zai maka qarin bayani akaina yanzu yanzu ka kama hanya ka fice min da gani ban san ganinka jeka…” ya fada tare da juyawa ya nufi ciki gbdy duk suka dare suka barshi tsaye cike da tsananin tashin hankali ya juya ya soma tafiya da kyar zuciyarsa na tafarfasa “. da sauri ajuwon ya biyo bayansa har suka kai bakin get ,bai tsaya jiran a bude masa murfin kofa ba ya bude ya shiga ya zauna yana huci .”
kwalkwaluwarsa ta toshe kansa ya cunkushe ya dinga zurfafa tunaninsa duk abinda suka fada babu wanda yafi tsaya masa a zuciya kamar ta mutumin da yaji ajuwon yace shine anas dashi kanshi jaguwa maganganunsu sunfi cakar masa zuciya da kwakwaluwa, ya rufe idanunshi ya jingina bayansa yana jujuya maganganunsu yana yin filla filla dasu yana neman wa kansa abinda zai musu ya halakasu “sam sam bazan barsu ba ,bazasu sha a banza ba ,sai na gina musu wani rami da zasu afka aciki amman bazan barsu ba har sai naga bayansu daya bayan daya har ya karasa office da wannan tunani ya karasa zuciyarsa kamar zata buga“.
Bayan tafiyar alhji tajudeeni jaguwa ya sauya kaya ya zauna ya janyo pillow ya rungume a qirjinsa yana nazarin maganar alhj tajudeeni yana son yatantance tabbacin abinda zai iya yi acikin maganganunsa wani bangaren na zuciyarsa yaji ya yarda alhji tajudeeni zai iya yin wani abu domin yaga bayansu yayinda wani zuciyar ke karfafa masa gwiwar cewar babu abinda zai yi nan take yayi accept da maganar kyakkyawar zuciyarsa babu
abinda zai yi .”
A natse anas ya turo kofar dakinsa ya shigo bai san ya shigo sai da ya dafashi sannan ya waigo yana sauke numfashi “karka takura kanka da tunani fa bazai iya komai ba zuciyarsa zataita tunanin abinda zai yi mana amman bazai iya komai ba ,wannnan gaskiy ne bazai iya ba amman duk da haka zamu sa hankalinmu akanshi shiyasa kullum da kake cewa mu ajiye makamammu nake cewa da kai aa nasan gaskiya kake fada min amman a yanzu bazan yarda da ita ba “ ya kamata ka yarda mu bari zan yi iyakar kokarina mu canza gbdynmu kuma inshaallahu zanyi nasara “ka kasa fahimtata ne anas barin wannan aiki yana da matukar hatsari sai muyi matukar shiri wanda bazai ruguje mana ba sannan ma idan zamu bari ya karasa mgnr yana cewa “ ya kake jin kan naka yanzu? ya fad’a ta hnayar katse maganar gbdy “har cikin kwayar idanuna nake ji ciwon kan amman maganr wancan banzar mutumin tasa na nemi ciwon kan na rasa jaguwa yayi murmushin gefen baki yana kokarin bude baki yaji ana knowking din kofa yasan cikin yaransa ne ya bada umarnin shigowa eku ya shigo rike da wayoyinsa daya na ringing aciki .
ya mika masa wacce take ringing din ya amsa yana dubawa number ya gani babu suna yana yawo akan screen din wayar shi kuma eku ya juya ya fice daga dakin ya dafe kanshi batare daya daga wayar ba anas ya matso kusa dashi “ka daga mana ko kiran ba mai mahimanci bane ? “number babu suna ! ya fad’a yana lumshe ido knowking suka sake ji anas yace “waye ?
“Nice !
Da saurin ya bude idanunshi sakamakon jin sautin muryarta ya kalli anas shima din kallonsa yake “na fad’a mata karta sake zuwa gidan nan me kuma ya kawota ?“Oho ai ka hadu da gamonka dan wannan yarinyar wallahi bazata koro ba kamar sauran matan daka saba kora ,ta zame maka karfen kafa mutu ka raba ya fad’a yana masa dariya kafin yayi wani hanzari har ta murda handle din kofar ta shigo ta tsaya tana dubansa da lulu eye’s dinta sanye take cikin doguwar rigar abaya yellow wanda akayiwa ado da flower ‘s baki haka yar cikinta baki ne ,hand bag da takalmi har ma da agogon dake daure a tsintsiyar hannunta baki ne tayi kyau matuka gbdy kamshin turarenta ya hade danashi ya gauraye dakin kamar ya tashi ya sureta yayi bedroom dinsa daita.”
kallonsa ta cigaba da yi wanda ya rigada ya saba da irin wannan kallon nata in dai tana tare dashi tô fa dukkanin idanunta na kanshi ya fahimci kallonsa ba qaramin jefata cikin nishadi yake ba .
bai damu da yadda ta tsare shi da idanunta ba saboda hasalima jin dadin hakan yake dan yana sa shi jin farinciki ,yanzu ma hakan ce ta kasance domin kuwa ya nemi dukkanin damuwarsa ya rasa .”
Anas ya kallesa ya girgiza kai yana dubansa dan yasan babu macen data isa ya tsaya yana kallonta haka sai ita data cire tuta .”
ya mike tsam zai fita daga dakin sai lokacin tanwer ta dauke idanunta akan jaguwa ta maida kanshi “anas ina yini ?
“Lafiya lau tanwer ya kwana biyu ?
“Lafiya gsky mun jima bamu ga juna ba tun a asibiti fa gashi har na warke “ ,alhamdulillah mun godewa allah dan da wani abu ya sameki ban san yadda wannan abokin nawa zai yi react ba ina ganin ma zare mana zai yi yayi maganr cikin zolaya yana murmushi yana kallon jaguwa murmushi tayi “ai sai yana sona ne zai zare muku inda wani abu ya faru dani “kinga ni nayi waje bazaa yi tone tone dani ba ya sa kai ya fice daga dakin ya rufo musu kofa .”