Sashe 118
Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk yanda Jannah zatai ta hane a gane Ummah ba lafiyayya bace tana yi sbd batason kowa yayi mata kallan mara hankali ko makamancin hakan,
Tana kulawa da Ummah sosai tana kiyaye dik abinda zai tayar da ciwonta,
Bata wasa da lulurar umman ko kadan,
Itama Umman ta nata bangaren duk dare bata iya bacci kwana takeyi kulawa da Jannah bata barin sauro ya cijeta shiyasa take kwana tana kulawa da tattalinta kamar qaramar yarinya.
Sauran abokan aikinsu basu san Ummah ba asalin mahaifiyarta bace sbd kaunar da tattalin datake mata shiyasa suke dan respecting Umman kadan.
Tin jikinsu bai saba da wahala da yanayin gurinba har suka saba jikinsu ya sabu da wahalar sbd suna cikin wata na biyu a gurin.
Lokacin da suka shiga wata na uku a lokacin ne albashin da suka samu yakai abinda suke nema na tafiya gida dan haka Jannah taje ta sanar da madam tafiya zasuyi.
Da farko kamar bazata barsu tafiya ba amma ganin yanda jannah din tai wata irin rama da duhu sosai ya saka tausayinta cikata sbd yarinyar tabbas tana buqatar hutu da kwanciyar hankali koda a kauye ne indai zata samu nutsuwa.
Sallamarsu tayi ta tattara dan abinda zata basu ta basu sukai godia cikeda girmamawa suka hada kayansu akan washe gari zasu tafi.
A daren jannah bata iya bacci ba sbd bawa kanta karfin zuciyar iyawa,
Basuda komai,
Basuda abinda zasu zaunar da kansu a birni sbd a zero suke yanzu abincin da zasuci ma basuda hanyarsa matiqar bata tafi kauyenba ta nema danginsu dad din ba ta samar masu mafakar da suna fitowa zasu je su fake su dora sabuwar rayuwa daga can ba to tabbas suna fitowa garari da wulaqanta zasuyi dan haka ta zabi komawa kauyen ta karbe dukkanin zafi da tsangwamar da zaayiwa su Dad din kafin fitowarsu ta yanda koda zasu zo ta gama gyara alaqarta da dangin bazasu tozartasu ba idan sukaxo.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899
*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
97
*SHOP WITH ME by RANO*
08030811300
Best children's clothing shop💯
https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.
*************
Da wannan ta tashi da sassafe suka shirya tin asuba sukai wanka sukaci abincin data samar musu tin dare koda karfe 7 na safe tayi sun fito bayan sunyi sallama da abokan Aikinsu.
Mota suka tara suka shiga zuwa tasha,
Takardar hannunta ta sake budewa tana karanta sunan porthcrt da sunan wani kauyen dayake da nisa sosai a cikinsa wanda batama san ya zatai pronouncing nasa tareda sunan familyn Mahaifiyarsu Dad duka a jiki harma da sunanta ita kanta mahaifiyarsu dad din da hotonta danasu dad din.
Ajiyar zuciya ta sake saukewa ahankali tana lumshe idanuwanta tareda maida takardar jakarta ta rufe.
Suna isa tasha babu bata lokaci akai directing nasu ga motar da zasu shiga tareda biyan kudin komai suka shiga suka zauna daga ita har Umman jikinsu a mace.
Basuyi zaman mintina Arbain ba motar ta cika aka rufe koina motar ta tashi ahankali ana musu Allah ya kiyaye suka fita ta lumshe idanuwanta ahankali tana kwantawa jikin Ummah wadda ta fara shafa bayanta ahankali itama tanajin kamar tinaninta zai dawo sbd damuwa da nauyin kirjine ya rufeta sedai bata iya cewa komaiba.
Tafiya sukai sosai kafin suka fice daga abuja suka kama hanya dakyau.
Tinda suka hau hanya bata bude idanuwanta ba har sukai tafiyarda ta dauki awanni tukuna ta bude idanuwanta da sukai jajir tana dagowa daga jikin Ummah datai shiru ta zubawa fuskan jannah din idanuwanta cikeda kulawa da tinanin da batama san tanayi ba.
Kasa kallan Umman jannah tai sai kawai ta maida kanta ta sake kwantarwa jikinta tana godewa Allah daya kawo Ummah rayuwarta dan a yanzu batama fatan yan uwan umman su bullo takoina tana fatan Ummah ta zama tata har mutuwa.
Tafiya me tsayin gaske sukai wadda takaisu ga isa dare sosai dan haka ko bayan isarsu a tasha suka kwana cikin baqin dake kwana tasha tinda asuba aka sakasu motar kauyen da zasu tafi me tsananin nisan gaske.
Ummah kadai ta siyawa Abinci wanda itama umman bata wani iya cinsa ba sbd sun galabaita,
Jannah jin hankalinta na tashi tsoro da fargaban abinda zata iya tararwa na ciketa dan haka tayi shiru a sanyaye tana kallan hanya.
Sai yamma lis suka isa kauyen wanda aka ajiyesu a farkonsa,
Drivern da kansa ya hadasu da yan gari tareda fada musu gidan da zaa kaisu.
Kallansu mutane dake gurin keyi suna mamakinsu sbd ganin yanda dukkaninsu sukai laushi sosai sukai zuru zuru musamman Jannah da bata taba tafiyar mota me tsayi ba hakama a rayuwarta bata taba xuwa kauye ba batama san rayuwa a daji shine kauyenba sai yanxu data samu kanta a dajin Allah me nisan gaske.
Tsoro da fargaba me tsananin gaske ke shigarta tanajin kaman bazata iyaba amma kuma sbd samarwa ahalinta mafakar rufin asiri dole ta iya.
Tafiyar qasa suka fara a wahale cikin kishirwa da gajia amma hakanan suka daure suka ringa bin wanda aka hadasu dashi yana tafiyarsa ba gajiya ko kadan sbd sabo.
Gap da magrib suka isa cikin garin qauyen wanda sai a lokacin suka ga mutane sosai da gidaje sosai kowa na harkan gabansa,
Fulanin daji ne kaf kauyen wanda kana kallansu ba tambaya zakasan kusan kowa a garin bafulatani ne baqaqe da farare gasunan kowa harkan gabansa yake.
Kallansu akeyi cikeda mamakinsu sbd ana ganinsu anga baqin da suka taho daga nesa.
Wani gida me girma da sashe sashe suka nufa har kofar gidan matashin ya kallesu yace
"Ga gidan nan ku shiga sai kuyi bayani"
Dagowa jannah tayi ta kallesa da idanuwanta da bakinta daya bushe qayau ta budesa tace
"Mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi"
Kallanta yayi ya washe bakinsa yana cewa
"ba damuwa ai da ganinku na gida ne"
Sallama ya kwada a cikin gidan yana ambatar sunan abokinsa Garba dayake gidan.
Garban ne ya fito daman yana kusa zai fito kenan.
Washe da baki ya fito yana kallan bellon kafin ya maida kallansa kansu jannah dake tsaye a rakube.
Zuba mata idanuwansa yayi sosai yana kallanta cikeda mamaki kafin ya maida kallansa kan Ummah ya juyo gurin Bello cikin fulatanci yace
"Daga ina?
Su waye?
Waye suke nema?
Kallansu bellon yayi shima cikin fulatanci yace
"Daga binni suke nan gidan suka taho ka shiga dasu ka kaisu gurin kawu Modibbo mana.
Garba dayaji daga binni suke da sauri yana washe baki ya kallesu yana cewa
"Barkanku da zuwa,
Bismillanku"
Juyawa yayi ciki dasu yana cewa bello ya jirasa.
Suna shiga gidan jannah ta sake riqe hannun Umma suka nufi ciki har babbar tsakar gidan wanda kowa ya fito aka fara kallansu cikeda mamaki.
Modibbo ne babba a gidan kuma me fada a ji kuma mafadaci dan haka kowa hanyar dakin Modibbon ya kalla Garba na wucewa dasu can yana sake musu sannu bakinsa a washe.
Modibbo ne ya fito sanye da Babbar rigarsa datake zuba qamshin ajiya maana qamshim rima da wularsa da shape dinta yafi kama da kofin silver fari tas dashi.
Yana ganinsu sake gyara zaman hularsa yayi yana kallan Ummah ita datake babbah sai yaga ta sauke kallanta qasa.
Jannah ya maida kallansa kanta yana cewa
"Garba su waye?
Daga ina kuma?
Sake washe baki garba yayi daidai nan kawu Isiya da kawu jibo suka iso suna kallansu jannah din dukansu baki a sake.
Garba yace
"Modibbo baqi ne daga birni nan gidan suka taho"
Maida kallansa kansu yayi yace
"To baqi barkanku da zuwa,
Daga ina?
Numfashi jannah ta sauke ahankali ta bude bakinta jikinta na mutuwa gabaki daya tace
"Sunana Jannah Zadeen jikar Hajiya Zeenah Zadeen.....
Tsit sukai gurin gabaki dayansu tareda kallan junansu cikeda mamaki a bayyane kafin Modibbo ya hade fuska yana cewa
"Kikace jikar haj zeenah??
Yar Mahmoud ko Ahmed?
Sake sunkuyar da kanta tayi ahankali ta bude baki tace
" 'yar Ahmed"
"Da wane shedan zan iya gane hakan??
Hannunta ta zira a jakarta ta ciro hoton kakarta dasu Dad ta miqa masa.
Karba yayi su kawu isiya na sake matsawa da sauri duba hoton suma cikeda mamakin abinda ya kawota gurinsu.
Zubawa hoton idanuwansu sukai suka kafawa yar uwarsu idanuwansu sbd da mahaifin daya haifesu su ukun da haj zeenah din uwa daya uba daya suke.
Shiru sukai kafin Modibbo ya dago ya zuba mata idanuwansa yana karantar kamannin Mahmoud da Ahmed daya sani tin suna yara suka taso tare amma tinda mahaifinsu yayi kudi ya bar qasar dasu basu sake nemansu ba haryanxu.
Cikin nutsuwa da sanyi yace
"Ina su Mahmoud da Ahmed din suke??
Dago jajayen idanuwanta tayi ahankali kai tsaye ba kwana kwana sbd batada karfin tsayawa boye komai sbd so take su karbeta a yanda Allah ya maidasu tace
"Daddy Mahmoud ya rasu,Mimi ta rasu,
Dad da sauran yan uwana biyu suna gidan yari sai bayan shekara guda zasu fito"
Da sauri dukkaninsu suka kalleta kawu isiya na cewa
"Mahmoud ya rasu??
Kasa cewa komai tayi.
Jin hakan ya saka Modibbo cewa a kaisu jannah din dakin Yakumbo su huta a basu abinci da nono me dumi su sha su huta da kyau tukuna ayi magana daga baya idan ta nutsu yanda ya kamata.
Dakin yakumbo aka kaisu matan gidan da yara na musu sannu da zuwa cikeda mutuntawa da farin cikin ganin jikar zeenah ce yau a gidan.
Kasa cin komai jannah tayi wanka tayi da ruwan sanyi a bandakin da baida rufi take sanyi da zazzabi suka rufeta.
Daqyar yakumbo ta sakata shan sabuwar madara me dumi wadda ta dan taimaka mata amma sallah kawai tayi ta dunqule guri daya tana rawar sanyi idanuwanta na tsiyayo da hawaye masu dumi.
Tana kulawa da Ummah sosai tana kiyaye dik abinda zai tayar da ciwonta,
Bata wasa da lulurar umman ko kadan,
Itama Umman ta nata bangaren duk dare bata iya bacci kwana takeyi kulawa da Jannah bata barin sauro ya cijeta shiyasa take kwana tana kulawa da tattalinta kamar qaramar yarinya.
Sauran abokan aikinsu basu san Ummah ba asalin mahaifiyarta bace sbd kaunar da tattalin datake mata shiyasa suke dan respecting Umman kadan.
Tin jikinsu bai saba da wahala da yanayin gurinba har suka saba jikinsu ya sabu da wahalar sbd suna cikin wata na biyu a gurin.
Lokacin da suka shiga wata na uku a lokacin ne albashin da suka samu yakai abinda suke nema na tafiya gida dan haka Jannah taje ta sanar da madam tafiya zasuyi.
Da farko kamar bazata barsu tafiya ba amma ganin yanda jannah din tai wata irin rama da duhu sosai ya saka tausayinta cikata sbd yarinyar tabbas tana buqatar hutu da kwanciyar hankali koda a kauye ne indai zata samu nutsuwa.
Sallamarsu tayi ta tattara dan abinda zata basu ta basu sukai godia cikeda girmamawa suka hada kayansu akan washe gari zasu tafi.
A daren jannah bata iya bacci ba sbd bawa kanta karfin zuciyar iyawa,
Basuda komai,
Basuda abinda zasu zaunar da kansu a birni sbd a zero suke yanzu abincin da zasuci ma basuda hanyarsa matiqar bata tafi kauyenba ta nema danginsu dad din ba ta samar masu mafakar da suna fitowa zasu je su fake su dora sabuwar rayuwa daga can ba to tabbas suna fitowa garari da wulaqanta zasuyi dan haka ta zabi komawa kauyen ta karbe dukkanin zafi da tsangwamar da zaayiwa su Dad din kafin fitowarsu ta yanda koda zasu zo ta gama gyara alaqarta da dangin bazasu tozartasu ba idan sukaxo.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899
*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
97
*SHOP WITH ME by RANO*
08030811300
Best children's clothing shop💯
https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.
*************
Da wannan ta tashi da sassafe suka shirya tin asuba sukai wanka sukaci abincin data samar musu tin dare koda karfe 7 na safe tayi sun fito bayan sunyi sallama da abokan Aikinsu.
Mota suka tara suka shiga zuwa tasha,
Takardar hannunta ta sake budewa tana karanta sunan porthcrt da sunan wani kauyen dayake da nisa sosai a cikinsa wanda batama san ya zatai pronouncing nasa tareda sunan familyn Mahaifiyarsu Dad duka a jiki harma da sunanta ita kanta mahaifiyarsu dad din da hotonta danasu dad din.
Ajiyar zuciya ta sake saukewa ahankali tana lumshe idanuwanta tareda maida takardar jakarta ta rufe.
Suna isa tasha babu bata lokaci akai directing nasu ga motar da zasu shiga tareda biyan kudin komai suka shiga suka zauna daga ita har Umman jikinsu a mace.
Basuyi zaman mintina Arbain ba motar ta cika aka rufe koina motar ta tashi ahankali ana musu Allah ya kiyaye suka fita ta lumshe idanuwanta ahankali tana kwantawa jikin Ummah wadda ta fara shafa bayanta ahankali itama tanajin kamar tinaninta zai dawo sbd damuwa da nauyin kirjine ya rufeta sedai bata iya cewa komaiba.
Tafiya sukai sosai kafin suka fice daga abuja suka kama hanya dakyau.
Tinda suka hau hanya bata bude idanuwanta ba har sukai tafiyarda ta dauki awanni tukuna ta bude idanuwanta da sukai jajir tana dagowa daga jikin Ummah datai shiru ta zubawa fuskan jannah din idanuwanta cikeda kulawa da tinanin da batama san tanayi ba.
Kasa kallan Umman jannah tai sai kawai ta maida kanta ta sake kwantarwa jikinta tana godewa Allah daya kawo Ummah rayuwarta dan a yanzu batama fatan yan uwan umman su bullo takoina tana fatan Ummah ta zama tata har mutuwa.
Tafiya me tsayin gaske sukai wadda takaisu ga isa dare sosai dan haka ko bayan isarsu a tasha suka kwana cikin baqin dake kwana tasha tinda asuba aka sakasu motar kauyen da zasu tafi me tsananin nisan gaske.
Ummah kadai ta siyawa Abinci wanda itama umman bata wani iya cinsa ba sbd sun galabaita,
Jannah jin hankalinta na tashi tsoro da fargaban abinda zata iya tararwa na ciketa dan haka tayi shiru a sanyaye tana kallan hanya.
Sai yamma lis suka isa kauyen wanda aka ajiyesu a farkonsa,
Drivern da kansa ya hadasu da yan gari tareda fada musu gidan da zaa kaisu.
Kallansu mutane dake gurin keyi suna mamakinsu sbd ganin yanda dukkaninsu sukai laushi sosai sukai zuru zuru musamman Jannah da bata taba tafiyar mota me tsayi ba hakama a rayuwarta bata taba xuwa kauye ba batama san rayuwa a daji shine kauyenba sai yanxu data samu kanta a dajin Allah me nisan gaske.
Tsoro da fargaba me tsananin gaske ke shigarta tanajin kaman bazata iyaba amma kuma sbd samarwa ahalinta mafakar rufin asiri dole ta iya.
Tafiyar qasa suka fara a wahale cikin kishirwa da gajia amma hakanan suka daure suka ringa bin wanda aka hadasu dashi yana tafiyarsa ba gajiya ko kadan sbd sabo.
Gap da magrib suka isa cikin garin qauyen wanda sai a lokacin suka ga mutane sosai da gidaje sosai kowa na harkan gabansa,
Fulanin daji ne kaf kauyen wanda kana kallansu ba tambaya zakasan kusan kowa a garin bafulatani ne baqaqe da farare gasunan kowa harkan gabansa yake.
Kallansu akeyi cikeda mamakinsu sbd ana ganinsu anga baqin da suka taho daga nesa.
Wani gida me girma da sashe sashe suka nufa har kofar gidan matashin ya kallesu yace
"Ga gidan nan ku shiga sai kuyi bayani"
Dagowa jannah tayi ta kallesa da idanuwanta da bakinta daya bushe qayau ta budesa tace
"Mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi"
Kallanta yayi ya washe bakinsa yana cewa
"ba damuwa ai da ganinku na gida ne"
Sallama ya kwada a cikin gidan yana ambatar sunan abokinsa Garba dayake gidan.
Garban ne ya fito daman yana kusa zai fito kenan.
Washe da baki ya fito yana kallan bellon kafin ya maida kallansa kansu jannah dake tsaye a rakube.
Zuba mata idanuwansa yayi sosai yana kallanta cikeda mamaki kafin ya maida kallansa kan Ummah ya juyo gurin Bello cikin fulatanci yace
"Daga ina?
Su waye?
Waye suke nema?
Kallansu bellon yayi shima cikin fulatanci yace
"Daga binni suke nan gidan suka taho ka shiga dasu ka kaisu gurin kawu Modibbo mana.
Garba dayaji daga binni suke da sauri yana washe baki ya kallesu yana cewa
"Barkanku da zuwa,
Bismillanku"
Juyawa yayi ciki dasu yana cewa bello ya jirasa.
Suna shiga gidan jannah ta sake riqe hannun Umma suka nufi ciki har babbar tsakar gidan wanda kowa ya fito aka fara kallansu cikeda mamaki.
Modibbo ne babba a gidan kuma me fada a ji kuma mafadaci dan haka kowa hanyar dakin Modibbon ya kalla Garba na wucewa dasu can yana sake musu sannu bakinsa a washe.
Modibbo ne ya fito sanye da Babbar rigarsa datake zuba qamshin ajiya maana qamshim rima da wularsa da shape dinta yafi kama da kofin silver fari tas dashi.
Yana ganinsu sake gyara zaman hularsa yayi yana kallan Ummah ita datake babbah sai yaga ta sauke kallanta qasa.
Jannah ya maida kallansa kanta yana cewa
"Garba su waye?
Daga ina kuma?
Sake washe baki garba yayi daidai nan kawu Isiya da kawu jibo suka iso suna kallansu jannah din dukansu baki a sake.
Garba yace
"Modibbo baqi ne daga birni nan gidan suka taho"
Maida kallansa kansu yayi yace
"To baqi barkanku da zuwa,
Daga ina?
Numfashi jannah ta sauke ahankali ta bude bakinta jikinta na mutuwa gabaki daya tace
"Sunana Jannah Zadeen jikar Hajiya Zeenah Zadeen.....
Tsit sukai gurin gabaki dayansu tareda kallan junansu cikeda mamaki a bayyane kafin Modibbo ya hade fuska yana cewa
"Kikace jikar haj zeenah??
Yar Mahmoud ko Ahmed?
Sake sunkuyar da kanta tayi ahankali ta bude baki tace
" 'yar Ahmed"
"Da wane shedan zan iya gane hakan??
Hannunta ta zira a jakarta ta ciro hoton kakarta dasu Dad ta miqa masa.
Karba yayi su kawu isiya na sake matsawa da sauri duba hoton suma cikeda mamakin abinda ya kawota gurinsu.
Zubawa hoton idanuwansu sukai suka kafawa yar uwarsu idanuwansu sbd da mahaifin daya haifesu su ukun da haj zeenah din uwa daya uba daya suke.
Shiru sukai kafin Modibbo ya dago ya zuba mata idanuwansa yana karantar kamannin Mahmoud da Ahmed daya sani tin suna yara suka taso tare amma tinda mahaifinsu yayi kudi ya bar qasar dasu basu sake nemansu ba haryanxu.
Cikin nutsuwa da sanyi yace
"Ina su Mahmoud da Ahmed din suke??
Dago jajayen idanuwanta tayi ahankali kai tsaye ba kwana kwana sbd batada karfin tsayawa boye komai sbd so take su karbeta a yanda Allah ya maidasu tace
"Daddy Mahmoud ya rasu,Mimi ta rasu,
Dad da sauran yan uwana biyu suna gidan yari sai bayan shekara guda zasu fito"
Da sauri dukkaninsu suka kalleta kawu isiya na cewa
"Mahmoud ya rasu??
Kasa cewa komai tayi.
Jin hakan ya saka Modibbo cewa a kaisu jannah din dakin Yakumbo su huta a basu abinci da nono me dumi su sha su huta da kyau tukuna ayi magana daga baya idan ta nutsu yanda ya kamata.
Dakin yakumbo aka kaisu matan gidan da yara na musu sannu da zuwa cikeda mutuntawa da farin cikin ganin jikar zeenah ce yau a gidan.
Kasa cin komai jannah tayi wanka tayi da ruwan sanyi a bandakin da baida rufi take sanyi da zazzabi suka rufeta.
Daqyar yakumbo ta sakata shan sabuwar madara me dumi wadda ta dan taimaka mata amma sallah kawai tayi ta dunqule guri daya tana rawar sanyi idanuwanta na tsiyayo da hawaye masu dumi.