← Book details Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 120

Sashe 31

Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tashin hankali iyalan gidan Baba alhassan da gidansu mama suka shiga me girman gaske tareda kukan da basa ma sanin ya kufce musu cikin rikicewa da tsoro me tsanani ganin gawar Ummitah.

Sayyid koda suka iso baya gani kwata kwata makarantar lokaci daya ta kamasa sbd kuka da tsananin ciwon da kirjinsa yakeci mai tsananin gasken da yana buqatan ganin likita amma ba wannan damar.

Mama ma riqota akai aka shiga da ita gidan baba alhassan wanda a gidan zaayi komai.

A dakin Ummitah aka kwantar da maman wadda itama ganinta da jinta yake daukewa ahankali.

Kasancewar yamma tayi sosai ga gawar ta jima dan haka ba bata lokaci aka fara shirin janazarta wanda Mama da Sayyid ne sukai qarfin hali da dauriyar yi mata wankan gawa da shirinta wanda mama bata gani kwata kwata sosai daurewa kawai takeyi sbd yiwa Ummitah wankan karshe da kanta.

Sayyid ma hakan ne daga garesa sedai qaramin dinkin dayake kirjinta ya zubawa ido yana goge mata shi sbd baisan yaushe taji rauni a gurinba sabo hakan,

Fuskanta ya dawo da idanuwansa yana fasa kukan dayake riqewa yana kasa cigaba sbd numfashinsa dayake sarkewa da sauri aka fitar dashi matar Babansa da mama ma datake kasawa suka qarasa shiryata cikin suturarta ta karshe a wannan lokacin ne zuciyar mama ta gasa itama sedai aka fiddo da ita bayan an fice da gawar Ummitah din wanda Hankalin kowa yake qarasa tashi anata kuka da firgicin tareda tsananin tausayin Dan uwanta dako gawarta Allah bai basa ikon gani ba wanda sunsani har abada bazai taba dena fita daga radadin hakan ba,

Mahaifinsa ya rasu batareda yayiwa gawarsa kallan karsheba sbd babu abinda ya rage a gawar mahaifin nasa wuta ta cinye,

Mahaifiyarsa ta tafiyarta tin yanada kuruciya,tana taye ko a mace bai samu ganin gawartaba itama,

A yanzu ya rasa rai mafi soyuwa a rayuwarsa amma bai samu ko sassaucin ganin gawartaba.

Wannan tinanin kadai yake sake saka mama da duk masu kaunarsa shiga mummunan halin dayake hana zuciyarsu samun sauki.

Sayyid ana saka gawar Ummitah kabarinta yaji wani irin Nauyin daya danne kirjinsa da har abada bayajin zai sauka,
Ahankali hawayen idanuwansa sukai gangarowan dayake jin duminsu har a kirjinsa da tafin hannuwansa dasuka Ummitah a kabarinta.

Rufeta aka fara yanaji yana gani har aka gama rufeta akai mata addua mahaifinsa ya kama hannunsa kaman makaho yana jansa suna barin makabartan yanajin duk taku daya yana rasa ruhinsa da ganinsa sbd dishi dishin dayake gani.

Suna isowa gida suka tarar da Alh saad da iyalinsa sun taho gaisuwa wanda shima yayi iya kokarinsa ne ya tarar da jana'izar amma Allah baiyiba.

Tashin hankalin dayake ciki da iyalinsa su kansu bamai faduwa bane sbd ABDULAZIZ din kawai suma suke kasa tinanin ma Halinda zai shiga din gashi suna hanya kira biyu yayi masa yana cewa a aika gidansa yanason magana dasu mama sbd kaf wayoyinsu basa shiga yanata kira tin dazu.

Kasa fada masa Alh saad yayi sbd yasan Komai zai iya faruwa da ABDULAZIZ din a inda baya tareda yan uwansa dan haka ya zabi boye masa saiya dawo.

Mama koda ake shigowa gaisuwa da magriba bata gane kowa da komai yanda ya kamata dan haka anty maryam ta sanar da Alh saad maman na buqatan ganin likita da gaggawa fa.

Daman basuda gurin kwana a gurin dan haka kwanan zaune sukai a garin ana lallabawa da mama wadda take jin kamar itama mutuwar zatai.

Yanda suka ga safe haka sukaga dare a zaune cikin qunci da damuwa da ciwon rayuka.

Ana gama sallar asuba Alh saad yace su shiry karfe goma na safe ayiwa Ummitan addua su tafi sbd akai mama ga likita.

Mama rikicewa tayi tana cewa bazata iya barin garinba har abada sbd Ummitah na garin.

Wannan kalman nata ya daga hankalinsu aka fara rarrashinta amma sam batama san tanayi ba sbd duk ta rikice kaman ta samu juyewan kai.

Baba alhassan ne da kansa ya shigo ya fara bata magana yana tinatar da ita a yanzu ABDULAZIZ ne wanda ya kamata ace duk sun duqufa roqarwa Allah ya basa dangana da ikon daukan kaddara ya samu sassaucin abinda zaiji tin kafin a fada masa,

Shine wanda yake tsananin buqatarta a yanzu fiyeda kowa daya rasa Ummitah sbd ita kadaice zata iya kulawa da shi idan wannan mummunan labarin ya samesa.

Ambatar ABDULAZIZ kadai idan akai saitaji tana neman sake zarewa sbd kunyarsa da shakkar yanda ma zata sanar dashi Ummitah tabarsa har abada ba dawowa sedai a mafarki ko hoto amma tabbas ABDULAZIZ na buqatanta a kusa sbd duniyarsa ce zata rushe da wannan mummunan labarin.

Addua sosai itama Mama da sayyid akai musu ta dangana aka basu suka sha kafin aka samu Maman aka tafi da ita tareda Sayyid wanda shima Saida akai musu nasiha sosai akan zamansu anan bazai taba dawo da Ummitah ba wadda babu kaunar da zasu saka mata dashi bayan Su kaunaci ABDULAZIZ su tsaya akansa batareda sun bari duniyarsa da rayuwarsa ta mutu gabaki daya akan rashintaba.

Wannan tinin da Mahaifinsa yayi masa ya sakasa jin duk wani asalin tsananin so da kaunar dayakewa Ummitah suna komawa akan Hammanta wanda zata iya bada rayuwarta akansa idan tana raye.

Babu zaman gaisuwan da zaayi dan haka Alh saad na barin garin dasu aka watse cikeda radadi da ciwon rashin Ummitah tareda tausayin yanda rayuwa zataiwa ABDULAZIZ a yanxu da babu ta baida jininsa ko daya a duniya sai abinda Ummitah tabar masa.

Tinda aka haifi babyn daga Mama har Sayyid haryanxu babu wanda yasan yanda take sbd kwata kwata sunma manta da ita matar mahaifin sayyid dince take kulawa da ita tinda suka isa .

A hanyar komawan nasu Anty maryam ce take dauke da babyn wadda sai alokacin itama ta budeta ahankali ta zuba mata idanuwanta tana kalla.

Sanyi jikinta yake dauka cikin tsananin tausayi da mutuwar jiki tana kallan kamannin Ummitah da ABDULAZIZ dake shimfide akan fuskan babyn wadda tin a yanzu da kammaninsu ta shigo duniyar wadda babu komai a cikinta sai son kai da son zuciya da gwagwarmaya tareda kaddarori masu kyau da marasa kyau.

Ahankali ta sauke numfashi tana kai hannunta cikin sanyin jikinta daya tsananta ta rufe fuskan babyn sbd sanyin Ac dayake motar duk da an ragesa sosai sbd Babyn.

Yamma sosai suka iso Abuja suka fara sauka gidan ABDULAZIZ din Alh saad yayiwa Mama da sayyid yar nasihar hakuri da dangana kafin suka wuce bayan Anty maryam ta nanatawa fiddausi kulawa da komai na babyn dasu maman da basa cikin walwala da nutsuwarsu.

Suna ficewa Sayyid yashige yayi alwala ya fita sallan magrib bai dawo ba acan ya tsaya yana karatun Alqurani yana kuka kaman zaciyarsa zata fito kozai samu sassaucin abinda yakeji a kirjinsa.

Yana ishai ya dawo gidan ya shige dakinsa bai sake fitowaba saida safe.

Mama ma da daddare bayan Fiddausi ta gama bawa babyn madara ta sauya mata kaya da pamper sbd batai mata sabon wanka ba tinda bata iya wankan jariraiba,

Dakin maman taxo tayi sallama ta bude tashigo rungume da babyn dake bacci cikin nutsuwar maraici da batasaniba.

Dago idanuwanta da sukai laushi sosai mama tayi ta zubawa hannuwan Fiddausin datake tinkarota da babyn ta miqa mata.

Hannuwanta rawa suka fara ta dagosu tana jin rawar zuciya ta karbeta tana dorawa akan kafafunta tareda bude fuskanta dake rufe,

Tana saukar da idanuwanta akan fuskan babyn bata san lokacinda kuka me qarfin gaske ya kufce mataba tana qanqame babyn wanda take sak mahaifiyarta da tana jinjira.

Fiddausi ma hawaye ne suka fara gangaro mata wainda taketa riqewa rashin Ummitah da tausayin megidan da baya nan dana sayyid sai kuma na babyn.

Kuka sosai mama takeyi wanda ya saka Sayyid fitowa sbd yana jiyo kukan sbd kofar dakin a bude suka barta dan haka ahankali ya tako ya nufo dakin.

A kofar dakin ya dakata idanuwansa na sauka akan fuskar 'yarsa wadda yake hango yanayin kamannin matarsa akan fuskanta.

Ja idanuwansa sukai yanajin tsananin sonta dabaisan yaya zaiyi da zuciyarsa da rayuwarsa ma.

Kallanta yakeyi ba tareda ya qarasa ba ya juya yana barin gurin sbd kukan maman dayake qaruwa yana kankaro masa ciwon dayake kokarin daurewa.

Fiddausi ma juyawa tayi ta fice da dakin cikin tsananin tausayin mama dake jin inama fatima da Ummitah suna duniya su tayata kulawa da ABDULAZIZ da tasan zarewa zaiyi.

A daren mama kwana tayi rungume da yar da har lokacin basama tinanin sunan da zaa saka mata huduba ma Baba alhassan ne yayi mata yace sai ABDULAZIZ ya dawo ya saka mata sunan daya dace.

Washe gari da safe su anty maryam suka dawo gidan da mutane tareda maqota dake shigowa gaisuwa anata jajantawa tareda yiwa babyn data bari fatan rayuwa me albarka.
#MAMUH
#AZIZ AY LIMBA
#FALAQ LIMBA
#SAYYEED

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070
Chapter 31 · 0% Book details