← Book details Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 120

Sashe 60

Kalbima Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahankali cikin nutsuwa ya gangaro da idanuwansa setin zuciyarta dake bugawa ahankali tana dauke idanuwanta daga kallansa sbd yanda idanuwansa ke karya kuzarinta zazzabi na neman rufeta.

Kirjinta ya zubawa ido yana karantar yanda bugun zuciyarta ke bayyana akan rigar data kwanta jikinta...

Falaq dake gefensa zaune ganin yanda gurin yayi shiru ta kwantar da fuskanta gefen jikin daddynta itama tana kallan jannah wadda ta kasa bude baki ta gaidasa.

Maheer ne yake fara bayanin inda jannah din tai zama da karatunta.

Sai alokacin jannah ta bude baki a hankali ta gaidasa sedai dauke idanuwansa yayi daga bangaren datake yana maida kan dad suna magana batarda ya amsaba sbd jin muryanta tamkar xuban ruwan dalma a kunnensa,

Tsana me karfin gaske da babu sirki ko sassauci a cikinta yakewa komai daya danganceta,
Jinsa a cikinsu tamkar a tsakiyar tekun wuta yake jinsa sbd tsanar dayake musu ba yar qarama bace,
Qi da fushin dayakeji yana cin zuciyarsa baya misaltuwa amma a hakan ya daure yana zaune a cikinsu sbd a cikakkiyar sabon binciken da akai masa akansu bazai taba kaisu qasa ba ya lalata gabaki daya asali da sunansu da rayuwarsu gaba dayaba saiya shiga cikinsu,

To amma kuma abinda ya fahimta sabo a cikinsu dinma shine Jannah Zad itace kadai abinda zasu rasa su tashi aiki gaba dayansu....

Miqewa jannah din tayi tareda bawa falaq hannu tana nuna mata kofa da idanuwansa tace

"Muje gurinsu Mimi ta gaisa da????

Cikin kai tsayenta data saba sbd gatan da yayi mata yawa itama tace

"Falaq Aziz"

Murmushi me kyau jannah din ta sauke tana kama hannunta suka fice tana cewa

"Falaq"

"No i said falaq Aziz not Falaq okay?"

Dariya jannah tayi tana qarasa janta zuwa palon Mimi dasu mama sukecan fira ta barke kaman sun saba.
#MAMUH
#KALBIM

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
48
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC (kayan mata)
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4200
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki

***********
Mama da sai alokacin ta lura da Jannah ta kuma ganeta cikeda kulawa da sakewa tace

"Ah ah beauty din Falaq ce wannan ai"

Falaq dake gefen jannah din barin gefenta tayi da sauri tana qarasawa gurin mama ta zauna tana bata fuska tace

"No,yaushe na fada hakan?
She's not my beauty,i dont even like her sbd ta taba cewa wani yafi daddyna and nikima ban hada Bestyna da kowa ba"

Mimi dake kallan Falaq din cikeda kauna da kulawa dariya me nutsuwa takeyi kafin tace

"Idan kuwa hakan jannah ta fada tabbas she's not your beauty sbd daddynki yafi kowa ko??

Gyada kai tayi tana hararar Fiddausi dake boye dariyarta sbd sai yanzu itama ta gane jannah din kuma tasan mama ta kwafsawa Falaq sbd ta zubar mata da class.

Jannah murmushi takeyi tana kallan falaq din cikeda kaunarta datake jin tana gauraya zuciyarta cikin sanyi dan haka qarasowa tayi ta zauna kusa da falaq din tana miqa mata hannu sbd ta fahimta mama ta bude mata aiki ne dan haka tace

"I'm sorry for saying that amma ai a baya ne kafin na gans...."

Kasa qarasawa tayi tana cewa

"Bazan qara fadan hakan"

Juyowa Falaq tayi tana kallan Kyakkyawan fuskanta tace

"Kin yadda babu handsome kamarsa??

Zubawa falaq din idanuwanta tayi tana kallan kyan kamanninta ta kasa fadan hakan sbd idon Mimi dayake kanta hakama Anny.

Basar da zancen taso yi falaq tace

"Haryanzu baki yadda ba kenan???

Bata fuska tai tana kokarin matsawa daga kusa da ita jannah din ta riqeta tan cewa

"Na yadda mana"

Murmushi falaq din ta sauke tana cewa

"Duk da haka ban hakura ba duka gaskia amma dai na dan sauko zamu iya gaisawa yanzu"

Hannu jannah ta miqa mata tana biyewa shirmen tace

"Friends??

Kaman falaq bazata bada hannunba ta miqa mata tana murmushi.

Fiddausi cikin bayyanarda murnanta tace

"Daga karshe Falaq Aziz yau tayi qawa a tayamu murna"

Mama dariya tayi tanawa jannah din kallan kauna
Itama Mimi murmushin take tana dawo da kallanta kan mama suna cigaba da magana.

Jannah kama hannun Falaq tayi suka bar palon tana cewa Fiddausi ta biyosu.

Bedroom dinta suka nufa
Suna shiga dakin akan hoton Ammar dake gefen gadon dakin idanuwan Falaq suka sauka ta zake guntun tsoki mara sauti tana cewa

"Yayi kama da namijin witch ma"

Fiddausi data jita hoton ta kalla tana mamakin zancen da dariya lokaci daya.

Jannah kuwa zaunar da ita tayi ta kira kitchen aka kawo musu tarin kayan zaqi dasu chocolates wanda kusan taste dinsu daya da falaq wadda aka hana cin chocolates da wasu abubuwan sbd kiba takeyi.

Fiddausi kuwa jannah din take kallo wanda komai nata yake a natse cikin burgewa da tsari.

Falaq kuwa an samu abinda akeso sakewa tayi tana ciye ciye suna kallan abubuwa a ipad din jannah din suna dariya kaman sun saba.

A can palon Dzad kuwa fira ce ta business take wakana a tsakaninsu cikin sakewa da ilimi suna bayyanar masa da irin nasarorinsu na rayuwa da successful businesses dasuka diba shekaru suna gudanarwa.

Mayen murmushi akan fuskansa batareda yacika bayanin tasa nasararba tasu yake saurara yana mamakin irin yanda a zantukansu yake karantar halayen kowannesu da fahimtarsu daya bayan daya yana kokarin fahimtar waye likita a cikinsu amma dayake sunada wani irin riqe sirrinsu da kiyayewa sam babu wata alamar da zata ganar dashi komai.

Abu dayane yake sake fahimta a kowannensu shine zasu iya komai akan kaunar dasukewa junansa,
Suna tsananin kaunar junansu babu shakkar hakan tabbas,

Amma kuma jannah din dai itace tamkar zuciyar kowanne Zaaden,
Itace basa hadata da komai ko a gurin zance,
Sun nuna,sun fada kuma idanuwansu da komai nasu ya nuna hakan sbd sunason yasan da hakan sbd kiyayewa da tsaro dan yasan ko rai zasu iya dauka akanta.

Wani shegen murmushi ya sake a lokacinda ya fahimci abinda suke nufi da nuna masa hakan a cikin kwanciyar hankali da wayewa batareda damuwar komaiba.

A natse ya dan yi baya yana jingina da jikin sofan dayake da muryansa mai cikeda nutsatsiyar wayewansa yace

"Inada nawa princesses din guda biyu da ba rai kadai zan iya dauka akansu ba rayuka zan lalata ba adadi akansu,
Dayan is no more dayar kuma is my little besty da kuka gani Falaq Aziz so i understand coz atleast we have this in common"

Cikin walwala suka fahimci shima tasa 'yar ce weakness dinsa dan haka kaman yanda ya fada suma sun fahimta,

Ammar ne wanda kwata kwata ya kasa walwala yanda ya kamata sedai lura da kaman ya shima zai iya komai akan abinda yakeso kamar yarsa dan haka yaji atlast yanada abinda ya birgesa dashi dan haka ya dan fara sakewa yana shiga firar wadda Maheer da dad tini suka sake jiki suka koma tamkar sunyi shekaru dashi sbd komai nasa yayi musu dari bisa dari tin daga kan ilimin daya mugun ratsashi da attitude nasa da tsagwaron zamansa genius dan ga kwanciyar hankali irin ta wadata ba hayaniya dan haka sunga guri sukam.

Dinner sukai gabaki dayansu a dining room bayan sunyi sallan magrib.

Falaq datake dakin Jannah tin dazu
Sunyi sallan magrib tare suka fito cin abincin falaq na jin dadin yawon da jannah tai mata alkawarin zata kaita taga gurare suka nufo dakin cin abincin.

Mama da Mimi ma da suke dakin Mimin sunyo sallan dining suka nufo suna zaunawa saleem ya shigo ya zauna saiga jannah da falaq din suma sun shigo saiga Anny sanye cikin wani kayan daban tayi wanka ta sauya.

Su Dad ne zuka shigo dining room din AZIZ din na gefen dad Maheer ma na dayan gefen Ammar yana bayansu yana waya ta saka AZIZ maida hankalinsa akan wayar sbd sunan maganin dayaji ya ambata take ya fara zargin shine dr din amma kuma yana buqatan tabbatarwa dan haka a natse ya dago ya juya ya kalli Sayd wanda shima take ya fara searching sunan maganin dayaji ammar din ya ambata.

Shigowansu ta saka gurin gaurayewa da kamshin turarukansu,

Qamshin turarensa ne ya fita daban sbd shine baqo a cikin kamshin da suka saba dashi a gidan dan haka take kai tsaye su jannah din daya shiga hancinta ta dago ahankali tana kasa kallansa sbd Ammar daya futo daga bayansu yana kashe wayarsa idanuwansa akanta cikeda tsananin sonta yake kallanta yana bude baki ba sauti yace

"Hey love"
Chapter 60 · 0% Book details