← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 101

Sashe 5

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun daga nesa da omar ya hangoshi ya bude masa gaban motar kusa dashi,don yadda haisam din ya bashi command ya sanya baima sa salana ya tuqoshi ba,kawai sai ya karbi motar.

Tab ne a gabansa wanda yake video call shi da maleek da naseeb. Naseeb din suna guri daya da maleek ne saboda ziyara daya kai masa. Duk da yadda aiki ya banbamta musu guraren rayuwa,amma hakan baya hanasu kaiwa juna ziyara lokaci bayan lokaci. Kowa a cikinsu yana iya ziyartar dan uwansa a duk inda yake,kafin lokacin da suke haduwa ta lokaci guda dukkaninsu yayi.

Da tattausar muryarsa yayi sallama yana sako gangar jikinsa cikin motar,sam hankalinsa baya kan tab din,baima lura da ita ba,yayin da idanun maleek da naseeb da sukayi shuru suna son surprising nasa yake kansa cikin murmushin nan dake cike da soyayyar juna.

Hannu ya bawa omari sukayi musabaha kafin ya zame hannun yana azashi saman qirjinsa,sai kuma ya sake zame hannun yana neman madannin da zai bashi daman kwantar da kujerar yadda zai samu daman yin relaxing sosai. Tsaiwa kawai yayi yana kallon screen din,yayin da naseeb ya saki dariya sosai,maleek na tayashi ta hanyar murmushi kasancewar shima din ba ma'abocin yin dariya bane kaman dai haisam din.

"Mr lowering gaze......wai meye hakan?" Maleek ya tambaya da yanayin sarauta cikin jininsa shima kamar dai haisam din. Kai kawai haisam ya girgiza murmushi yana qwace masa,omari ya shammaceshi,hakanan wannan karon yaji kunya ta yadda aikin gaba daya ya shagaltar dashi daga barin nemansu.

"Wanne irin aiki ne ya shagaltar dakai haka?.....na dauka wata me rabon muka samu data dauke mana hankalin sheikh dinmu?" Maleek ya sake fadi yana murmushi.

"Ka sani ko ya samu nasarar kammala aikinsa da kuma gwagwgwabar kyautar princess of agadez?" Naseeb ya fada yana dariyar tsokana. Tsokana dabi'ar naseeb ce,har sun riga sun saba da haka,amma wannan karon maganansa ta yiwa haisam girma tare da maido masa mode da dabi'u dukka na akhnan daya sani,da sauri ya furta.

"A'uzubillah......a'uzubillah" Gami da miqa hannu ya kashe gaba daya karatun qur'anin dake tashi can qasa ta speakers din motar.

Harara ya fara watsawa omari........ya tabbatar akwai wata magana da suka fara dasu naseeb din,sai omar din ya fuske gami da mazewa yaqi yarda ya kalleshi,duk da yadda yakejin nauyin idanuwansa kamar kullum

"Don Allah......na roqeka wannan maganan ya fita a bakinka naseeb koda wasa kake......ban shirya wasa da zazzafar wuta ba" Ya qarashe maganan yana hade tafukan hannayensa biyun guri guda alamun roqo.

Dukkansu dariya ya qwace musu,maleek ya jinjina kai sannan yace.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Me kake tsoro obbo?......There's no woman on earth you can't deal with". Kansa ya jinjina a hankali yana kadashi. Ya lumshe idonsa a nutse sannan ya bude yana motsa labbansa da yanayin daya tabbatar musu akwai gajiya a tattare dashi,walau ta jiki kota tunani.

"I want peace always.......am not interested in drama". Maganansa ya sanya omari da naseeb sakin qaramar dariya,yayin da maleek yayi murmushi.

Kasantuwarsu daga gidan sarauta dukkansu shida haisam......hakan ya sanya akwai kamanceceniya na wasu dabi'u a tsakaninsu,don haka duk cikinsu bakwai din yafi kowa fahimtar haisam,saidai yafi haisam din mu'amala da 'yammata duk da cewa tsaftatacciyar mu'amala ce da yake sanya ran zaben matar aure a cikinsu. Kai ya gyada yana duban haisam din

"Kaima kasan ka taro match......tunda ka kayar da ita a gasa cikin yankinta". Kansa ya juya kadan,sai yanzu yanayin kallon da take masa ya dawo masa. Ya sani,ya kuma fahimta tanason fahimtar cewa shine abokin takararta ne,duk wani motsi da acting nata ya nuna masa hakan,saidai shi kuma sam bazai taba bata wannan damar ta gano komai ba. Ba drama ko wasa bane ya kawoshi yankinsu,ya kuma kawoshi masarautarsu,yazo ne kawai ya kammala wani aiki ya fice ya koma zuwa qasarsu. Aiki ne da zai tabbatar da zaman lafiyan iyayensa......zaman lafiyar qasarsa......da kuma zaman lafiyar yankinsa da qabilarsa.

Akan wadannan abubuwan daya lissafa ba shakka zai iya sadaukar da komai,shi yasa yakeji a cikin jikinsa da jininsa......ya shirya tunkarar komai don cimma nasara,musamman a yanzun da yake ganin wasu kebantattu kuma baqi sabbin abubuwa suna gilmawa ta gabanshi.

Hira sukai sosai irin ta abokai shaqiqai da suka saba da juna,hirar har takai sai da aka tabo su mutallab,dukkansu suka hadu cikin video call din cikin yanayi na kewar juna,duk da haisam din kusan yayi relaxing ne cikin kujerar,sai daya biyu kawai yake jefa bakinsa yayi murmushi a wuce gurin.

Sun saba da irin dabi'ar nan tasa,musamman a lokutan da bayason dogon magana,suma kuma sun iya tafi da 'yan miskilancinsa.

*AGADEZ PALACE*

Dukkaninsu hankalinsu idanunsu dama numfashinsu dukka sun tsaidashi ne akan doctor hadizatu data kasance qwararriyar likitar dake aiki cikin masarautar,qarqashin babban clinic na masarautar da yake aiki don duba marasa lafiya na cikin gida da ciwukansu basuyi girma da yawa ba.

A hankali ta zare allurar da kafin ta kammalata ta jiqe da gumi,allurar da tayi ta cikin cannula cikin takatsantsan da nutsuwa.

"Alhamdulillah" Ta fada tana goge fuskarta da handkerchief tana kuma kallon yadda gumi ya fara jiqa goshin akhnan.

Falaak ce ta sanya tattausan handkerchief din da aka kawo cikin tarkacen da aka ajiye a gurin ta soma share mata goshinta,yayin da aisa ta dauki remote tana dan qara qarfin Ac din dakin.

"Anyi nasara gubar ta fara sakinta in sha Allah,ga alamu nan.......amma tabbas lallai duk wanda ya kawo idea din mata allurar farko ba qaramin sanin abinda yakeyi yayi ba......allurar ta taimaka qwarai wajen saurin saukar da tasirin allurar da akayi mata yanzu.......sannna ta dakatar da harbuwar gubar zuwa sassan da idan ta tabasu to xai wahala a samu rai da rayuwa,kamar hanta qoda hunhu da kuma zuciya" Sosai wani irin kima da qaunar haisam ta sake samun kyakkyawan gurbi a zuciyar sultane. Da gaske muhammad din ya zama wani sashe me muhimmanci a tattare dashi raywarsa dama ta iyalinsa.

Baya tunanin inda bai wanzu a gurin ba akhnan zata kai wannan labarin da akeyi a yanzu......lallai yana sanya rai yana kuma kyautata zaton ubangiji ya laluba cikin tulin tarin ayyukansa ya aiko masa dashi ne kawai.

"Zata iya bacci har na awa kusan uku ko hudu,kada a tasheta,a barta ta huta sosai......idan ta farka kada ace mata komai,ku jira abinda zata soma cewa,sai a sanar dani da zarar ta farka,so samu gurin ya zama so quite" Kai morsa ke jinjinawa tana kuma fahimtar bayanan doctor hadizatu sosai.

"Ina ganin ya kamata abarta hakanan ta huta......."

"Aisa........falaak.......shehnaz.......ku zauna tare da 'yar uwarku,ku bata duk kulawar data dace har zuwa sanda zata farka". Morsa safiyya ta furta da wata kalar izza da take bayyana kanta da kanta a tattare da ita,tayi kuma maganar tata kanta tsaye ba tare data dubi koda shiyyar da mammina ke tsaye ba,wadda ke shirin tsara yadda za'ayi ta yadda zai dace da plan dinta.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/1, 19:59] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 07*
__________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________

"Hakan yayi.....don Allah.....wannan din ba qaramin abu bane da wasa ko shashanci zai shigo ciki,ku kula da ita da kyau,duk wani motsi da zai zamana kuna buqatar wani kuna iya kira" Nannie da tunda tazo ta samu guri ta zauna,gwiwarta tayi wani irin sanyi da bata taba jin tayi makamancinsa ba.

Hankali cikin kuma wani irin salo me kama da gilmawar walqiya ta shanye duk wani mamaki da bacin rai daya saukar mata na katsalandan wa umarninta da kuma hambarar da iyakokin da take qoqarin shatawa.

"Gaskiya ne.....don a wannan yanayin dole ku sake ninka kulawarku a kanta......kada sakacin da mukayi a baya ya sake maimaituwa......kada kuyi nesa da ita don Allah koda na sakanni ne" Mammina din ta fada tana sanya gefan tattausan mayafinta tana dauke hawayen daya gangaro mata.

A nutse morsa safiyya ta waiwayo ta kuma aje mata wani irin kallo kafin ta dauke kai. Har yanzu zuciyarta bata aminta ba bata kuma tsaya guri daya ba......amma kuma wani sashen na zuciyarta na gaya mata.

"Inda mammina ce.....inda mammina nada plan na kashe akhnan da bata kawo war haka a raye ba,bata kasheta a sanda take da cikakken dama a kanta ba sai yanzu data mallaki hankalin kanta?.

Kusan dukkansu morsa safiyya mammina nannie da kuma sultane suke fitowa daga bangaren akhnan din.

Ba wani a cikinsu da yake da kuzarin yin magana a cikinsu,duk kuwa da cewa kowa magana ne fal bakinsa.

"Ina gayyatarku zaman cin abinci gobe da daddare" Abinda sultane kawai ya fada kenan,abinda kuma yake gaya musu a yau bashi da muradin ganin kowa,sai yayi gaba yana ci gaba da takawa don isa farfajiyar da zata sadashi da hadimansa daya tabbatar suna nan tsaye suna jiransa a inda ya dakatar dasu.

Morsa safiyya ce ta soma yin gaba ba tare data waiwayo ko tace da kowa komai ba. Nannie ta bita da kallo kafin ta maido dubanta kan mammina.

"Har yanzu na kasa aminta da cewa biftu ce da kanta ta dauki guba tasha saboda qiyayyar auren wani?". Kaman dazun,hawaye masu yawa ta tsane da gefen mayafinta daya kasance cotton.
Chapter 5 · 0% Book details