← Book details Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 120

Sashe 59

Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shi kansa dad zancen ya sake sakasa cikin kwanciyar hankali sbd da kansa yakeson kulla Kyakkyawar alaqa me karfin gaske da LIMBA sbd baya wasa da billionaires dan haka da kansa zai jagoranci neman kusanci da Limban sbd kada ma su kawo matsala ko daya su 'yayan nasa.

*********Sayd dayake jiran kiran Zaadens din tin ranar da suka dawo Nigeria se yau ya samu kiran daga garesu dan haka cikin rashin basu mahimmanci a natse ya gama sauraron bayanin Deen kafin ya basu damar contacting Limba din kai tsaye wanda Maheer ne ya kira AZIZ da kansa sedai bai daga ba sbd baimasan numbern ba sai kusan bayan kwana biyu daya sake kira kafin Ya daga cikeda iko da nutsuwa da izzansa data saka Maheer jin kishinsa me tsanani ya rufesa sedai kuma yana tsananin son kasancewansu dashi dan haka cikin tasa class din da wayewa tareda dukiya daya taso cikinta da hutu suka gaisa ya gabatar masa da kansa.

Wani irin yanayi me daci ne ya dan tasowa AZIZ din yanajin saukan muryan Maheer din kamar wani yankan rezan dayake yanka zuciyarsa sbd bai taba tinanin zai iya sauraronsu da kunnuwansa masu tsafta ba.

Bude kyawawan idanuwansa da ya dan rufe yana cigaba da sauraron Maheer din wanda ya nuna masa sakewa.

A natse cikin kwanciyar yake dan magana kafin ya amince da gayyatarsu na haduwa bayan yace zai duba proposal nasu da suka turawa sayd insha Allah zaizo da approval nasa na hada business din.

Sallama sukai Maheer na cikin farin ciki da samun cikar burinsu dan haka suka fara shirin tarbonsa a Zad mansion.
##MAMUH

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
47
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC (kayan mata)
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4200
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki

************
A bangaren LIMBAs komai yana tafiya a familyn daidai sbd falaq bata samu damuwa ko jin rashin dadin qasarba sbd bata taba zuwaba tinda aka tafi da ita gana Nigeria dan haka kamar wannan ne zuwanta na farko bayan data barta dan haka suke tinanin zata iya shiga damuwa da rigimar batason nan din amma kuma a nata bangaren Nigeria din ta zama best gurin da zatai rayuwa me dadi sbd daddynta zai kasance dasu ba yawan tafiye tafiye dan haka hankalinta yake kwance sbd tana tareda familynta duka hakama yanayin duniyar dake cikin gidan yasakata batajin wani banbanci da qasar da suka baro dan haka takejin dadinta kawai hankalinta kwance.

Kwanciyar hankalinta da walwalwanta ya saka gabaki daya gidan suma suke cikin walwala da kwanciyar hankali da farin cikin komai yana tafiya daidai gashi daga mama har Fiddausi suna cikin farin cikin dawowan dan gashi sam bai fadawa mama abinda akaiwa Ummitah ba dan kada ya sakata quncinda baida magani dan haka suke cikin walwalansu gidan.

Baba alhassan ma ya taho yana abujan saiya huta yanda ya kamata zai koma gida dan haka sosai gidan ya zama cikin walwala.

Falaq sosai suke fita yawo da Latif da Fiddausi sbd taga gari da yawon shopping.

Ya karba gayyatarsu ne sbd bazai bari su sukawo masa ziyarar ba dan bayason abinda zai kawosu cikin gidansa da iyalinsa dan haka zai dira a nasu empire din da kansa.

****A cikin qanqanin lokaci ya kasance suna yawan waya dashi harma dashi Dzad din dakansa dan haka ya fara sakar musu hanyoyin businesses da suke buqata sbd su sake jikinsu sosai dashi.

A ranar daya shirya ziyartar familyn da nasa familyn sbd yanda suke son haduwar familyn nasu...

Cikin nutsuwa dukkani familynsa suka shirya suka fito banda Baba alhassan da hutu kawai akeson yayi.

Lafiyayyar RR ce da beymach Baqaqe suna daukan ido suka kawosu mansion din Zaadens da ake jiransu cikin Kyakkyawan tarba wanda suma lafiyayyun motocine a jere harabar gidan dan dukkanin wanda yake gidan yana motan datake amsa sunanta mota shi dad dinma kusan uku ne dashi Maheer ma biyu dashi sauran daddaya ne sbd basason mota da yawa.

Securities din gidan da sauri suka budewa motocinsu gate suka sako kai a cikin gidan sayd na kallan Zaadins din dake fitowa daya bayan daya cikin iko da suke murzawa dan tarban AZIZ LIMBA da basusan balai da masifar rayuwarsu ce suka fito tarba da hannu bibbiyu ba.

AZIZ kuwa idanuwansa ya tsayar akan Dzad dayake fitowa sanyeda kayan alfarma cikin dattako da nutsuwa ta ilimi daya ratsashi da dukiya amma zuciya duk tsatsa sedai yayi masa alkawarin kankare tsatsar zuciyarsa da abinda yafi tsatsan muni.

Parking aka latif ya fito daga mazaunin driver yana budewa mama mota,

Sayd kuwa AZIZ ya budewa sayar motar.

Fitowa qafafunsa ya ziro a natse yana fitowa sanyeda navy blue wata tsadaddiyar cashmere data fidda tsananin haske da kyan fatarsa da hutu ne kawai a bayyane koina na aji.

Gabaki daya sun Maheer zuba masa idanuwansu sikai aura dinsa na cike idanuwansu da kuma asalin nutsuwa da steez dinsa.

Hannu ya miqa a natse ya budewa Falaq mota wadda a duniya ita kadaice yakewa hakan.

Kallan wanda aka budewa mota sukai suna jiran ganin ko matarsa ce suka ga Yarinya qarama ce wadda kai tsaye suka fahimci itace 'yar da babu abinda yakaita mahimmanci kaf rayuwarsa.

Fuskanta dauke yake da murmushi koda ta fito sanye da doguwar riga lilac da mini hijab dinta.

Hannunsa ta kama cmda sauri cikin nata tana murnan sunzo baqon guri sbd tanason shiga mutane sosai sbd ta taso a killace.

Mama da Fiddausi ma cikin walwala suke ganin daga karshe ya yadda zasuyi muamala da mutane sosai tinda gasu a cikin wani familyn sun kawo ziyara wanda sai wanda ya yadda yayi kusanci dasu yake hakan.

Cikeda sakewa da farin ciki tareda bayyanarda shaquwa Maheer ya miqa masa hannu yana cewa

"Welcome to zaadens LIMBA"

Dagowa yayi yana miqa masa hannunsa tareda sakin wani lafiyayyan murmushin daya saka Zuciyar Jannah data sako kai dauke wuta cak tana kallansa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan na meneneba batareda ta qara taku ko daya ba...

Anny data sako kai tareda jannah din itama wutar ta dauke tana zubawa masa dukkanin idanuwanta zuciyarta na ambatar sunan Allah.

Dad cikin sakewa da bayyanarda farin cikin samunsa a gidansu yau din ya miqa masa hannu shika ya miqa masa yana cewa

"The pleasure is mine"

Ammar ma cikin danne abinda yakeji ya sake fuska cikin nuna farin cikinnsa yai masa welcome.

Saleem kuwa da farin cikin ganin AZIZ din yake tin daga zuciyarsa murnan haduwansu ya bayyana masa suna qarasawa ciki.

Mimi datake fitowa daga dining room da aka gama hadawa da farin ciki ta tarbi su mama tana musu sannu da zuwa.

Itama maman cikin sakin fuska take amsawa.

Anny juyowa tayi ta kalli jannah data kasa motsawa jikinta a sanyaye musamman daya rabata ya wuce ciki batareda ya lura da ita dinba a karo na biyi kenan yana mata hakan yabarta da kamshinsa daya saka kanta cakewa tana kasa dauke idanuwanta akansa.

Anny zuba mata idanuwanta tayi tana nazartanta batareda tace komaiba....

Me yake shirin faruwa?
Me jannah ke tinani?
Cabdijam" tafada a fili tana shiga lissafin da idan har hakanne to wlh saita tabbatarda hakan ya faru sbd a yanzu da AZIZ LIMBA yake gabansu to iya business dashi ba shine kadai zai fiddasu ba suna buqatan hada family dashi ta hakan ne zasu shiga dukiyarsa su juya a cikinta su samesa yanda sukeso,
Dan Maheer na buqatan sanin hakan indai neman mafita suke kuma a saukake Lamarin zaizo indai Jannah ta kamu da tsananin son AZIZ din dan haka tayi Alqawarin sakawa jannah din tsananin son AZIZ LIMBA batareda saninta ba sbd kamuwa da sonsa kawai zaisaka familyn su hana aurenta da Ammar su aura mata wanda takeso...

Wani Murmushi ta sake tana kallan jannah din cikin tausayi dan babu alamar Akwai mace ma rayuwar LIMBA bare soyayya...

Taba jannah din tayi ahankali tana cewa

"Cewa Jan muje ko"

Ciki suka nufo Anny din na gaba Jannah na bayanta a natse.

Dad ne dasuke zaune suna magana kowa a cikin wayewa da arziki daya gama hudasu ya kalli jannah yana miqa mata hannu yacewa AZIZ

"Meet the princess of d family JANNAH ZAD my daughter"

Dago Fararen idanuwansa yayi an natse ya saukar akanta daidai itama ta dago tana kallansa bayan ta kama hannun dad dinta ta zauna kusa dashi.

Fuskanta yayiwa kallan Minti daya yanajin wata wuta me zafin gaske tana cin zuciyarsa,
Kallanta kadai qona rahamar idanuwansa yakeyi...
Chapter 59 · 0% Book details