← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 101

Sashe 9

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ji tayi bata da wani sauran zama a gurin,ji tayi bata da sauran abinda zata zauna tayi a gurin,tana jin idan taci gaba da zama abubuwa sake kwabewa zasuyi,idan har tace zataci gaba da zama abubuwa zasu lalace ne. Ba zata iya shuru ba,ba kuma zata iya ci gaba da saka idanu tana kallon komai yana tafiya a yadda yake a yanzu ba. Da nannie da sultane akwai wani abu daya gifta ta cikin idanunsu da batasan sai yaushe zai bude ko ya yaye ba. Bata sani ba......shin cikin qullin mammina ne data sha ALWASHI?,ko kuma tsananin soyayyar akhnan ce take jawo wasu abubuwan?.

"Ayimin afuwa......na barku lafiya" Abinda morsa safiyya ta fadi kenan tana miqewa a hankali tana jin kamar bata ganin gabanta sosai ta fara takawa tana fara fita a dakin.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Da kallo nannie ta bita,zatayi magana sultane ya daga mata hannu kawai alamun ta barta. Ya sani,zataji tsananin rashin jin dadi,ya sani zata zargeshi a zuciyarta,ya sani,zataga zallar rashin adalcinsa......to amma inda ta haqurqurtar da wannan zuciyartata me yawan fushi,me saurin fusata da zata fahimci komai bai canza ba.

"Janye auren hakeem bai canza komai ba!" Ya fada da yanayin daya dawo da hankulansu mammina kanshi.

"Eh......kwanan watan dana sanya na auren akhnan bazai canza ba......hakanan duk wani shiri da nayi akan bikinta ban canza komai ba......komai yana nan akan tsarinsa.......watanni biyu masu zuwa tabbas diyata akhnan zata zama MATAR AURE......" Maganan saita dan saka rudani a zukatansu,musamman zuciyar mammina dake cike da babban buri da kuma shirin da take fata ya fado yayi daidai da wannan lokacin.

"Ki gayawa 'yarki.....daga sultane of agadez......Muhammad hammud.......taci nasarar janye maganae auren hakeem a kanta......amma ba abinda zai canza wa'adinta na zama matar aure,watanni biyun aurenta.......sune watannin da take dashi na kawo duk wanda takeso........don nayi alqawari......ni ba mutumin banza bane,qafar wani d'a da zummar son ganinta ya aureta ta yanke daga zuwa gidan nan indai a kanta ne.......watanni biyu kacal take dasu ta kawo wanda takeso ta aura.......ku rubuta ku ajiye......daga yau zuwa biyar ga watan sama,a ranar juma'a,muddin bata kawo wanda takeso ta aura ba......ni.muhammad hammud zan daura mata aure da duk wanda naga dama. Ba kuma lallai ya zama kalar mijin da takeso ba......ba kuma lallai tasan waye ba wataqila har sai ta shiga dakin aurenta......aure na dindindin.......auren da saidai a fidda gawarta daga gidansa" Ya fada da wani irin sauti daya tabbatarwa nannie da mammina ba wani sassauci ko sauyi a maganarsa.

Ba qaramar juriya tayi ba data iya shimfida tashin hankali saman fuskarta ba. Sunan ALMAZ kawai ke mata yawo saman harshe da kwanya,saidai ba yanzu ba.......ba da sauri haka ba......ba'a wannan taqin ba.......akwai ragowar taku biyu zuwa uku daya kamata tayi.

"Amma sultane......ta yaya mace kaman akhnan.......mace me tarin martaba da mutunci za'a buqaci ta fidda mijin aure a wannan tsukakken lokacin,shi baka tsoron ya zamana tayi zaben tumun dare?".

" Zaituna" Ya furta da tarin nutsuwar nan tasa da yau take cakude da bacin rai.

"Daga rana irin ta yau....bana son wata magana data shafi akhnan akan aure a sake tasomin da ita,abu daya nake jira ta sanarmin ta samu miji shikenan". Qasa tayi da kanta,wani irin farinciki yana shawagi da zagayawa da ita a duniyarta.

"Allah ya huci zuciyarka,tuba nake" Abinda ta furta kenan kanta a qasa ba tare da sun hada ido ba.

♣️:~ Juyawa tayi ta sake juyawa ita daya cikin dakin tana jin kamar wani kida ko sauti na musamman ake busa mata. Irin wannan yanayin yanayi ne da yafi dacewa ka rabashi da wani mutum na musamman daga gefenka,to amma ita din bata gama aminta da dukkan kowa ba ballantana ta saki jiki yasan dukkanin fuskokin data mallaka.

Tana da tarin girma da alfarma,banda haka tabbas ya cancanci tayi wannan juyinne a sararin da zata shaqi iska da kyau.

BURINTA MAFARKINTA da kuma MURADINTA na shekara da shekaru a yau yana dab da cika. Ta yarda a karan kanta cewa ita din WUTA ce......wata irin WUTA me tsananin had'ari duhu da kuma baqin HARSHE dake iya nakasta rayuwar duk wanda ya rab'eta.

Wannan lokacin ta jima tana jira,cikin tarin mafarkan IDO BIYU da tashayi a zaune cikin duniyarta. Wannan lokacin data lashi takobin ajiyewa kaf familyn DIORY MUMMUNAN TARIHI da zaita bibiyarsu har qarshen rayuwarsu. Wannan lokacin da tasha alwashin sanya SAFEENA kuka da hawayenta.......tasha alwashin sanyata cikin tarin NADAMA DA DANASANI koda kuwa qasa ta lullube idanunta.....koda kuwa tana kwance cikin kushewarta.......wannan lokacin wani lokaci ne daya girmimi a kirashi da DAUKAN FANSA......lokaci ne na ajiyewa ahalin gaba daya MUMMUNAN TARIHI.

Z'a haife 'ya'yan da ba za'a taba alfahari da samunsu ba.....'ya'yan da zasu zamewa tarihi BARAZANA.....'ya'yan da za'a ce zaman uwarsu JUYA shine mafi Alkhairi sama da haihuwarsu. 'Ya'yan da muddin suna raye a duniya.....muddin sun wanzu a doron duniya.....to a kowacce rana da qwayar idanuwa zasu sauka a kansu......baqinciki ne zaici gaba da hallaka zukata da yawa d'aya bayan d'aya har zuwa ranar da tarihi rayuwa da tsahon zamani zai shafe babinsu gaba daya.

ALMAZ da AKHNAN dukkaninsu cikin tarko suke......cikin tarkon da babu me iya fahimta,koda kuwa TAMIM ne......koda kuwa YALWA ce......koda sauran boyayyun ma'aikatanta ne......wannan din wani sirri ne dake tsakanin zuciyarta zuwa qirjinta kawai.
(Tofa.....me karatu?,wanne irin qudunannen sirri ne wannan?.......Allah yasa ko yaya mammina ta buda mana zuciyarta ko zamu iya fahimtar me take qullawa haka tsakanin almaz da akhnan).

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/2, 20:07] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 10*
____________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________

Batayi wani gaggawar zuwa ga akhnan ba,sai misalin qarfe sha daya na dare. Tanason tabar mata dukkan daren ya qare a tunani da neman mafita,mafitar data tabbatar bata da ita......neman mafitar kuma shine zai danganata da zuwa inda take.....zuwan nata kuma shine abu na qarshe da take fata da burin kasancewarsa.

Qasaitattun kayan baccin alfarma masu taushi da kyau ta saka a jikinta,sannan ta dora doguwar riga yalwatacciya akai,don tana saka ran daga nan ta biya ta sassan me martaba ta sake kashe awanni don sake dasa abubuwa da take buqatar sanyawa da ajiyewa cikin zuciyar sultane,ajiyar da zata mata amfani wata rana.

Daga ita sai yalwa kawai suka fita,suna ratsawa cikin gidan da sawaye suka dauke saboda kutsowar dare,sai gilmawar hadimai da fitarsa a sannan ya zama dole,da kuma masu bada tsaro na sashe sashe dama gidan gaba daya.

Sanye yake da Moroccon jallabiyya da aka saqata da wani silk yadi me sulbi da wani irin daukan idanu,yayin da qafarsa ke sanye da wani lallausan halfshoe daya dace sosai da yanayin rigar. A daren hula ce kawai saman kanshi kalar rigar,wanda yawan larabawa ke amfani da ita.

Wani irin dare ne daya cika da hasken watan da zai gaya ma mutum wata ya fara nisa,abinda yake sake zaburar dashi kan aikin kenan,ya kuma hanashi kwanciya a daren.

Target biyu yake dashi,wanda ya tabbatar yana buqatar kulawa da takatsantsan. Samun matsayin D'A a wajen sultane ba yana nufin zaiyi komai bane gaba gadi.......dole komai ya zamana akan tsari kulawa da kuma takatsantsan.

Tsakanin jiya da shekaran jiya....bayan shudewar kowacce daqiqa tunaninsa yana sauka akan banguls din hannuwanta.......abun adon da yake da tabbaci cikin kaso saba'in cewa qirar qasar ETHIOPIA ne.......abun hannu me daraja da tsada kwatankwacin wanda suka taso suka gani nanay tana amfani dasu a yawancin lokuta.

Abun ado ne da yawan matan sarauta da attajirai na qasan Ethiopia a wasu shekaru a baya suke amfani dashi......to amma aikinsa aiki ne dake tafe da yaqini da samun tabbaci gudun samun kuskure. Dole yana buqatar wannan abun hannun......dole yana da buqatar sa a hannunsa don turawa ayi masa bincike tare da bashi tabbacin wanda hasashensa ya yawaita a kai ne?.

Dakin ajiye ajiye na gidan......wani guri na biyu da shima yake cikin lissafinsa......amma kafin isa gareshi yana buqatar sanin abubuwa da yawa. Canzawar motsi zirga zirga da kai kawo na gidan daga daqiqa zuwa daqiqa.......yaya kowanne qofa window da sashe na gidan yake kasancewa daga kowacce daqiqa zuwa wata daqiqar......wannan shine abinda ya fito dashi,yana kuma tafiya ne da cikakken nutsuwar nan tasa,can qasan zuciyarsa kuma suratul rahman yake karantawa ba tare da sauti ba,sai motsawar tausasan lips dinsa da motsawar Adams Apple dinsa lokaci zuwa lokaci.

Idanunsa ya dauke daga windows din da yake qoqarin kiyaye adadinsu da kuma wadanda kake iya hangen haske a cikinsu da wadanda ma duhu ke lullube dasu,alamun dake nuna akwai guraren da masu rayuwa a ciki sukayi bacci a daidai wannan lokacin. Alamun takun da yaji shi ya sanya ya sake sassauta yanayin tafiyarsa,haruffan dake cikin surar suna sauka a zuciyarsa gami da wata irin nutsuwa,ma'anoni da girman ubangiji dake bayyana cikin ta yana jin kamar suna sauka a ruhinsa da kuma zuciyarsa kai tsaye......a daidai wannan lokacin idanunsa suka sauka a kanta sanda take takowa cike da wani kalar karsashi.

Duba na nutusuwa yayi mata kafin a hankali ya zare idonsa daga kanta yana maidawa ga inda yake sauke sawayenshi. Qasan zuciyarsa yana sake jin abu me qarfi yana dasuwa a ranshi. Ita dimma kamar wancan mutumin,akwai dan wani abu daya jirkita yanayin zubinta dana al'ummar agadez......akwai wani tasiri na daban cikin yanayinta da babu shi jikin agadasawan yankin,duk kuwa da yadda shigarta yanayinta damu'amalarta suke maidata ba'abzina ta sosai.......amma yanayin da kamannin da yadda a komai nata al'adar abzinawa ke shiga tayi kane kane ya soma d'arsa wani qaqqarfan zargi a ransa.
Chapter 9 · 0% Book details