← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 101

Sashe 91

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nutsuwarsa ta dawo jikinsa,ya dinga zuqar iska yana fesarwa. Ya zama dole ya nunawa matar cewa YA ISA isar kuma da bata da alaqa sam da samuwarta. Zai sanya wani tabbataccen alqalami,ya kuma zana mata rubutun da ko nan da shekara dubu duk inda taji ance wannan sunansa MUHAMMAD sai hantar cikinta ta kada......zai sanyata da bakinta da kanta ta bawa wasu labarin wannan ISA da take inkarin yana da ita.

Kiran daya shigo wayarsa ya dauki hankalinsa kadan,kamar bazai duba ba sai ya tuna jiya bobbo yanata kiransa,abinda ya sanyashi cusa hannunsa a jubha dinsa ya fiddo wayar.

Bobbo dinne yake kiransa,ya fesar da iska kadan daga bakinsa yana daga Kiran ya saka a kunnensa.

"Kana lafiya kuwa Muhammad?" Shine abinda ya fara tambayarsa bayan sallama

"Alhamdulillah bobbo" Shuru ya ratsa kadan,yanayin muryar haisam din tana qaryata masa maganarsa. Ya san halinsa sarai,idan ya boye maka abu,bai shirya gaya maka ba,barinsa shine yafi,don haka ya sauke ajiyar zuciya yana cewa.

"Shikenan.....Allah yayi muku jagora......kunyi magana ne da sultane." Kai ya gyada tamkar yana gaban bobbo din. Har yanzu yanajin daci saman harshensa

"Munyi magana.....inaso ka shaida masa na amince......ka gayawa motii amincewata shima". Sosai bobbo yayi shocked,maganan na zuwa masa a bazata.

"Muhammad.....wanne irin hukunci ne haka da sauri?" Kansa ya sake girgizawa yana hadiye wani abu da qyar. Banda bobbo dinne tsinke wayar yafi muradin yi baci gaba da magana ba,don a duk sanda yake cikin fushi irin wannan yana taqaita magana ne qwarai gudun dana sani

(Wannan din koyarwar ma'aiki ce,idan har kana da dabi'ar yin shuru a sanda ranka ya baci ko yake bace,to tabbas ba zaka zama me nadama ba,amma muddin ranka yana bace kuma kace sai kayi magana,ko sai ka dau mataki,to akwai yuwuwar nadama da danasani me yawa a tare da kai)

"Wannan hukuncin dana dauka bobbo shine abinda ya kamata nayi.....shine abinda ya dace kowanne da na halak yayi".

"Amma kana tunanin d'iyar abokin mahaifinka ta zame maka wata garkuwa ne bayan garkuwar da akayi da ita ba tare da tasan da hakan ba?". Sai a sannan maganar bobbo ma ta harba masa wani abu cikin kansa.....sai a sannan yasan AUREN zai iya zamewa mammina wani BABBAR BARAZANA koda bai nufaci ya zame mata barazanar ba,koda iya manufarsa ta nuna mata ISA ce kawai. Baisan murmushi ya subuce masa har sai da shuru ya gilma.

"Zanji komai daga gareka bobbo bayan wani lokaci......zan zameta GARKUWA ne bawai ita din ta zamemin GARKUWA BA. Namiji ako yaushe zama yake madubi bawai ya buya a bayan wani ba ya zame masa madubin ba.....namaji GARKUWA ne bobbo.....zan zame mata garkuwa saboda albarkacin SAFEENA albarkacin NANAY......zan zameta GARKUWA ne zuwa lokacin da zan amintar da rayuwarta......zan sakar mata 'yancinta a sanda dukka wasu kuraye dake farautarta suka kwanta dama.....suka tsoraci kusantar inda take. Taci albarkacin SAFEENA taci albarkacin NANAY......uwa uba kuma ZUMUNCI ya siya mata wannan damar ta qayyadaddun lokuta.....badon MORSA SAFIYYA BA....ba don SULTANE Ba......albarkacin IGIYAR ZUMUNCI.....Albarkacn nagartacciyar uwa da QODARTA har yanzu ke rayuwa jikin YARUWA GA NANAY DITA. Zamuyi sauran magana bobbo.....amma a yanxun shuru nake buqata,amma Amincewata ta isa ga sultane da motii,kome sukace bobbo na baka dama akan hakan.......TA KIRA WUTA da kanta batasani ba......tayi wasa da DAFIN MACIJI tana tunanin ordinary ruwa ne kamar kowanne kalan ruwa" Yana kaiwa nan ya katse kiran a hankali yana jin wani sassauci a ransa.

Ya sani bobbo zai iya qalubalantarsa......amna a yanzun da kwanyarsa ta harbo masa tarin gajiyar da auren Akhnan zata mallaka masa gurin sake dulmiya mammina da sanyata fiddawa duniya da nunawa duniya cewa itadin asalin CRIMINAL ce,sai yake sakejin ba wani abu da zai dakatar dashi daga karbar auren Akhnan din.

*MAMMINA*

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/11, 20:53] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 80*

"Allah ya taimakeki.....ba girmanki bane,kinfi qarfin kiyi jayayya da wani....kinfi qarfin wani dan tsako ya daga hankalinki wallahi" Tafisu ta fada cikin tsantsar girmamawa tare da son kwantarwa da mammina hankali. Da idanunta da suka sauya launi ta dubi tafisu dake durqushe a gabanta kamar me neman rahama,kamar itace tayi laifin,kallonta take sosai,tana son taji ko yaya ta yarda da kalaman tafisun akan cewa haisam din dan tsako ne,amma kuam zuciyarta ta gaza gasgata haka.

"Ina me tabbatar miki koda ace ya nuna miki taurin kai.....koda ace ya nuna miki yana kan bakansa.....koda ace ya nuna jarumtarsa.....tabbas can qasan zuciyarsa cike take da TSORO da kuma d'ar d'ar.....don ba wanda ya isa yayi jayayya dake ya kwana lafiya......ya tashi qalau cikin zuciyarsa.....kwarjininki da girman ikonki cikin qasar nan kadai ya isa kowanne dan adam shiga fargaba da zullumin saba miki". Wani numfashi sosai mammina taja. Karon farko da taji zuciyarta sam bata aminta da zantukan tafisu ba,karon farko da taji har cikin jikinta cewa zantukan tafisu na faranta mata ne zallah bawai na fadin anihin abinda yake shine gaskiyar magana ba.

Sai data tabbatar ta soma dawowa saitinta ta hanyar zuqar iska da fesarwa sannan ta kalli tafisun.

"Na rantse shine zaiyi wannan aikin.....don shi na hangowa cancantar yin aikin a sauqaqe.....sannan duka tsarin dukkanin plan din nasa ne.....QADDARAR wannan karon tashi ce" Ta fada da wani irin zafi

"Tabbas....babu ko makawa" Tafisu ta jaddada tana gyada kanta,wanda basu kai qarshen zancan ba yalwa ta shigo duka ilahirin jikin yalwa din yana tsuma.

Ido mammina ta tsareta dashi,yayin da yalwa din tayi qasa da kanta tana jiran umarnin fara magana daga gurin mammina,duk da yadda hanjin cikinta yake kaduwa. Cak mammina ta dauke kanta daga duban yalwa din,ta maida dubanta wani guri daban.

"Ki gaggauta fadin abinda yake tafe dake kafin fushina yakai ga sauka a kanki"

"Allah ya taimakeki.....tamim ne ya iso.....yace kuma cikin gaggawa yakeson ganawarku sama da duk irin gaggawar daya taba gabatarwa a gabaki".

"Ya shigo......yalwa" Ta bada umarni gami da kiran sunanta.

"Ina amsawa ranki ya dade"

"A tabbatar an nesanta duk wani me rai daga wannan area din" Ta fadi still idanunta na kallon wani guri daban,tana sauraron wani irin bugu da zuciyarta takeyi. Wani yanayi ne da muddin ta jishi tattare da ita yake alamta mata sunan MATSALA. Wani yanayi ne data tsani jinsa a tare da ita,yayi da can qasan zuciyarta yake danqare da tsanar haisam.

Silar banzayen dokokinsa ya sanya zata gana da tamim a karon farko kan wata magana da tafi.mata rayuwar duk wani me numfashi dake masarautar muhimmanci.....zata gana dashi a budadde guri irin wannan da bai dace da sirri irin nata ba.

Tafisu ta gani tana miqewa tsaye,saita waiwaya a hankali tana duban inda tafisun ke kalla.

Tamim ne ke takowa da wani irin sassarfa.....da wani irin yanayi me nuna zallar rudewa da dimuwa a tare dashi. Abinka da dogo kuma zabgegen mutum,ko ina na jikinsa gaf gaf yakeyi,har zuwa sanda ya qaraso gabanta ya kuma zube kamar me shirin tafiya sujjada.

Samun kanta tayi da gaza tambayarsa.......saita bishi da idanu sanda yake cusa hannunsa cikin babbar rigar jikinsa dake dauke da tarin aljihun da wani ma baisan da zaman wani ba,ya zaro wasu takardu yana miqasu kai tsaye ga mammina. Hannunsa dake riqe da takardun wadanda suke rawa tabi da kallo,dukkaninsu daga su har takardun shaking suke,sai kawai ta miqa hannunta ta karba din,ta koma da baya ta zauna ta fara budesu.

Wani irin yanayi taji yana saukar mata,a hankali taji ta fara daina gane komai daga karanta layi uku kadai da tayi na takardar wanda yake dauke da rubutaccen saqo da yaren oromo.

Gumi na lokaci daya ya yanko mata,iya abinda idanunta suka iya hange qwaya daya ne da take ganin kamar ga cika takardar gaba daya
"ABA JIFAR ROYAL BLOOD". Bata sani ba.....tsohon karonta da MASARAUTAR karon da bai mata dadi ba ko qanqani shine yake son farautarta a yanzu?,yake mata yawo da qwaqwalwa da kuma tunaninta?,ko kuma da gaske sunan take gani jikin takardar. Sakin takardar tayi ta sulale tana duban tamim.

"Ba karatu a takarda nake buqata ba.....don ba ita na aika ta samomin muhimman bayanai ba.....NAMIJIN DUNIYA TAMIM nake buqatar gani a gabana.....ba zaburarren bawa ba,me kama da kazar da aka tsoma cikin ruwan sanyi". Wadannan maganganun nata sun dan tattaro kadan daga cikin qwarin gwiwar dake maqale a wani saqo na zuciyarsa,sai ya zauna sosai yana qoqarin share zufar fuskarsa.

"Uwar gijiyata....bincike ya cimma agadez!!" Ya fada da wani sauti daya aike da wani kalar razani kowanne lungu da saqo na jikin mammina. Wani irin abu yarrr ya sauka a jikinta yana zartawa har tsakiyar kwanyarta. Wani abu takeji yana kurkkurdawa kowanne lungu da saqo na jikinta,wani irin matsanancin mamaki yana cikata. Koda ace tana zaton anaci gaba da bibiyar sawunta ne.....amma koda wasa.....ko a mafarki bata taba tunanin akwai wanda hasashensa zai kawo ga AGADEZ din ba.....bata tunanin akwai wanda zaiyi tattaki ya tsoma kansa a bala'i wajen tunkararta cikin agadez ba. Agadez din da take jinta tamkar wani GIDA nata mallakinta da take da ikon sarrafashi da kuma juyashi. Agadez din da take da tabbacin ta kowacce fuska cimmata a cikinta zai zama abu me wahalar gaske.

"Wa ya taka wannan hanyar?" Ta jefawa TAMIM tambayar da idanunta da suka sauya launi tana dubansa.

"Ba'a ambaci suna kai tsaye ba......saidai inkiyar dana jima da saninta.....inkiyar dana jima da sanin tasirinta da kuma hadarin da take dashi.....bansan ma'abocin inkiyar ba......amma kuma hadarinsa kaifin kwanyarsa da tasirinsa a hukumar ya zarta na kowa.....naso sanin fuskarsa tun a wancan zamanin.....amma akwai wani irin amana da kutsen me kutse gurin samo sahihan bayanai yake wahalar gaske......"

"Duk inda kaji jita jita akwai qamshin gaskiya tattare da wannan labarin,koda kuwa zai kasance kaso casa'in cikin dari na labarin qarya ne.....mece inkiyar tasa?"
Chapter 91 · 0% Book details