← Book details Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 160

Sashe 77

Kuskuren Baya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tashi yayi ya mike tsaye tare da fad'in "me ?!
Hawaye suka Kara zubo mata a hankali ya koma ya zauna saboda juyan dake dibansa bakinsa na karanta salatin manzon Allah gbdynsu tsit sukayi na tsawon lokaci sai mumy dake zubar da hawaye bai yi auni ba yaga numfashinta na fita da kyar da sauri ya tarairayota zuwa jikinsa Yana Kiran sunanta "Zainab !Zainab !!Dan girman Allah karki Kara min tashin hankali akan Wanda nake ciki ya jawo Goran ruwa ya zuba a hannunsa ya yarfa mata ya cigaba da shafa mata ruw a fuskarta a hankali har ta dawo haiyacinta ta bude idanunta tana kallonsa sannan ta sake fashewa da wani sabon kuka da take Jin radadinsu har cikin zuciyarta Nan take tausayinta yasa hawayen minister suka zubo bakinciki kamar ya Kai mumy lahira "kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki Zainab wannan jarabawa ce daga Allah Babu Wanda ya Isa ya Hana Hakan faruwa ,ban son ki cigaba da tsananta damuwa domin zata jefaki cikin mummunar matsayi ki dogara da Allah shine zai magance komai mu ma godewa Allah da qaddara ce ta fad'awa tanweer ba bin Maza take ba.

" Aranshi yace Ina ma zan iya goge *kuskuren baya* dana aikata hakika na tafka kuskuren gashi ya shafi yaruwar dilon diyata .Ta goge hawayenta tayi iya yinta ta tashi zaune ta kasa yace karki damu da sai kin tashi yanzu kiyi kwanciyarki ki huta bari na kwaso magunhunaki naga Wanda ya dace ki Sha .
Ya mike da sauri wani duhu ya rufe idanunshi baya ganin komai sai wasu taurari dole tasa ya dawo ya zauna Yana furta hasbinallahu wa ni'imal wakil yayi ta maza ya sake mikewa mumy tace "ka zauna karkaje ka fadi ka nakasa bai kulata ba ya fice dan yafi bukatar rayuwarta akan tashi .
bai dade ba ya dawo d'akin da kwadon magungunanta ya zauna yana bincikawa jikinsa na rawa
Saboda bacin rai Amman haka ya daure ya d'auki kanta ya d'aura saman cinyarsa yana mata sannu ya goge mata kwalla sai daya kwantar mata da hankalin sannan ya mike ya nufi dakin tanweer cikin tsananin tashin hankali.
tana kwance tayi ruf da ciki ya tsurawa bayanta Ido daman wannan shine karshen masu halin munafurci irin nasa, karshen mai son zuciya kenan, Kuma duk Wanda yaci bashin Allah sai ga karshensa tun anan gidan duniya ,sannan karshen mai irin halinsa kenan dansani.
a yanzu ya gane kuskurensa da yayi tsawon shekaru yana aikatawa a boye ,ya goge kwallan data zubo masa ya kirasa sunanta "tan!
Ta juyo a natse tana fuskantashin "Tashi ki shirya muje hospital a cire miki cikin " da sauri ta shiga girgiza masa kai alamun bazata zubar .Wani irin juya ne ya soma dibarsa nan kuma ya shiga furta Kalmar Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun yana maimaitawa cikin haka mumy ta rarrafo ta shigo d'akin adaidaita lokacin da dady yake sake bawa tan umarni "ni dady Abar min abuna ina so ..."
"Kina son me dan ubanki ?"me zakiyi dashi ? kina hauka ne Ko kin fara Shaye shaye ne ?"tayi mata tmbyr ajere juya na sake dibarta kafin kace me tuni ta soma yin kasa da sauri tanwer ta sauko daga kan gado suka hadu da dady a lokacin da take kokarin kaiwa Kasa da kyar take fidda numfashi bakinta na rawa tace "tan..! tan !! ki amince a cire cikin ...."

Assalamu alaikum yan'uwa barkanmu da wannan lokacin jama'a , ku taimakawa wannan baiwar Allah Mai suna rukayya wacce ta kasance budurwa ce tana fama da ciwon no-no tsawon shekara daya Kenna saboda iyayenta basu da halin da zasu dauki nauyinta yasa brest dinta d'aya fara lalacewa , rukayya tana zaune ne a garin Kaduna a unguwar kanawa tare da iyayenta dan Allah ku taimaka mata saboda Allah da darajan fiyayyen halitta annabi Muhammadu sallallahu alaihi wa sallam ga masu bukatar taimakawa ga account number nan 1438775094 Aishat Abdullahi access bank .Domin Jin qarin bayani a tuntubi wadan nan numbobin
07039569430
07037450698
08059623096
Allah ya bada iKon taimakawa .

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

PAID BOOK

 WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin na kudi ne  mai bukata karanta shi  ya tura 500 ta wannan  account number din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert  domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu  a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.

🅿️25

zama   jaguwa  ya  cigaba   da  yi  rike  da  waya   zuciyarsa  na zafi da  farfasa  a qalla  ya kusan minti  goma  yana  tunanin maganganunta,"  bai  san me yasa  zai  damu  kansa  akan cikin  ba , cikin  ma  da bashi da  tabbacin  tana d'auke dashi .
wani   dogon   tsaki  yaja  yana   sake  kiran  layinta , babu 'bata  lokaci   ta   d'auka  qirjinta na bugawa  fat  fat "Ke ni zakiwa wulakacin ? "
shiru  tayi  taki  ce masa komai  sai  dai  zuciyarta  ke wani irin  bugawa da sauri sauri .
"har  kin  isa   ki dinga  farfad'a min  magana son  ranki  ?"
ya sake tmbyrta tare da jan  tsaki "har  ma  da  kashe min waya ? "shiru  tayi  still  cikin  tsananin  tashin  hankali tana tunanin  abinda  zata sake fad'a masa  wanda  zai sake d'aga masa  hankali  sai dai bata kai ga tattara  abinda zata  fada  masa ba  ta  tsikayi  muryarsa na dukan   dodon  kunnenta.
"dan  kinga ina lalla'baki  shine zaki d'auka ko ina  jin  tsoron ki haifi cikin ne ? "to  kar  allah yasa ki cire cikin ai cikin ba ajikina  yake  ba  idan akwai shi kenan  dan  haka  ko ki cire ko Karki  cire ruwanki sannan  matsalarki ce  bata Adnan  .
ba Adnan za'a dinga kwatance dashi ba , sannan ba shi zai rasa mai aurensa ba . aurenki  ne dai bazan  yi ba  kije ki nemi abokin rayuwarki  dan ni  tuni na amince da  zabin mahaifiyata aikin  banza Kawai  ki jira  ki gani  idan  zan sake  nemanki".
ya k'arasa maganar yana jan dogon  tsaki sannan ya katse Kiran  yana fidda wani wahalallen numfashi ,yasa hannunsa  d'aya ya dafe goshinsa yana  jin  zafi  da ciwo a ransa, shiru yay na  second goma  qirjinsa  da  gangar jikinsa na  rawa   gbdy  sai   yaji  kimai ya tsaya  masa  guri  daya  ya shiga tunanin abinda yayi mata  a ganin zuciyarsa   bai  kyauta mata  ba daya farfad'a mata son  ranshi  dan  bata  cancaci  ya fad'a  mata  magangun daya fad'a mata ba ,ita din wata aba ce mai daraja da  kima a  rayuwarsa. amman daya  tuna irin maganganun  data  fad'a masa da irin mugun fatan da tai masa a mintunan da suka gabata  sai  ya  dawo  haiyacinsa ,  komai ya dawo  masa daidai, qirjinsa da gangar jikinsa da suka d'auki rawa  suka  daidaita  yaga  mai ma yayi mata ai bai mata komai ba  . "

Bangaren  tanwer  kuwa maganganunsa sun  daki Kunnuwanta  sosai sannan sun wuce  har  cikin zuciyarta, gbdy ya  kunno  mata  wutar  damuwar da take dannewa  acikin  zuciyarta  ,Kawai sai ji  hawaye yazo idanunta  ya fara zuba  akan  kuncinta, a hankali ta fara  rare kuka mara sauti qirjinta na zafi  "Allah ka gani ba wai  nayi  masa haka dan  na wulakatanshi bane , "na yi dan na raunata zuciyarsa,na yine  ko zai saduda ya zubar da makamansa ya  canza rayuwarsa  darajan  tace  bata zubar ba suyi aure  ,ashe  wata sabuwar maseefa  ta jefa kanta ciki tayi maganar a fili tana sheshekan kuka  "wayyo Allah  ka d'auki raina  na  huta  da wannan rayuwar  da nake " wani  zafi take a kahon zuciyarta sam ba taji kashi  daya na son da take masa ya  rugu  sai ma qaruwa da son shi yayi acikin zuciyarta , tana  sonshi    muddin zai aureta zatai  confuse din  iyayenta  akwai  hanyoyi  da dama da idan ta bullo dasu dolensu  su  hakura su rungumi  nata qaddarar su aura mata shi amman shi kuji abinda yake fad'a  mata har ma ya amince da zabin mahaifiyarsa ita ko  oho  zama  tayi ta  cigaba da rera  kukanta tare da rafka uban tagumi cikin zullumi da rashin  sanin  madafa ."

tana  cikin  wannan halin  rukayya ta shigo d'akin ganin idanun  tanwer   na  zubar da ruwan   hawaye yasa ta karasa shigowa  d'akin da sauri  tana cewa "lafiya  tanwer menene Kuma ?"
Rukayya ta samu guri gefenta ta zauna ta riko hannuwanta duka  cikin  nata  tana dubanta cike da tausayawa , runtse idanunta tanweer  tayi sai ga wasu hawayen  sharrrrrr."
"wallahi ina cikin damuwa  rukayya ,ina cikin tashin hankali  na rasa  yadda  zanyi da wannan rayuwar da nake  ciki , komai ya canza  min rukayya  ina ma rayuwata ta baya  zama dawo  , "ina ma ban dawo kasar nan ba"..
Rukayya  ta numfasa tace" haka ne  kina cikin  damuwa da jarabawar  rayuwa  tanwer  amman  kiyi  hakuri da sannu komai zai  daidaita ,"sannan   kiyi kokari ki  rage damuwar nan duk  da  tasan komai dake faruwa  daita amman taki fitowa ta bayyana mata .
" ki kara  imani  da qaddara komai ya faru da bawa a rubuce yake  bawa bai isa ya gujewa qaddararsa, rayuwar bawa tana tattare da qaddarori ne  kawai dai  Allah  ya bamu Ikon cinye jarabawarmu  rukayya   ta  fadi  haka ne dan takaita maganar .
"nima ina son na rage tunanin  Adnan acikin zuciyata  amman na rasa dalili da tunaninsa  kullum sai gaba  yake , wallahi ina  masa wani irin so da bansan ranar da zan daina shi  ba , kuma bazan taba fidda raina akanshi  ba sai  ranar dana ji an shafa fatihan  aurensa ta k'arasa maganar tana  mai  runtse idanunta."
Chapter 77 · 0% Book details