Sashe 95
Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
************
Wash gari dole Dad gado aka basa a asibitin sbd Bp dinsa kwata kwata yaqi dawowa daidai.
Mimi ma taqi yadda ko kadan ta baro asibitin itada Saleem wanda Ammar yake cikin ransa sosai dan haka dole Maheer shima ya kasa baro asibitin.
Karfe 11 na rana Sayd y iso asibitin sanye d face mask da fcap daukan Jannah wadda tinda sassafe ta iso asibitin ko tsayuwa bata iya yi da kujera aka kawota.
Sayd na shigowa dakin Ammar na farfadowa dan jannah ta kalli Sayd din tace yabarta zata dawo daga baya.
Baice komaib wayarsa ya fidda ya saka kiran LIMBA yana dauka ya bata wayar yana juyawa ya fice daga dakin yabarta tayi magana dashi idan ya Yadda.
Harta yanke bai dagaba dan haka ta ajiye wayar akan kafafunta tana kallan Ammar wanda idanuwansa dake a jeme suka sauka akan hoton dayake kan wayar sayd baro baro na Ummitah da AZIZ wanda asalin kamanninsu suka bayyana kaman an tsaga kara tana dariya a jikinsa.
Duk da baya gani sosai rawa hannuwansa suka fara yi yana son nuna hoton Ummitah dayake cikin wayar wadda sukeda hotonta haryanzu a cikin file na jannah.
Rikicewa gabaki daya yayi yana wani irin yunkurin magana hannuwansa da bakinsa na rawa.
Sayd ne ya shigo dakin ya karbi wayarsa yana barin asibitin da jannah ya maidata gida sbd itama neman rikicewa jikinta keyi sbd tashin hankalin ganin yanayin Ammar.
Da gudu likitoci sukayo dakin tareda su Mimi dasu Maheer dasuka je dakin dad dubosa.
Suna shigowa Ammar ya damqe maheer da karfin gaske yana kallansa yana kallan Abraham muryansa n sarkew yace
"AZIZ limba da donor dinmu,
Zuciyar dayake bugawa a zuciyar Jannah AZIZ LIMBA,AZIZ LIMBA ya.....
Ganin yana neman fallasa komai a gaban mutane da sauran likitocin batareda yasan me yake fada ba ya saka hankalinsu gabaki daya tashi cikim mugun faduwar gaba da shiga Rikitaccen yanayi dr Abraham ya masa allurar data sakasa zubewa a gurin yana tinanin kwakwalwan Ammar tabbas ta tabu.
Anny jin tayi zufa ya rufeta hankalinta na neman tashi da abinda yake shirin faruwa idan baa nema maganin ciwon Ammar da gaggawaba zai iya tona asiri su shiga masifar da babu fita.
AZIZ LIMBA karfe 7 na dare motarsa ta isa Zaadens tareda Sayd wanda suke shirye tsaf dan gama komai su tattara su koma inda suka fito.
Babu kowa kaf a mansion din sai masu aiki da securities sai Daddy mahmoud daya fito jin isowansu sbd matarsa mummy tayi asibiti da daren dubo Ammar da kaiwa su Mimi abinci masu tarin yawa kala kala.
Kasancewan Daddy mahmoud din shima yanada weak heart ya saka abu kadan yake sakasa samun attack ko bugawan zuciya shiyasa ko farkon samun matsalar financial crisis dinsu ya kamu da paralys dakyar ya dawo daidai dan hakanne tin jiya yake fama da ciwon kirji.
A yanayinda ya fito yana kallansu ya saka AZIZ masa kallo daya ya hango zuciyarsa gap take da bugawa dan haka fasa zama yayi ya kalli Say wanda yayi amfani da sabuwar waya ya tura sako zuwa wayar Anny.
Kallan Daddy mahmoud din AZIZ yai a qasqance kafin ya bude baki yace
"Ka dena daga hankalinka akan Ammar Zaaden sbd ya riga ya rasu.........
Wani mummunan bugawa zuciyar daddyn tayi ya dago da sauri yana kallan AZIZ hannuwansa na rawa da kafafunsa ya bude baki zaiyi magana AZIZ din ya katsesa da cewa
"Tinda wuri zaka buga zuciyarka bayan baka gama jin abinda zan fada maka ba"
Girgiza kai daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa muryansa na rawa yace
"Ammar ya rasu??
"Ba shi kadai ya rasu ba hadda Dan uwanka shima lokacinsa yayi na......
Faduwa Daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa da karfi zuciyarsa na kokarin bugawa ganinsa na daukewa yana son yayi magana amma ya kasa azababbiyar azaba kirjinsa ke masa....
Durqusawa gabansa AZIZ yayi shima hannuwansa na dan rawa idanuwansa n sauyawa zuwa jajir yace
"Kirjinka baya iya dauka ko?
Fiyeda hakan na samu kaina a lokacinda na samu labarin mutuwar yar uwata,rabin jikina,rayuwata,uwar Falaq Aziz wadda ayau zuciyarta take bugawa a kirjin 'yarku da kukaso ta rayu kuka kashe tawa rayuwar........
A cikin tsananin azabar datafi karfin kirjinsa Daddy mahmoud y dago idanuwansa da sukai jajir din azaba ya kalli AZIZ cikin tsananin mamaki da shock idanuwansa n fitowa sosai sbd azaba sa shock yana kallan fuskan AZIZ wanda sai a lokacin yake ganin kammaninsa da Yarinya me cikin da suka samarwa Jannah sbd akwai hotonta a cikin file din jannah har yau.....
Magana yakeson yayi amma ina maganganun AZIZ ragargaza zuciyarsa sukeyi zuciyarsa na qara samun bugawa.
Shi kansa AZIZ din cikin wani matsanancin halin yake magana yana fada masa yanda ya shiga cikinsu da yanda zai qarar dasu daya bayan daya ya tabbatarda ko sunansu aka fada sai an la'ance su an tsinewa zuriarsu.
Kofa Sayd ya kalla sbd jin shigowan mota gidan ya tabbatarda Anny ce wadda ta iso gidan a gigice.
Ko gani batayi sosai ta iso gidan sbd sakon daya shigo wayarta na cewa
AZIZ LIMBA na hanyar isa Zaadens Daddy mahmoud ya nemesa zai basa takardun ciwon jannah daya buqata kuma tafi kowa sanin Sun goge sunan Ammar a cikin likitocin ciki daga nata saina sauran likitocin.
A yanda tasan Familyn tsaf zasu cire sunan Ammar abar nasu hakama akan neman lafiyan jannah zasu iya fidda file dinta a bawa AZIZ LIMBA wanda hakan na faruwa sun gama Rayuwa a doran qasa sbd bazai rufa musu asiriba,
Hakama matakin da Ammar yake kai yanzu na rashin lafiya harda kusan wadda ta shafi kwakwalwa take familyn zaa rifesa a matsayin baida lafiyar kwakwalwa ya sha ita kuwa fa??
Inaaa,bazata yadda ba wlh ko kadan....
Kwata kwata fita tayi hayyacinta taji bata gane komai bayan ta riga isa gidan kafin isar LIMBA.
Gabaki daya ta fice hayyacinta sbd maganar Ammar datake yawo a cikin kanta wanda sai yanxu take kokarin tina kammannin donor din jan wadda take son hadawa da kammanin AZIZ din tanajin kanta na neman kuncewa.
Kafafunta har rawa sukeyi ta iso palon daidai lokacinda Su AZIZ sun riga sun bar palon Daddy mahmoud ya daga hannu ya bude baki zai ambaci AZIZ din cikin tsananin azaba Anny bata tsaya lura da yanayinsa ba kawai ta dauka AZIZ din zai kira dan masa magana dan haka ta fidda allurar data taho da ita ta soka masa a wuya tana juye masa ruwan ciki daidai lokacin Saleem da mommy na shigowa palon shikuma AZIZ da sallama me nutsuwa ya qarasa cikin palon jannah wadda ke zaune shiru idanuwanta sunyi jajir ta qara fadawa sosai a kwana da wunin.
Dago idanuwanta tayi ta kalli kofar jin muryansa da qamshinsa a lokaci daya.
Ajiye kafafunta qasa tayi ahankali qasa tana kallansa a sanyaye sbd rabonta da ganinsa ko jinsa tin shekaran jiyan daya bar nan din.
Takowa yayi ahankali cikin nutsuwa shima yana kokarin daidaita kansa daga halinda yake ciki na tafarfasan zuciya da tsananin ciwon zantukan daya maimaitawa zuciyarsa na yanda suka rabasa da Ummitah.
Kallon dayake mata ne ya sakata miqewa ahankali tana jin zuciyarta na narkewa akansa taku daya tayi ta kasa ta tsaya tana kokarin faduwa qasa zaune ya tarota jikinsa yana kallan tsakiyar idanuwanta da suka kasa daukan kallansa ta lumshe su tana sauke ajiyan zuciya jiki a mace.
Shiru yayi baice mata komai fuskanta kawai yake kalla yana jin yanda zuciyarta ke bugawa Kirjinsa....
Komai nata yana nuna yanda take tsananin sonsa ne wanda hakan yake masa illa mai girma a nasa bangaren sbd yasan soyayya zata iya zama rauninsa kaman yanda take rauninta...
Ihun Mummy me karfin gaske ne ya sakashi lumshe idanuwansa ahankali ya budesa akanta ita kuma a lokacin ne ta bude nata idanuwan ahankali tana kallan kofa.
Jame jikinta tai ahankali tana son zuwa palon amma batada karfin hakan a jikinta ko kadan dan haka ta kasa dagowa ta kallesa.
Lura da hakan ya saka hannunsa ya zagoyo qugunta ta mannu da jikinsa ahankali ya dauketa gabaki dayanta a jikinsa ya nufo kofar da ita zuwa babban sitting room na gidan da hayaniyar ke fitowa ta can.
Sayd shima a lokacin ya shigo palon kaman yanzu yake shigowa shima,
Anny da hannuwanta ke rawa kallan Daddy mahmoud din dayake wani irin numfashi yana kokarin rasa ransa sbd Alluran datai masa kwata kwata baa yiwa wanda yake cikin heart attack hakan na matiqar hadarin gaske,
Ganin su Mummy da Saleem akanta ya sakata fara rawar jiki tana kokarin daidaita kanta ta kalli Mummy tana cewa
"Mummy koda nazo inaga ya samu attack ne ina kokarin basa taimako ne zamu iya gaggawan kaisa asibitin"
Mummy bata iya amsata ba da gudun tayo kansa itada saleem tana ganin yanda yake wani irin jan numfashin wahala idanuwansa na rufewa shine ta fasa ihun me karfi tana kiran sunansa.
A lokacin ne AZIZ da jannah din suka fito idanuwan Daddyn akan AZIZ yana kallansa wasu hawayen azaba da dana sani dana son ya fada musu waye AZIZ limba suka gangaro masa idanuwansa suka rufe ahankali cikeda azaba.
Saleem ne da Sayd suka daukesa da gaggawa zuwa mota hakama jannah rawa jikinta yafara tana kallansu cikin tashin hankali da fargaban sabuwar masifar data tinkaro su.
Fitowa sukai dukkaninsu harabar gidan yacewa Sayd yaje tareda Saleem ya taimaka masa shikuma ya karbi key din motarsa ya saka jannah a ciki motar saleem na fita tasa tabar mansion din shima ya nufi gida da ita.
Mummy da duk ta fita hayyacinta take sbd tsananin tashin hankali daqyar Anny ta iya sakata mota itama a rude hannuwanta na rawa suka bi bayansu saleem din sai a lokacin take jin tsoron rashin tinanin datai na bin sakon da kyau taga inda ya fito ta jefa kanta cikin kaddara,
Hakama waye wannan dayasan sirrin su bayansu dazai mata text din wanda takeda tabbacin yayi magana ne sbd yasan sirrin dasuke boyewa.
Tin a mota saleem cikin damuwa da tashin hankali ya sanarwa Maheer suna hanyar asibitin da Daddy mahmoud.
Miqewa Maheer yayi cikin tashin hankali yana kallan Dad daya ji abinda aka fada dukkaninsu hankalinsu na tashi da sabon tsoro.
Wash gari dole Dad gado aka basa a asibitin sbd Bp dinsa kwata kwata yaqi dawowa daidai.
Mimi ma taqi yadda ko kadan ta baro asibitin itada Saleem wanda Ammar yake cikin ransa sosai dan haka dole Maheer shima ya kasa baro asibitin.
Karfe 11 na rana Sayd y iso asibitin sanye d face mask da fcap daukan Jannah wadda tinda sassafe ta iso asibitin ko tsayuwa bata iya yi da kujera aka kawota.
Sayd na shigowa dakin Ammar na farfadowa dan jannah ta kalli Sayd din tace yabarta zata dawo daga baya.
Baice komaib wayarsa ya fidda ya saka kiran LIMBA yana dauka ya bata wayar yana juyawa ya fice daga dakin yabarta tayi magana dashi idan ya Yadda.
Harta yanke bai dagaba dan haka ta ajiye wayar akan kafafunta tana kallan Ammar wanda idanuwansa dake a jeme suka sauka akan hoton dayake kan wayar sayd baro baro na Ummitah da AZIZ wanda asalin kamanninsu suka bayyana kaman an tsaga kara tana dariya a jikinsa.
Duk da baya gani sosai rawa hannuwansa suka fara yi yana son nuna hoton Ummitah dayake cikin wayar wadda sukeda hotonta haryanzu a cikin file na jannah.
Rikicewa gabaki daya yayi yana wani irin yunkurin magana hannuwansa da bakinsa na rawa.
Sayd ne ya shigo dakin ya karbi wayarsa yana barin asibitin da jannah ya maidata gida sbd itama neman rikicewa jikinta keyi sbd tashin hankalin ganin yanayin Ammar.
Da gudu likitoci sukayo dakin tareda su Mimi dasu Maheer dasuka je dakin dad dubosa.
Suna shigowa Ammar ya damqe maheer da karfin gaske yana kallansa yana kallan Abraham muryansa n sarkew yace
"AZIZ limba da donor dinmu,
Zuciyar dayake bugawa a zuciyar Jannah AZIZ LIMBA,AZIZ LIMBA ya.....
Ganin yana neman fallasa komai a gaban mutane da sauran likitocin batareda yasan me yake fada ba ya saka hankalinsu gabaki daya tashi cikim mugun faduwar gaba da shiga Rikitaccen yanayi dr Abraham ya masa allurar data sakasa zubewa a gurin yana tinanin kwakwalwan Ammar tabbas ta tabu.
Anny jin tayi zufa ya rufeta hankalinta na neman tashi da abinda yake shirin faruwa idan baa nema maganin ciwon Ammar da gaggawaba zai iya tona asiri su shiga masifar da babu fita.
AZIZ LIMBA karfe 7 na dare motarsa ta isa Zaadens tareda Sayd wanda suke shirye tsaf dan gama komai su tattara su koma inda suka fito.
Babu kowa kaf a mansion din sai masu aiki da securities sai Daddy mahmoud daya fito jin isowansu sbd matarsa mummy tayi asibiti da daren dubo Ammar da kaiwa su Mimi abinci masu tarin yawa kala kala.
Kasancewan Daddy mahmoud din shima yanada weak heart ya saka abu kadan yake sakasa samun attack ko bugawan zuciya shiyasa ko farkon samun matsalar financial crisis dinsu ya kamu da paralys dakyar ya dawo daidai dan hakanne tin jiya yake fama da ciwon kirji.
A yanayinda ya fito yana kallansu ya saka AZIZ masa kallo daya ya hango zuciyarsa gap take da bugawa dan haka fasa zama yayi ya kalli Say wanda yayi amfani da sabuwar waya ya tura sako zuwa wayar Anny.
Kallan Daddy mahmoud din AZIZ yai a qasqance kafin ya bude baki yace
"Ka dena daga hankalinka akan Ammar Zaaden sbd ya riga ya rasu.........
Wani mummunan bugawa zuciyar daddyn tayi ya dago da sauri yana kallan AZIZ hannuwansa na rawa da kafafunsa ya bude baki zaiyi magana AZIZ din ya katsesa da cewa
"Tinda wuri zaka buga zuciyarka bayan baka gama jin abinda zan fada maka ba"
Girgiza kai daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa muryansa na rawa yace
"Ammar ya rasu??
"Ba shi kadai ya rasu ba hadda Dan uwanka shima lokacinsa yayi na......
Faduwa Daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa da karfi zuciyarsa na kokarin bugawa ganinsa na daukewa yana son yayi magana amma ya kasa azababbiyar azaba kirjinsa ke masa....
Durqusawa gabansa AZIZ yayi shima hannuwansa na dan rawa idanuwansa n sauyawa zuwa jajir yace
"Kirjinka baya iya dauka ko?
Fiyeda hakan na samu kaina a lokacinda na samu labarin mutuwar yar uwata,rabin jikina,rayuwata,uwar Falaq Aziz wadda ayau zuciyarta take bugawa a kirjin 'yarku da kukaso ta rayu kuka kashe tawa rayuwar........
A cikin tsananin azabar datafi karfin kirjinsa Daddy mahmoud y dago idanuwansa da sukai jajir din azaba ya kalli AZIZ cikin tsananin mamaki da shock idanuwansa n fitowa sosai sbd azaba sa shock yana kallan fuskan AZIZ wanda sai a lokacin yake ganin kammaninsa da Yarinya me cikin da suka samarwa Jannah sbd akwai hotonta a cikin file din jannah har yau.....
Magana yakeson yayi amma ina maganganun AZIZ ragargaza zuciyarsa sukeyi zuciyarsa na qara samun bugawa.
Shi kansa AZIZ din cikin wani matsanancin halin yake magana yana fada masa yanda ya shiga cikinsu da yanda zai qarar dasu daya bayan daya ya tabbatarda ko sunansu aka fada sai an la'ance su an tsinewa zuriarsu.
Kofa Sayd ya kalla sbd jin shigowan mota gidan ya tabbatarda Anny ce wadda ta iso gidan a gigice.
Ko gani batayi sosai ta iso gidan sbd sakon daya shigo wayarta na cewa
AZIZ LIMBA na hanyar isa Zaadens Daddy mahmoud ya nemesa zai basa takardun ciwon jannah daya buqata kuma tafi kowa sanin Sun goge sunan Ammar a cikin likitocin ciki daga nata saina sauran likitocin.
A yanda tasan Familyn tsaf zasu cire sunan Ammar abar nasu hakama akan neman lafiyan jannah zasu iya fidda file dinta a bawa AZIZ LIMBA wanda hakan na faruwa sun gama Rayuwa a doran qasa sbd bazai rufa musu asiriba,
Hakama matakin da Ammar yake kai yanzu na rashin lafiya harda kusan wadda ta shafi kwakwalwa take familyn zaa rifesa a matsayin baida lafiyar kwakwalwa ya sha ita kuwa fa??
Inaaa,bazata yadda ba wlh ko kadan....
Kwata kwata fita tayi hayyacinta taji bata gane komai bayan ta riga isa gidan kafin isar LIMBA.
Gabaki daya ta fice hayyacinta sbd maganar Ammar datake yawo a cikin kanta wanda sai yanxu take kokarin tina kammannin donor din jan wadda take son hadawa da kammanin AZIZ din tanajin kanta na neman kuncewa.
Kafafunta har rawa sukeyi ta iso palon daidai lokacinda Su AZIZ sun riga sun bar palon Daddy mahmoud ya daga hannu ya bude baki zai ambaci AZIZ din cikin tsananin azaba Anny bata tsaya lura da yanayinsa ba kawai ta dauka AZIZ din zai kira dan masa magana dan haka ta fidda allurar data taho da ita ta soka masa a wuya tana juye masa ruwan ciki daidai lokacin Saleem da mommy na shigowa palon shikuma AZIZ da sallama me nutsuwa ya qarasa cikin palon jannah wadda ke zaune shiru idanuwanta sunyi jajir ta qara fadawa sosai a kwana da wunin.
Dago idanuwanta tayi ta kalli kofar jin muryansa da qamshinsa a lokaci daya.
Ajiye kafafunta qasa tayi ahankali qasa tana kallansa a sanyaye sbd rabonta da ganinsa ko jinsa tin shekaran jiyan daya bar nan din.
Takowa yayi ahankali cikin nutsuwa shima yana kokarin daidaita kansa daga halinda yake ciki na tafarfasan zuciya da tsananin ciwon zantukan daya maimaitawa zuciyarsa na yanda suka rabasa da Ummitah.
Kallon dayake mata ne ya sakata miqewa ahankali tana jin zuciyarta na narkewa akansa taku daya tayi ta kasa ta tsaya tana kokarin faduwa qasa zaune ya tarota jikinsa yana kallan tsakiyar idanuwanta da suka kasa daukan kallansa ta lumshe su tana sauke ajiyan zuciya jiki a mace.
Shiru yayi baice mata komai fuskanta kawai yake kalla yana jin yanda zuciyarta ke bugawa Kirjinsa....
Komai nata yana nuna yanda take tsananin sonsa ne wanda hakan yake masa illa mai girma a nasa bangaren sbd yasan soyayya zata iya zama rauninsa kaman yanda take rauninta...
Ihun Mummy me karfin gaske ne ya sakashi lumshe idanuwansa ahankali ya budesa akanta ita kuma a lokacin ne ta bude nata idanuwan ahankali tana kallan kofa.
Jame jikinta tai ahankali tana son zuwa palon amma batada karfin hakan a jikinta ko kadan dan haka ta kasa dagowa ta kallesa.
Lura da hakan ya saka hannunsa ya zagoyo qugunta ta mannu da jikinsa ahankali ya dauketa gabaki dayanta a jikinsa ya nufo kofar da ita zuwa babban sitting room na gidan da hayaniyar ke fitowa ta can.
Sayd shima a lokacin ya shigo palon kaman yanzu yake shigowa shima,
Anny da hannuwanta ke rawa kallan Daddy mahmoud din dayake wani irin numfashi yana kokarin rasa ransa sbd Alluran datai masa kwata kwata baa yiwa wanda yake cikin heart attack hakan na matiqar hadarin gaske,
Ganin su Mummy da Saleem akanta ya sakata fara rawar jiki tana kokarin daidaita kanta ta kalli Mummy tana cewa
"Mummy koda nazo inaga ya samu attack ne ina kokarin basa taimako ne zamu iya gaggawan kaisa asibitin"
Mummy bata iya amsata ba da gudun tayo kansa itada saleem tana ganin yanda yake wani irin jan numfashin wahala idanuwansa na rufewa shine ta fasa ihun me karfi tana kiran sunansa.
A lokacin ne AZIZ da jannah din suka fito idanuwan Daddyn akan AZIZ yana kallansa wasu hawayen azaba da dana sani dana son ya fada musu waye AZIZ limba suka gangaro masa idanuwansa suka rufe ahankali cikeda azaba.
Saleem ne da Sayd suka daukesa da gaggawa zuwa mota hakama jannah rawa jikinta yafara tana kallansu cikin tashin hankali da fargaban sabuwar masifar data tinkaro su.
Fitowa sukai dukkaninsu harabar gidan yacewa Sayd yaje tareda Saleem ya taimaka masa shikuma ya karbi key din motarsa ya saka jannah a ciki motar saleem na fita tasa tabar mansion din shima ya nufi gida da ita.
Mummy da duk ta fita hayyacinta take sbd tsananin tashin hankali daqyar Anny ta iya sakata mota itama a rude hannuwanta na rawa suka bi bayansu saleem din sai a lokacin take jin tsoron rashin tinanin datai na bin sakon da kyau taga inda ya fito ta jefa kanta cikin kaddara,
Hakama waye wannan dayasan sirrin su bayansu dazai mata text din wanda takeda tabbacin yayi magana ne sbd yasan sirrin dasuke boyewa.
Tin a mota saleem cikin damuwa da tashin hankali ya sanarwa Maheer suna hanyar asibitin da Daddy mahmoud.
Miqewa Maheer yayi cikin tashin hankali yana kallan Dad daya ji abinda aka fada dukkaninsu hankalinsu na tashi da sabon tsoro.