Sashe 30
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Barka da warhaka sheikh muhammad" Tunda ta shigo ta karanci akwai abinda xai iya faruwa masu shige shige da wannan......akwai wani abu daya tsinto cikin muryarta da yake gaya masa confidence din data aro,wataqila don ta cimma wani abu ne.....ko don ta nuna cikin harin jiya ba abinda ya tsoratata ko kadan......saidai yafi karkata ga cimma wata buqatar.....don tun daga daren jiya zuwa safiyar yau ya samu labarin nasarar dasa kakkaifan tsoro da sukayi cikin zuciyarta.
Da kalar girmamawar data bashi ya amsa mata gaisuwarta,sai taji wani iri,don bada wannan salon bada wannan harshen taso ya fara karbarta ba a karon farko ba a gaban sultane.
"Khadeejatu baki gama shiryawa yin maganan bane?" Sultane ya furta yana duba agogon hannunsa. Numfashi ta sake ja kamar zata zuqe dukka isar da tayi saura a gurin,ta daga kai a sace tana duban mammina. Taji a jikinta sanda mammina ta shigo mamminan zata saita komai......zata sanya sultane ya tashi wannnan malamin daga gabanta......daga cikin shirgin daya shafesu.....cikin al'amuran da suke kebantattu garesu.
"Muhammad haidam D'ANA ne......dan sultane muhammad hammud agg abba ne daya cancanci komai.....yake da ruwa da tsaki da dukkan komai" Kai tsaye sultane yayi maganan data daure musu kai gabadayansu..basusan daga inda maganar ya samo asali ba,basusan daga inda maganan ya dauko ba.
Ido ta samu ta hada da mammina ko akwai wani taimako?,saidai idanu ta juya mata abinda ya alamtawa akhnan ba wani sauran abinda ya rage banda ta fasa maganar a gaban wannan malamin. Nazarinsa ya janye daga kan matar yana ganin yadda tayi amfani da idanunta ta sarrafa tunanin akhnan din,sarrafawar da lafazin mahaifinta ya gaza yinsa wanda ke dauke da sautin gargadi da wani tasiri kadan na bacin rai a cikinsa.
"Done" Ya fada can qasan ransa,abinda yake buqata ya tattara a kanta kaso saba'in cikin dari ya kammala,iya wannan kason kawai ya isheshi ya afka cikin bin diddigin kowanne motsinta har zuwa sanda zai san alqarta da mutanen da suke farauta.
"Bappi......na fitar da mijin auren kamar yadda ka buqata".
[1/15, 20:01] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 27*
Tsit parlor din yayi,wani irin shuru ya ratsashi kamar ba sauran halitta a cikinsa data rage. Zukatan mutane biyu suka shiga nazarin kalmomin da suka fita a bakin akhnan din.
D'aya bayan daya haisam ke fasa kalaman bakinta.......bawai don bada hankali akan masa'alar da bata shafeshi ba,don shiga nazari a kalamai daga bakunan mutanen da bai gamsu da maganganunsu ba ya zame masa dabi'a.
Introvert person ne na gasken gaske. Wanda shurunsa yakan zama nazari ne......kauda dubansa yakan kasance hakaltar dan adam. Yanayin kaman bai gani ba kuma ya gani,zaka dauka ya manta amma yana hankalce......yana ajjiye da komai. Ba komai ke burgeshi ba kaman yadda ba komai ke bata ransa ba,ko yaya yake akwai alamu na rashin gaskiya a tattare dakai yana iya fahimtar hakan,omari yakance.
"Me laifi kamar wani qamshi daban yake maka cikin hancinka?" Murmushi kawai yake baiwa omari amsa dashi,shi kansa a lokuta da dama mamakin kansa yakeyi. Sake janye nazarinsa a kanta yayi ya maida kan mammina da tayi qasa da kanta. Iya nutsuwar da yanayinta ya nuna kadai ya tabbatar masa tasan komai......iya yadda tayi shuru kawai ya tabbatar masa akwai wani abun a bayan shurunta. Me yasa sultane bazai fahimta ba wai?. Ya samu kansa da tambayar kansa da kansa. SULTANE BA IRIN KAI BANE......MUTANE DA YAWA BA IRINKA BANE. Amsar da zuciyarsa ta bashi kenan ta kuma tilastawa kanta da kanta yin relaxing.
"Kula da al'amuranta da suka shafi bincikenka shine priority dinka.....shine dolenka,dole komai ka barshi a inda ka ganshi,dole komai ka barshi a yadda yake indai bai taba bincikenka ba....hakanne kawai zai baka nutsuwa da tafiyar da aikinka kadai cikin tsari da yanayin daya dace" Ya fadawa kansa da kansa,sai ya samu kansa da zare duk wani yanayi da aikinsa daya soma hawa kan ruhinsa da zuciyarsa.
Zuciyar sultane taci gaba da harba jini a hankali,yana jin sauran buri da fatansa yana kwaranyewa. Mafarkin da yasha shafe darare yana yi......addu'o'in da yafi tunanin rashin alkhairi da rashin dacewar abun ubangiji ya kalla wataqila ya dakatar da amsar addu'arsa. Sai da yayi gyaran murya
"Ma sha Allah......Allah yasa albarka,na tayaki murna.....amma kuma.....sanda kika shigo banga kin gaida WALIYYIN naki ba" Ya furta maganan yana tsare akhnan da ido. Idanunta ta daga da sauri abubuwa biyu suna dukanta. Yadda SULTANE yayi accepting maganan cikin sauri?,cikin sauqi?,ba tare da kalar kowacce tambaya ba?,ba tare da kalar kowanne challenge ba. Maganan WALIYYI ita tayi Mata tsaye a rai,tana son banbance ma'anar waliyyin da ya furta,amma kwanyarta ta kasa wani cikakken aiki a wadannan mintunan,sai tayi qasa da kanta tana jin muzanci yana bin sassan jikinta da jininta gaba daya. Muzancin da bata taba jin kalarsa ba tana jin yadda kalaman sultane ke raunata duk wata izza tata daya kamata ya zama na farko wajen dagata tana fadin.
"Barkanka da safiya". Da fari kamar baiji maganan nata ba,don ba a nan hankalinsa da lissafin abubuwa masu muhimmanci a wajensa yake ba,amma sai zuciyarsa ta harbo masa muryartata,abinda ya jinkirta amsawarsa kadan kafin yace
"Barka". Kai sultane ya jinjina,yayin da yanayin amsawar tasa ta sake danqara wani irin zafi saman zuciyarta,zuciyar daketa kokawar gano WALIYYINKI da sultane ya fadi,saidai kuma bai barta tayi nisan zango a tunani ba ya gajarta mata komai ta hanyar fadin.
"Juma'a......juma'a me zuwa ba wannan da muke ciki ba za'a daura aurenki da mijin da kika gabatarmin din......in sha Allah sheikh haisam zai wakilceni zai zama madaurin aurenki!". A razane ta dago kai......ba kuma ita daya ba,hatta da mammina maganan ya razanata. Bata razana bane don daura auren akhnan da aka zabge masa kwanakin wata ba......ta razana ne saboda GIRMAN MATSAYIN da sultane ya dauka ya baiwa malamin. A iya saninta.....dauren auren d'iyar sarauta.....diya me cikakken gata,wadda izzarta darajarta da martabarta ya kerewa dukkanin diyoyin gidan sarautun da nijer ke dashi......waliccin aurenta wani abune me tsananin tsada da kowa ke yunwar a bashi,da kowa ke fatan sultane ya zabeshi.....wani abune da zai zama GIRMA da martabawa me tarin yawa da ba zata shafe ba cikin babin tarihin rayuwar dukkan wanda aka bawa......wanne irin GIRMA da MATSAYI ne yaron ya taka haka a zuciyar sultane cikin qaramin lokaci ba tare data ankare da haka ba?.......sai a yau ta sake yadda ta kuma tabbatar da gaske ne sultane YA D'IYANTAR DASHI......da gaske ne da sultane yace YA MAIDASHI D'ANSA da gaske yana nufin abinda ya fada din......iya yau kawai ta tabbatar mata da haka.
Amma kuma tana raye?.....ta yaya zata bari haka ta faru?.....ta yaya zata bari haka ta kasance?. Ta kasa haifawa sultane MAGAJI kamar yadda ta hana kowacce d'iya mace haifa masa magaji sai magajiya qwalli biyu da take jinsu kamar wutar dake cin naman jikinta a kowacce safiya idan ta kallesu. BAI KAMATA TAYI SAKACIN DA WANI ZAI HAURO ta saman kanta ba......ya rusa duk wani matsayi kusanci da martaba da tayi shekaru tana tattalinsu ba.....bai kamata ta bari wani ya fado tsakiyar wannan kakkauren zaren data debi shekaru tana saqashi ba ya tsinkashi. Waninma da har yanxu xuciya da gangar jikinta ke alamta mata DANGER a duk wani kallo da zata aza idanunta a kanshi ba.
"Bappi......bayan dukka wanzuwar su kawu mammani dake raye?". Akhnan ta samu kanta da furta tambayar tana duban sultane da wani irin sanyin mamaki daya daketa.
Kai tsaye yake duban idanunta shima,sannan ya jinjina kai.
"Bakisan MATSAYIN D'A a wasu guraben ya haura na DAN UWA BA?......Bakisan kuma matsayin D'A wajen yin waliccin auren qanwarsa ya zarta na kawunnanta ba?" Maganar tasa ta fito da wani nauyi me yawa daya sanyata maida kanta qasa kawai. Banda tauri da kafiya gami da tsaiwa da zuciyarta ke dashi.......banda tattalinnan da takewa GIRMA da IZZARTA ba abinda zai hanata fashewa da kuka a yanzun nan.
"Amma ranka ya dade......Allah ya taimakeka.......bai kamata kafin ka yanke rana da komai ka tsaya gana da yaron ba?......kasan wayeshi da asalinsa?" Tayi maganar da sanyin murya da sanyin zuciya,sanyin daya sanya haisam tattarasu dukka ya aza saman ma'auni daya.
"Ba buqatar hakan......indai ta iya gabatarmin dashi......ta sani ya dace da dukka wani tsarinta ne......ku shirya komai,zata zama matar aure nan da kwanaki goma masu zuwa.....kaji abinda na fada muhammad?" Ya maida dubansa da tambayarsa kan haisam da yayi kaman baya wajen.
"Indai wannan din umarni ne daga gareka zan cikashi in sha Allah"
"Umarni ne haisam.....umarni ne muhammad" Ya furta cikin nuna girman umarnin nasa da gasken gaske.
"Ranka ya dade......ba kuskure kuwa?,.......ya kamata a duba.....muna neman alfarma,aure ba wasa bane.....diyarka mafi daraja zaka miqa......."
"Zaituna ya isa haka......na rufe wannan babin har abada,na rufe matsalan akhnan akan aure har abada......bana son wani ko wata su sake tayar da ita......yin hakan zai iya sawa mutum ko waye ya fusakanci mummunan hukunci daga wajena kai tsaye kuma"
Runtse idanunta tayi tana jin kamar jiri na shirin kayar da ita daga zaunen da take. Ta gaji da zama a gurin,tanaso ta shaqi wata iskar daban bayan wannan,tana jin kamar wannan iskar ta gurbace da yawa,don haka ta miqe cikin girmamawa.
"Na gode bappi......" Ta iya hada kalmomin da qyar
"Madalla" Ya amsa mata a taqaice yana kauda idonsa daga dubanta,wani abu yana cakar zuciyarsa.
"Tafiyar zata yuwu?" Sultane ya sake tambayarsa,tambayar data aza masa wani tarin nauyi ta kuma sake jan hankalin mammina cike da mamakim wacce tafiya sultane din zaiyi wadda ita bata da labarinta?.
Tafiya da sultane wani abune da zaya bata tsarin aikinsa gaba daya......dukkan wani plan nasa na kammal aikinsa cikin wata daya zuwa wata daya da rabi yana jin zai iya samun naqasu ko koma baya. Amma kuma ta yaya zai fito ya gayawa sultane haka kanshi tsaye?.
Da kalar girmamawar data bashi ya amsa mata gaisuwarta,sai taji wani iri,don bada wannan salon bada wannan harshen taso ya fara karbarta ba a karon farko ba a gaban sultane.
"Khadeejatu baki gama shiryawa yin maganan bane?" Sultane ya furta yana duba agogon hannunsa. Numfashi ta sake ja kamar zata zuqe dukka isar da tayi saura a gurin,ta daga kai a sace tana duban mammina. Taji a jikinta sanda mammina ta shigo mamminan zata saita komai......zata sanya sultane ya tashi wannnan malamin daga gabanta......daga cikin shirgin daya shafesu.....cikin al'amuran da suke kebantattu garesu.
"Muhammad haidam D'ANA ne......dan sultane muhammad hammud agg abba ne daya cancanci komai.....yake da ruwa da tsaki da dukkan komai" Kai tsaye sultane yayi maganan data daure musu kai gabadayansu..basusan daga inda maganar ya samo asali ba,basusan daga inda maganan ya dauko ba.
Ido ta samu ta hada da mammina ko akwai wani taimako?,saidai idanu ta juya mata abinda ya alamtawa akhnan ba wani sauran abinda ya rage banda ta fasa maganar a gaban wannan malamin. Nazarinsa ya janye daga kan matar yana ganin yadda tayi amfani da idanunta ta sarrafa tunanin akhnan din,sarrafawar da lafazin mahaifinta ya gaza yinsa wanda ke dauke da sautin gargadi da wani tasiri kadan na bacin rai a cikinsa.
"Done" Ya fada can qasan ransa,abinda yake buqata ya tattara a kanta kaso saba'in cikin dari ya kammala,iya wannan kason kawai ya isheshi ya afka cikin bin diddigin kowanne motsinta har zuwa sanda zai san alqarta da mutanen da suke farauta.
"Bappi......na fitar da mijin auren kamar yadda ka buqata".
[1/15, 20:01] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 27*
Tsit parlor din yayi,wani irin shuru ya ratsashi kamar ba sauran halitta a cikinsa data rage. Zukatan mutane biyu suka shiga nazarin kalmomin da suka fita a bakin akhnan din.
D'aya bayan daya haisam ke fasa kalaman bakinta.......bawai don bada hankali akan masa'alar da bata shafeshi ba,don shiga nazari a kalamai daga bakunan mutanen da bai gamsu da maganganunsu ba ya zame masa dabi'a.
Introvert person ne na gasken gaske. Wanda shurunsa yakan zama nazari ne......kauda dubansa yakan kasance hakaltar dan adam. Yanayin kaman bai gani ba kuma ya gani,zaka dauka ya manta amma yana hankalce......yana ajjiye da komai. Ba komai ke burgeshi ba kaman yadda ba komai ke bata ransa ba,ko yaya yake akwai alamu na rashin gaskiya a tattare dakai yana iya fahimtar hakan,omari yakance.
"Me laifi kamar wani qamshi daban yake maka cikin hancinka?" Murmushi kawai yake baiwa omari amsa dashi,shi kansa a lokuta da dama mamakin kansa yakeyi. Sake janye nazarinsa a kanta yayi ya maida kan mammina da tayi qasa da kanta. Iya nutsuwar da yanayinta ya nuna kadai ya tabbatar masa tasan komai......iya yadda tayi shuru kawai ya tabbatar masa akwai wani abun a bayan shurunta. Me yasa sultane bazai fahimta ba wai?. Ya samu kansa da tambayar kansa da kansa. SULTANE BA IRIN KAI BANE......MUTANE DA YAWA BA IRINKA BANE. Amsar da zuciyarsa ta bashi kenan ta kuma tilastawa kanta da kanta yin relaxing.
"Kula da al'amuranta da suka shafi bincikenka shine priority dinka.....shine dolenka,dole komai ka barshi a inda ka ganshi,dole komai ka barshi a yadda yake indai bai taba bincikenka ba....hakanne kawai zai baka nutsuwa da tafiyar da aikinka kadai cikin tsari da yanayin daya dace" Ya fadawa kansa da kansa,sai ya samu kansa da zare duk wani yanayi da aikinsa daya soma hawa kan ruhinsa da zuciyarsa.
Zuciyar sultane taci gaba da harba jini a hankali,yana jin sauran buri da fatansa yana kwaranyewa. Mafarkin da yasha shafe darare yana yi......addu'o'in da yafi tunanin rashin alkhairi da rashin dacewar abun ubangiji ya kalla wataqila ya dakatar da amsar addu'arsa. Sai da yayi gyaran murya
"Ma sha Allah......Allah yasa albarka,na tayaki murna.....amma kuma.....sanda kika shigo banga kin gaida WALIYYIN naki ba" Ya furta maganan yana tsare akhnan da ido. Idanunta ta daga da sauri abubuwa biyu suna dukanta. Yadda SULTANE yayi accepting maganan cikin sauri?,cikin sauqi?,ba tare da kalar kowacce tambaya ba?,ba tare da kalar kowanne challenge ba. Maganan WALIYYI ita tayi Mata tsaye a rai,tana son banbance ma'anar waliyyin da ya furta,amma kwanyarta ta kasa wani cikakken aiki a wadannan mintunan,sai tayi qasa da kanta tana jin muzanci yana bin sassan jikinta da jininta gaba daya. Muzancin da bata taba jin kalarsa ba tana jin yadda kalaman sultane ke raunata duk wata izza tata daya kamata ya zama na farko wajen dagata tana fadin.
"Barkanka da safiya". Da fari kamar baiji maganan nata ba,don ba a nan hankalinsa da lissafin abubuwa masu muhimmanci a wajensa yake ba,amma sai zuciyarsa ta harbo masa muryartata,abinda ya jinkirta amsawarsa kadan kafin yace
"Barka". Kai sultane ya jinjina,yayin da yanayin amsawar tasa ta sake danqara wani irin zafi saman zuciyarta,zuciyar daketa kokawar gano WALIYYINKI da sultane ya fadi,saidai kuma bai barta tayi nisan zango a tunani ba ya gajarta mata komai ta hanyar fadin.
"Juma'a......juma'a me zuwa ba wannan da muke ciki ba za'a daura aurenki da mijin da kika gabatarmin din......in sha Allah sheikh haisam zai wakilceni zai zama madaurin aurenki!". A razane ta dago kai......ba kuma ita daya ba,hatta da mammina maganan ya razanata. Bata razana bane don daura auren akhnan da aka zabge masa kwanakin wata ba......ta razana ne saboda GIRMAN MATSAYIN da sultane ya dauka ya baiwa malamin. A iya saninta.....dauren auren d'iyar sarauta.....diya me cikakken gata,wadda izzarta darajarta da martabarta ya kerewa dukkanin diyoyin gidan sarautun da nijer ke dashi......waliccin aurenta wani abune me tsananin tsada da kowa ke yunwar a bashi,da kowa ke fatan sultane ya zabeshi.....wani abune da zai zama GIRMA da martabawa me tarin yawa da ba zata shafe ba cikin babin tarihin rayuwar dukkan wanda aka bawa......wanne irin GIRMA da MATSAYI ne yaron ya taka haka a zuciyar sultane cikin qaramin lokaci ba tare data ankare da haka ba?.......sai a yau ta sake yadda ta kuma tabbatar da gaske ne sultane YA D'IYANTAR DASHI......da gaske ne da sultane yace YA MAIDASHI D'ANSA da gaske yana nufin abinda ya fada din......iya yau kawai ta tabbatar mata da haka.
Amma kuma tana raye?.....ta yaya zata bari haka ta faru?.....ta yaya zata bari haka ta kasance?. Ta kasa haifawa sultane MAGAJI kamar yadda ta hana kowacce d'iya mace haifa masa magaji sai magajiya qwalli biyu da take jinsu kamar wutar dake cin naman jikinta a kowacce safiya idan ta kallesu. BAI KAMATA TAYI SAKACIN DA WANI ZAI HAURO ta saman kanta ba......ya rusa duk wani matsayi kusanci da martaba da tayi shekaru tana tattalinsu ba.....bai kamata ta bari wani ya fado tsakiyar wannan kakkauren zaren data debi shekaru tana saqashi ba ya tsinkashi. Waninma da har yanxu xuciya da gangar jikinta ke alamta mata DANGER a duk wani kallo da zata aza idanunta a kanshi ba.
"Bappi......bayan dukka wanzuwar su kawu mammani dake raye?". Akhnan ta samu kanta da furta tambayar tana duban sultane da wani irin sanyin mamaki daya daketa.
Kai tsaye yake duban idanunta shima,sannan ya jinjina kai.
"Bakisan MATSAYIN D'A a wasu guraben ya haura na DAN UWA BA?......Bakisan kuma matsayin D'A wajen yin waliccin auren qanwarsa ya zarta na kawunnanta ba?" Maganar tasa ta fito da wani nauyi me yawa daya sanyata maida kanta qasa kawai. Banda tauri da kafiya gami da tsaiwa da zuciyarta ke dashi.......banda tattalinnan da takewa GIRMA da IZZARTA ba abinda zai hanata fashewa da kuka a yanzun nan.
"Amma ranka ya dade......Allah ya taimakeka.......bai kamata kafin ka yanke rana da komai ka tsaya gana da yaron ba?......kasan wayeshi da asalinsa?" Tayi maganar da sanyin murya da sanyin zuciya,sanyin daya sanya haisam tattarasu dukka ya aza saman ma'auni daya.
"Ba buqatar hakan......indai ta iya gabatarmin dashi......ta sani ya dace da dukka wani tsarinta ne......ku shirya komai,zata zama matar aure nan da kwanaki goma masu zuwa.....kaji abinda na fada muhammad?" Ya maida dubansa da tambayarsa kan haisam da yayi kaman baya wajen.
"Indai wannan din umarni ne daga gareka zan cikashi in sha Allah"
"Umarni ne haisam.....umarni ne muhammad" Ya furta cikin nuna girman umarnin nasa da gasken gaske.
"Ranka ya dade......ba kuskure kuwa?,.......ya kamata a duba.....muna neman alfarma,aure ba wasa bane.....diyarka mafi daraja zaka miqa......."
"Zaituna ya isa haka......na rufe wannan babin har abada,na rufe matsalan akhnan akan aure har abada......bana son wani ko wata su sake tayar da ita......yin hakan zai iya sawa mutum ko waye ya fusakanci mummunan hukunci daga wajena kai tsaye kuma"
Runtse idanunta tayi tana jin kamar jiri na shirin kayar da ita daga zaunen da take. Ta gaji da zama a gurin,tanaso ta shaqi wata iskar daban bayan wannan,tana jin kamar wannan iskar ta gurbace da yawa,don haka ta miqe cikin girmamawa.
"Na gode bappi......" Ta iya hada kalmomin da qyar
"Madalla" Ya amsa mata a taqaice yana kauda idonsa daga dubanta,wani abu yana cakar zuciyarsa.
"Tafiyar zata yuwu?" Sultane ya sake tambayarsa,tambayar data aza masa wani tarin nauyi ta kuma sake jan hankalin mammina cike da mamakim wacce tafiya sultane din zaiyi wadda ita bata da labarinta?.
Tafiya da sultane wani abune da zaya bata tsarin aikinsa gaba daya......dukkan wani plan nasa na kammal aikinsa cikin wata daya zuwa wata daya da rabi yana jin zai iya samun naqasu ko koma baya. Amma kuma ta yaya zai fito ya gayawa sultane haka kanshi tsaye?.