← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 101

Sashe 59

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ka daukomin wayoyina" Ya bawa omar umarni nakai tsaye idanunsa cikin nasa don kada ma ya masa musu,saidai duk da haka saida omar ya kauda kansa kadan sannan yace.

"Ka fara maganin abinda yake damunka mana haisam kafin ka magance matsalar qasarka." Yakai qarshen maganar sanda maleek ke qarasowa dauke da tray. Yau din duk tari sarautarsa da mulkinsa.....amma abota ta gaskiya ta sanya da kansa yake hidimawa haisam. Shi kansa haisam da kallo ya bishi yana mamakin yadda ya zubda duk qasaitarsa da mulkinsa saboda abota ta gaskiya,gefe daya kuma maganar omar tana daure masa kai.

"Akwai wata matsala ne da nace maka ina da ita?" Ya jefawa omar tambayar yana tsareshi da ido,saidai sam.omar yaqi kallonsa don yasan zurfin gubar kallonsa idan yaso. Ga mamakinsa sai amsa ta fito a bakin maleek daya samu nashi gurin zaman daura da haisam din.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/31, 23:37] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 53*

"Damuwar da za'a barta cikin qwaqwalwa tafi kowacce kalar damuwa cutarwa,kasan da haka.........me yasa ka gaza fahimtar ka fara jin qaunarta cikin zuciyarka?......me yasa kayi fatali da komai?". Sosai maganan maleek yazo masa a bazata,ya kuma zo masa da wani irin yanayi da kai tsaye zuciyarsa ta qaryatashi.

"Wace kenan?" Yayi tambayar da alamun rashin fahimtar maganar maleek din na gasken gaske.

Idanu maleek ya janye,yana mamakin yadda haisam keta yin komai kaman baisan komai ba.

"Ka daina pretending mana haisam.....akhnan nake maka magana" Maleek ya fadi kansa tsaye yana dubansa.

Manyan idanunsa ya qanqance ciki kadan,yana ci gaba da duban maleek din.

"Maleek?.....matar aure?....matar wani?,kasan inda matatace aka kama wannan hirar a kanta kowa zai iya rasa wani sashe na jikinsa?" Yayi maganar dake nuna da gaske ne abinda yake furtawa akan harshensa shine har cikin zuciyarsa. Murmushi kadan maleek ya saki yana sake karantarsa da dukka ilimin karantar halayyar dan adam din da yake dashi.

"Matarka ce.....amma kayi sake kaje ka aurawa wani.....type dinka ce haisam.....itace kalar matar da kake nem......"

"Stop it mana maleek!" Haisam din ya fadi da husky voice dinsa,sannan yayi shuru yana jin wani abu me kama da rai a jikinsa yana motsi.

"Bakaji me na fada ba maleek?......matar wani ce.....matar aure ce,sannan a yanzun bakaga kalar aikin da yake gaba na ba?.......rayuka ake dab da rasawa amma zancan soyayya kake maleek?,soyayya fa?,a irin wannan yanayin?,a irin wannan lokacin?" Ya qarashe maganan muryarsa tana sanyi ba kaman dazu ba.

Idanu maleek ya janye yana lumshesu sannan ya girgiza kai sosai.

"Is okay.....shikenan......amma bayan hankula sun kwanta naka bazai taba kwanciya ba.....bayan ka kammala wannan aikin a sannan ne zakasan girman aikin dake gabanka,sabon babi zaka bude captain" Maleek yakai qarshen maganar yana miqewa tsam,ya dauki mug daya na coffee kawai ya soma takawa yana barin gurin.

Wani abu yakeji yana yamutsawa a kansa da qirjinsa......yana kuma qaryata maleek karon farko a dukkanin wani hasashensa......yanaji cewa abinda ke gabansa ya danne abinda maleek din yake magana akai. Ta yaya zaiso yarinyar da bai ganta sau goma ba a rayuwarsa?,yarinya da tako ina dabi'unta basuyi masa ba?,yarinyar data shigo ne kawai cikin aikinsa da tsarinsa?,uwa uba kuma MATAR WANI?,Duk da yana qoqarin ganin WAYE WANIN nan kafin takai ga zuwa gidansa?. Yana gudun isarta ga hannun mutumin da nan gaba dashi sultane zaiyi kuka......yana gudun shiga cikin tsarikan mammina da yayi imanin ta gama hada dukkan wani target dinta. Ya tabbatar da cewa wannan auren SHIRYASHI AKAI akwai tsararru kuma shiryayyun manufofi a qarqashinsa......ta yaya zai bari daidai da taqi daya ya zamana yana da gudunmawa wajen tabbatuwar tsarinta masu rushe rayuwa?.

"Bishi" Yace da omar kansa tsaye yana hade dukkanin girar sama data qasa tasa.

"Yes sir" Omar ya fadi kawai yana yunqurawa gami da miqewa yana danne wani abu me kama da dariya can qasan ransa. Yana tare da maleek a wannan hasashen,daga inda yake yana ganin zurfin nazarin da haisam din ya fada,zurfin nazari kuma yana faruwa ne ga haisam a bisa dukkan abinda ya bawa muhimmanci ne kadai.

*TAMIM*

*_MABUDI/MAFARI_*

_YANZU QADDARAR ZATA FARA_

A dukkan wani gaba ta jikinsa da jini yake iya wanzuwa a gurin....a dukkan wani tsoka dake da alhakin ji(feeling) yana jin wani gagarumin tashin hankali yana saukar masa.

Ya bude yatsun hannunsa......yayi qididdigen shekarun daya dauka yana bauta mata har sau ba adadi......yayi lissafi har baisan sau nawa ba......ya sake maimaita lissafin har yana bacewa daga qa'idarsa.

Yayi YAKANA yayi JURIYA ya kuma KAUDA KAI daga kan yarinyar a dukkan shekarun. Ya adana ya kuma tattala dukkan wani KWADAYINSA duk da irin tarin damarmakin da ya samu,yake dashi akan tabbas ZAITUNA zata fahimceshi tun bai furta abinda ke ransa ba......zaituna zata fahimci yaren cikin idanunsa da zuciyarsa ta kuma tattala masa TUKUCINSA a sanda zai buqaci haka. Yayi zaton shiga tsakanin burin TUKUICINSA mutuwa ce kawai,wadda yayita addu'ar kada ta daukeshi ba tare daya cika wannan burin nasa ba.

Yayiya qoqarin sake tunzura wutar nesantata da kowanne d'a namiji,a fili da bayyane,ya samu nasarori masu yawa,ya kwanta duk wata qura da tashin hankali sun biyo ta kansa,sai yanzu kuma ya zamana cikin HASARARRU?.

Qafarsa ya buga,yana jin wani qarfin zuciyar tunkarar duk wani abu da zai masa silar rasata ko nesantata dashi komai girmansa......ballantana almaz din da ta kowacce hanya yana da qarfin ikon ruguzashi ya kuma ruguza komai cikin sauqi.

"Giwa na kiranka shugaba" Yaji an furta daga bayansa cikin girmamawa. Waiwayowa yayi ya zuba idanu akan bawan. Bawan da akayi domin ya zama photocopy dinsa,bawan daya dauka ya mallaka masa irin sunansa.

"Yaushe ta buqaci ganina?".

"Tace yanzun nan,don tana da baqin da take sallama". Siririn tsaki yaja,yana jin kamar yabi shawarar da daya sashen na zuciyarsa suke bashi,saidai yaka tuna da wani abu wanda shi kadai ne yake masa shamaki.

Kewaye yaron yayi ya fara takawa ta gabansa,shi kuma ya rufa masa baya cikin matuqar biyayya.

*MAMMINA*

Idan kaga yadda take hidima cikin jama'arta,gami da kai kawo a cikinsu,ci gaba da rabon kyautututtuka masu nauyi da girman gaske ga duk wanda Allah ya tsaga yana da rabo. Ta bude qofa sosai ga.masu son ganinta da masu son gaisheta saboda yanayin farincikin da take ciki,tana so kuma ta sake jaddadawa kowa,kowa kuma ya shaida cewa da gasken gaske tana auren diyar da tafiso duk duniya ne sama da kowaaka.

Daga yanayin giftawar yalwa ta tabbatar da isowar tamim,don haka ta miqe tana bada umarnin dakatar da ganinta har sai zuwa gobe.

A yau akwai abubuwa da yawa da takeso ta dasa harsashinsu,harsashin da zai zama wani tushe kuma sanadin da zai qarasa tarwatsa rayuwar dukkan wani mutum daya kasance ahali ko tsatson diory hamani......zai qarasa sanya giyar takaici baqinciki da bacin rai cikin ruhi da gangar jikin duk wani ahalin safeena......giyar bacin ran da zata yita bugar da kowannensu har izuwa numfashinsa na qarshe.

Yana tsaye saman qafafunsa,yana kuma goye da hannuwansa a qirjinsa,saidai takun shigowarta ya sanyashi daidaita nutsuwa da yanayinsa zuwa yanayin da suka saba.

"Zauna" Tace da tamim bayan ta zauna. Zama yayi kaman yadda ta buqata,saidai kuma zuciyarsa tana gaya masa a irin wannan lokacin kamata yayi ace darajarsa ya d'aga daga wadda yake kai yanzu zuwa mataki na gaba.....matakin daya tabbatar banda tayi masa shigo shigo ba zurfi da qudundune shine yanzu akai,ba wancan tsintaccen magen ba almaz.

"Ina fatan gidan ango ya kammala ko?" A nutse tamim ya jinjina kansa,yana jin wani abu me ciwo yana tsaye masa a wuya

"An kammala komai"

"Yayi kyau.....inajin dadin aikinka tamim qwarai da gaske......a bisa al'ada yau zataje ta kwana a gidan,gobe da asuba ya rakota da kanshi.....to amma nasan abune me wahalan gaske ta yarda da hakan,don haka na yanke shawarar fara qulla kusanci a tsakaninsu....." Saita dan dakata tana sanin murmushin dake nuna zallar farinciki.

"Zai bita Niamey a satin nan kamar yadda ta tsara zata tafi,duk da har yanzu ban yarda zai iya karbarmin ragowar kamfanin sahel ba......amma tafiyarsu tare nada tarin alfanu masu yawan gaske......a yau zan tilasta mata ganawa dashi koda ba zata shiga gidanta ta kwana ba......akwai maganganun da nakeso yayi da ita,na sanya an rubucesu a killace....duka hirar da zaiyi da ita yau a killace take a rubuce,banason ya dara daga abinda na tsara. Yana da kwanya fiye da yadda kake tunani,tabbas nasan zai haddaceta kamar yadda nakeso,kaje masa da ita,da yammaci ina buqatar a rakoshi cikin ayari.......ya zamana cikin shigar alfarma ta gasken gaske......ka tunasar dashi,kada ya nuna zalama ko rawar kai.....kada ya nuna mata damuwa ko kulawa me yawa.......a jininta ta tsani wadannan dabi'un.....amma a halittarta tanason namijin dake dasu". Mammina takai qarshe tana bashi takardar dake ajiye a gefe tuntuni.

"An gama....cikar umarninki shine muradinmu" Ya fada da zallar girmamawa yana hade hannuwansa guri guda. Murmushin farinciki ta saki tana gyada kai.

"Saura kadan na mallaka maka shugabancin gidannan tamim......yadda kayimin rana da alfanu masu yawan gaske,dole kaima ka amfana daga falalata me fadin gaske" Ta fadi da gasken gaske saboda jin dadin yadda ko sau daya bai taba jawo mata asara faduwa ko musanta umarninta ba.

Kai ya jinjina mata yana jaddada godiyarsa,saidai kuma abinda ke kaikawo a zuciyarsa yasha bambam da tazara me tarin yawa da abinda ke bayyane a zahiri.

Iska ta zuqa me yawa tana fesar da ita,har yanzu murmushi yaqi gushewa daga kan fuskarta,saita kira yalwa da dama ba nisa tayi ba.

"Ki daukomin alkyabbata,zani gurin akhnan".

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"An gama" Ta amsa mata tana fita da sassarfa.
Chapter 59 · 0% Book details