← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 101

Sashe 78

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Iska ta zuqa sosai don daidaita nutsuwarta da hankalinta da takejin kamar tana shirin daburcewa daga sanda kallon cikin idanunsa ya zame mata wani abu na kusa kusa da tayi a yau din. Idanun da cikin mafarkinta kadai take ganin irinsu,......idanun da take tsammanin su ta gani a hippodrome,yau gasu kusa da ita ainun,kusancin da baifi banbamcin d'ani biyar ba. Kwarjinin da take hanga a nesa a kusa ya ninka wannan.......idanun sun zame mata alaqaqai din rayuwa da a yanzun cikin qasa da second ashirin na gaurayar idanunsu waje daya ta soma tunanin anya ba sihiri gareshi ba?.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/6, 19:28] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 69*

Ba wani ido daya taba hanata furta bacin ranta koda kuwa idanun mammina ne.....mamminan dake da girma da kima a rayuwarta,amma a yau da kallo daya da yayi mata ya shafe duk wani tunaninta na abinda ya kamata ta fada masa,na sanya masa iyakoki da tsaidashi daga shiga hurumin da ya shafeta. Da kallo guda daya tak taji ya saka mata wani irin fargaba da rudewar da batasan dalilinta ba.......da wannan kallon guda daya ta daina shaqar kowacce iska saita wannan mayataccen qamshin da har yau bata gaji da neman wanne nau'in turare bane haka?.

A nutse ya miqe,miqewar data sanya idanunta sauka kan qafafunsa duk da yadda take qoqarin yiwa qwayoyin idanunta control. Kai tsaye suka fada kan takalmin dake sanye cikin doguwar qafarsa. Fes take fara sol kamar bai taba taka qasa a duniya ba,yayin da baqin takalmin da aka saqashi da magi daukakar darajar fata ta dace matuqa da gaske da qafar tasa.

Karon farko wani abu ya fusgi hankalinta,ta zubawa takalman idanu sosai sanda yake matsawa baya da baya a hankali yana barin jikin dokin.

Crown half shoe ne na kamfanin Dolce and Gabbana.......irin takalmin sultane sak,takalmin da aka taba bawa sultane din kyautarsa don nuna girmamawa daga sarkin tahoua. A lokacin suna tare da sultane din,tana zaune a farfajiyarsa yana duba kayan,kurkusa lokacin da take a matsayin aminiyar sultane din,ba yanzu da komai ya sauya ba.

Takalmin ya burgeta sosai a sannan,don har sultane yana cewa.

"Inda namiji ce ke da na bar miki shi kadeejatou" Tayi murmushi sosai a sannan,ta kuma dauki wayarta tayi qiyasin adadin kudinsa. Kanta ya kwance sosai da zallar kudin da aka buga mata lissafi da CFA din qasarsu.

Idanunta take ta qoqarin zarewa,ko kuma qaryata asalin takalmin shine a qafarsa. Sam takalmin bai dace da malami ba......takalmine dake bayyana zallar kuma tsantsar mulki da iko ga duk wanda ya mallakeshi,anya ba takalmin sultane dinne ba?,idan har haka ya kasance kenan baya ga shigar sauri da yakewa sultane da dukka al'amuransa har ya fara shiga taskokinsa?. Idan hakane gaba me zai faru?,anya bazai shiga sahun mutanen da suke zuwa a madadin baqi ba amma daga baya su qwace sarauta daga anihin wanda sarautar ke hannunsu ba.

"Da ambaton Allah kadai zukata suke samun nutsuwa" Yayi maganar hankali kwance yana sakin akalar dokin. Blue eyes dinta ta dauke daga saman takalmin tana maidawa kansa,daidai lokacin da ya juya baya,bata iya hangen fuskarsa sai kwanctacciyar baqar sumar da take kwance a qeyarsa zuwa dokin wuyansa kadan,shigen yadda asalin matasan samarin BUZAYE 'yan qabilarta suke.

Wani irin taku da take iya hangen zallar izza a tattare dashi,izzar da har yanzu take qalubalantarsa akan yinta,izzar da takejin bai cancanceta ba.....izzar da take alaqantata da tsananin girman kai ne kawai irin nashi,tare dakai kanshi inda bai baije ba.

Wani abu ya mata tsaye a wuya sanda take jinsa yana magana da hadiman gurin.

"Koda dabba ne sai Allah ya tambayeku yadda kukayi kiwonta kuka kula da damuwarta,kada kuyi tunanin idan akwai zalunci gurin kula dashi Allah bazai muku hisabi akai ba,don haka ku kula" Yadda dukkaninsu suka rusunar dakai cikin girmamawa ya sake tunzurata qwarai. Me yasa yana bare zai shigo masarautarsu ne har ya dinga iko mulki da kuma izza?.....don me sultane zai bar masa riqon babbar masarauta kaman masarautar agadez?,bayan shi din baqone akan komai ma. Hasalima baisan me ake kira da sarauta ba,meye hadinsa da ita?,sunyi hannun riga ta kowacce fuska. A yanzun tsakanin ita dashi batasan waye magajin SULTANE OF AGADEZ ba. Tana hangen wani girmamawa da dukka hadimai ke.masa,har tayi kunnen doki da irin girmamawar da suke mata.

Wannan bacin ran shi ya sanyata yin abinda bata taba yi ba wato kiran bawa da kanta. Yana dab da fita daga gurin yaji sautin kiran,karon farko da shima yaji bayyanar muryarta a fili irin haka,sai yaja numfashi sosai ya fesar dashi yana lumshe idanunsa gami da budesa duka lokaci guda.

Kadan kadan yakejin magananta cikin fada,kalma daya tak ya iya jiyowa.

"Akwai wani dama dana bayar na kowa ma zai iya shigarmin barga da duba dawakaina bayan ku?". Idanunsa ya lumshe a hankali yana maida hankalinsa ga maleek dake tattauna matsalolin daya hanga tattare da dokin,can qasan zuciyarsa kuma tana sake cika da mamakin tsananin girman kan dake damunta. Bai cewa maleek komai ba,har zuwa sanda shi da kansa ya sauya topic din.

Ita kanta batasan dalili guda daya da ya sanya taketa zabga fadan ba. Saita dinga jin kamar ba ita ba,kamar an canzata sanda ta baro bargar tana takowa gami da komawa sassanta. Yanayin girman kansa da izzarsa ke sake bata mata rai. Yana da wani dabi'a data lura da ita,basarwa tare da attitude na I don't care. Komai ma yana nuna bai gabansa bai dameshi ba,abinda take gani a matsayin zallar wulaqanci da kuma girman kai.

wadannan idanun suka sake gilmawa ta tsananin hijabin tunaninta,taja siririn tsaki yana qoqarin kauda tunanin gefe. Abu daya ta sani tabbas koda ba shine mutumin hippodrome ba.....komai nasu yazo da tarin tsananin kamanni,mutumin da har yanzu yaqi barin cikin baccinta,a wannan karon tana jin zata saka kudo ko nawa ne don binkito gaskiyar WAYE SHI?.

"Ranki ya dade.....mammina ta aiko tana son ganinki......"

"Bana sha'awar ganawa da kowa......" Ta amsawa birra a taqaice wadda ta karbo saqon daga hannun yalwa. Ko d'ar bataji ba soma takawa zuwa balcony dinta. Har qasan ranta tana jin wani zafi zafi na mammina.....tana kuma son nuna mata taji radadin da bata taba ji ba a tsahon rayuwarta don ta fahimci cewa ta bata mata da gasken gaske. Ta bata mata martabarta tarihinta da GIRMANTA da taketa fama riritawa,sai takai hannunta a hankali da zummar jawo mayafin kanta dake shirin sauka,nan take hancinta ya shaqi wannan daddan qamshin da duk sanda zata shaqeshi yake haifar mata da faduwar gaba.

Sake kai hannun nata tayi hancinta da sauri,sosai qamshin ya shige mata qofofin hancinta yana ratsawa a hankali yana isa ga kwanyarta dama zuciyarta gaba daya.

Dakatawa tayi da tafiyar a hankali,sunan barratu ta kira,ta qaraso a hanzarce,saita miqa mata hannunta kawai. Ta fahimci me take nufi,ta matso a hankali cikin d'ar d'ar takai hancinta ta shanshana.

"Inaso ki nemo contact na kamfanin YASMEEN.....shine kawai company din daya rage bamu yiwa magana ba akan turaren nan ba haka ne?" Kai ta girgiza cikin girmamawa.

"Haka ne ranki ya dade".

"A siffanta musu shi,ina buqatar wannan qamshin.....indai suna dashi su fadi price din da zasu siyar dashi,ni kuma zam biya ko nawa ne.....idan ma babu,muddin sun shirya samar dashi,su fadi abinda suke buqatar a basu" Ta qarasa maganar tana wucewa ciki ba tare data tsaya ko waiwaye ba.

_Hmmm,nikam akhnan me zakiyi da wannan tsadadden scent da kika qwallafa rai haka a kanshi,anya?🫣🫣....muje dai zuwa_

*MORSA SAFIYYA*

Tun daga farkon sashenta yasan akwai banbamci me tarin yawa a tattare da komai ma,abinda yake bayyana masa akwai wani abu daban da yasha banbam dana sauran sassan gidan. Kowa a nutse,cikin kuma doka da order,kowa kuma cikin tsari yake a tsaye akan nasa aikin. Sam ba maza kusa da mata,hakanan basu kusa da ainihin ginin gidan,kamar yadda ba mata kusa da inda maza suke nasu ayyukan. Surutacciyar shiga dake bayyana nutsuwa kamun kai da kiyaye doka gami da kiyaye dokokin musulunci.

Mewada ne yayi masa jagora cikin tarin girmamawa har zuwa sanda ya isa gurin da morsa safiyya take jiransa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Tunda ya doso gurin ta miqe don nuna girmamawa a gareshi,ya sauke dubansa qasa yana jin kaman ta aza masa nauyi. A qa'ida UWA take a gareshi,wani irin yanayi me kama da na nanay dinsa yake hanga sosai tattare da ita. Yadda ta tsaya tana jiran isowarsa da tarin girmamawa. Yadda tayi tsaye fuskarta a washe da wani yanayi da baiyi kama da murmushi ba.....amma yafi murmushi fidda nutsuwa saman fuska gami da nuna halin girma da dattako.

Da cikakkiyar sallama ya qaraso gurin,ta amsa masa tana furta.

"Ga guri ka zauna muhammad" Yadda ta ambaci sunan sai yaji fitar sautinta sak na nanay dinsa. Sai a sannan yake tuna me yasa lokuta da dama idan tayi magana yakejin girman maganarta,idan tayi magana yakejin kamar ya santa a wani guri?.

A nutse ya zauna,itama saita koma ta zauna tana karantarsa a hankali.

"Tubarakarrahman......ma sha Allah" Ta fadi can qasan ranta. Bataga lafin falaak ba data fadaawa wannan character din ba.....wannan nutsuwar.....wannan kamalar......wannan kamun kan.....uwa uba wani kebantaccen kyau da kuma gayu daya sake yiwa kyan ado da sake bayyanashi.

"Na gode sosai da amsa kirana da kayi akan lokaci" Ta fada tana dan duban agogonta a sace. Baiko qara minti guda tak ba daga lokaci da ta sanya na zamansu,abinda ya sake sanya wata kimarsa da darajarsa qaruwa ainun cikin ranta da idanunta.

Miskilin murmushinnan me wahalar fahimta ta saki yana gyara hannun jubah dinsa.
Chapter 78 · 0% Book details