Sashe 29
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wannan kallon dake cike da kulawa......da wannan kallon dake dauke da qaunar datasha banbam data sauran 'ya'yan da ya haifa......qaunar da a wannan karon yake qoqarin yaqi da ita yake dubanta.
Da rusunannun idanunta ta qaraso tana yiwa kanta muhallin zama daura da falaak. Numfashinta take qoqarin daidaituwa,tana jin yadda dakin gaba daya ya gauraye da wannan qamshin dai. Wannan qamshin da har yanzu ta rasa makamancinsa......qamshin nan daya zame mata tamkar jarrabi tun daga hippodrome kawo yau......qamshin da har yanzu ta rasa waye ainihin mamallakinsa?......wanne irin turare ne wannan me kassara gabobi?.
"Barka da safiya yaa biftu" Falaak ta gaidata cikin girmamawa qauna da kulawa irin ta 'yan uwantaka. Motsa labbanta tayi da qyar tana maidawa falaak.
"Barkanki.......barka da safiya bappi" Ta furta tana rusunar da idanunta da kanta don nuna girmamawa ga sultane din.
"Barkanki kadai khadeejatu". Ya kirata da asalin sunanta,sunan da ya sauka sosai saman zuciyar haisam ya kuma maimaitashi cikin qirjinsa har sau biyu
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 26*
Sunan wani suna ne da yake da tarin daraja martaba da kima a idanunsa,sunan NANAY dinsa......halittar 'ya mace ta farko daya soma so da qauna a rayuwarsa,yake kuma qauna har yanzu,yake martaba dukkan wanda yake da irin sunan bama ita kanta din ba.
Dauke idanunsa sultane yayi daga kan akhnan din data koma wani cool,yana karantar duk wani yanayi nata da motsinta,yana kuma ankare da yadda bata gaida haisam din.
"To kaji muhammad......ita kuma qanwar naka canjin course din da takeso tayi kenan" Sultane ya fada da murmushi saman fuskarsa yana duban haisam cikin tarin kulawa da kuma kwadayin shigar haisam din kowanne al'amari daya shafi iyalinsa. Ya fuskanci har yanzu haisam din bai shiga lamarin iyalinsa da zurfi yadda yakeso ya shiga ba. Yanaso ya saje dasu ya dinke dasu sosai,ya zama ba wani banbamci ko kadan a tsakaninsu.
Wani miskilin murmushi daya kashe zuciyar falaak ya kuma sanya gabanta tsananta faduwa ya saki,ya tashi ya gyara zamansa sosai yana duban sultane.
"Ana iya bata dama a ganina.......abinda ta buqata bai sabawa ra'ayinka da burinka ba......bai kuma sabawa addini da al'adarta......ubangiji zai sanya albarka sosai a ciki".
"Gaskiya ne" Sultane ya fadi cikin tsananin gamsuwa yana gyada kanshi. Daga qasan ransa yana jin kamar akwai wani saqo da yakeson isarwa ne me matuqar muhimmanci.
Iska ta zuqa sosai cikin kiyayewa da fitar numfashinta,ta qanqance idanunta kadan tana jin saukar maganarsa cikin tsakiyar zuciyarta,tana jin maganarsa kai tsaye tana tunkarota da wani irin yanayi me qarfin gaske. A hankali zuciyarta ta fara maimaita mata DAKE YAKE,maganan ta soma takura zuciyarta tana son tilasta mata jin muzanci,muzancin da alfaharinta da izzarta suka hana ya mamayeta.
"Zan baka mamaki......zan kuma kunyataka gaban sultane tabbas.......sai sultane yasan kaine namiji na farko daka fara hada jiki da diyar da yafi qauna duk duniya har sau uku!" Ta dire alwashin cikin zuciyarta tana jin qwarin gwiwar kiran sunan sultane din.
"Bappi......" Ta kirashi tana sunkuyar da kanta
"Khadeejatu" Ya amsa mata kai tsaye.
"Zan iya samun mintuna biyar?". Idanu sultane ya dan zuba mata sannan ya waiwaya ga falaak.
"Tashi kije mamana......zamu qarasa maganan". Gyada kai falaak tayi,sannan cikin girmamawa ta rusuna
"A fito lafiya" Tace da sultane da kuma haisam da hankalinsa yayi nisa wajen bin CCTV camera din dake sassansa wanda yayi linking nata da wayar hannunsa. Wani motsi yake gani very suspicious ta daukan da yaja hankalinsa sosai.
Numfashi ta sauke me nauyi,me yasa sultane ya gaza fahimtarta?,ba falaak take buqatar ya sallama ba......ba falaak take nufi ta matsa daga gurin ba,shine bata son gani a tsakaninsu.......shine bata qaunar wanzuwarsa a gurin.....tanason lokutan babanta ita kadai ne,tanaso ta kebe da mahaifinta ita kadai ba tare dashi a gurin ba. Tana ganin ya cancanci ya sallameshi......ya kamata ya fahimci akwai SIRRI cikin rayuwarta da wani bare bai kamata yaji ba.......magana ce data shafi rayuwarta da sirrinta,BATA SHAFI WANNAN SHEIKH DIN BA DAN GIRMAN KAI irin girman kan da take ganin yana batawa kansa lokaci ne.....irin girman kan da take gani bai kamata ya dorawa kansa shi ba a matsayinsa na ba kowan kowa ba,a matsayinsa na wanda baisan komai ba,baisan me rayuwa ke ciki ba. Tayi imanin koda cikin gida koda cikin fada tace zata zagaya dashi wasu guraren sai qauyancinsa da rashin wayewarsa sun bayyana muraran.
Shurun da tayi batace komai ba ya sanya sultane dauke dubansa a kanta,ba tare daya buqaci tayi magana ba ya aza kan haisam.
"Umra nake buqatar zuwa d'ana.......wannan lokacin na dauki lokaci me tsaho banje ba,ina buqatar zuwa gurinnan" Sultane ya fadi yana duban haisam.
Daidai sanda ya gama gane gilmawar wanda ya gani,ya kuma tsaida daukan a daidai inuwarsa,ya daga manyan fararen idanunsa yana duban sultane cikin girmamawa. Kai ya jinjinawa sultane din,ya sani koda sultane bai fadi ba,sultane din yana buqatar yawan zuwa gurin don ajiye buqatunsa.......ya kuma yarda ya aminta shi din me yawan zuwa gurinne......wataqila shi yasa gagarumar gobarar dake ci cikin gidansa ta qarqashin qasa ubangiji ya hanata tayi tasirin da zata qona gidan qurmus ta kuma hadiye hardashi.
Masarautar qunshe take da manyan al'amuran da idanun sultane basa iya gani.......tana dauke da manyan sirrika da manyan qullikan da haisam yakeji a jikinsa sun haura wadanda idanunsa suke gani. Inda shigowa rayuwarsu shine manufarsa.......inda ace shigowa rayuwarsu shine abinda target dinsa da farko,ya tabbatar akwai sirrikan da zai tonasu masu azaban doyi da rashin kyan gani. To amma tashi masarautar itace a gaba........tasa masarautar itace ta fiddoshi daga ainihin nashi izzar nashi sarautar da nashi qafin ikon dana mulki,ta maidashi wani malami dake zaune qasan alfarmar wasu cikin yanayi na karantarwa kadai.
"Idan zai yuwu wannan karon inaso mu tafi tare,don inaso nayi kalan umrar da ban taba yi ba tare dakai d'ana,inason sanin gurare masu muhimmanci da zan gudanar da addu'o'in dake tari tari a zuciyata,ban sani ba ko zuwan qarshe zanyi,qila shi yasa Allah ya jefoka cikin rayuwata". Sultane ya fadi still murmushin nan baibar saman fuskarsa ba.
Wani irin abune ya harba cikin qirjinta tana jin iskar da take shaqa wadda tun dazu ke gauraye da turarensa tana matse mata. Tun daga ranar data mallaki hankalin kanta itace take riga kowa sanin plan din sultane,tun daga sanda tasan meye ma'anar umara da aikin hajji ita sultane yake fara gayawa Lokacin da yakeson zuwa,su zauna kuma su tsara lokacin tafiyar.......ta dauki hutu daga company ta rakashi suje su dawo........yau duka wannan malamin ya samu nasarar ture dukka wadannan muqamai nata da sauri haka?.......anya baiyi amfani da asirin da taji da yawansu suna dashi ba wajen mallakar sarakuna ko juya akalar tunaninsu ba?. Dole ta zame cikin dabara ta zauna sosai,tana ji har cikin jininta yadda yau sultane ya maidata wata baquwa daban a gabansa,ya jawo bare......wanda babu dangin iya ko na baba a tsakaninsu yake fadimasa abinda ita ya kamata ita ya cancanta ta fara ji daga bakinsa. Baima maida hankali ga batun da tazo dashi ba......hankalinsa dukka yana kai wannan malamin da ayanzu jikinta ya fara bata akwai abinda ya yiwa sultane na janye hankali.
"Na tsaneka......na tsaneka,tabbas saina nisantaka da mahafina......mahaifina nawa ne ni kadai.....sirrakansa da komai nasa......nan din layikana ne da babu me tsallakeminsu na zuba masa ido" Tayi maganganun qasan ranta tana hadiyar yawu da qyar saboda wani abu daya tsaye mata a wuya.
Sallamarta da muryarta data fita fes da wani irin confidence shine abinda ya dakatar da maganan da sultane yayi niyyar fada ya waiwaya yana amsa sallamar tata,kamar yadda haisam da bai waiwaya ba ko motsawa daga zamansa ba ya motsa labbansa yana amsa sallamar muryarsa can qasa da sautin da bazaka jishi ba.
Shine mutum na farko da idanunta suka fara sauka a kansa,ta zube idanunta fes a kansa,zuciyarta na wani irin motsawa. Tana jin inama zata ita sanin zahirinsa da badininsa da iya kallonsa kawai da takeyi a yanzu?.
"KUSANCI" Abinda zuciyarta ta fara ayyana mata a kanshi kenan,tana qoqarin sarrafa kalmar ya daga fararen idanunsa a nutse,abinda ya harba wani irin faduwar gaba a sassan zuciyarta ya sanya janye idanunta da sauri a kansa,saidai hakan bai hanashi fahimtar kallon qurillar data zube masa ba wanda tuni ya jishi a jikinsa tun daga shigowarta gurin.
"Zan iya tafiya idan hakan ya zamana ba damuwa a tattare da sultane?" Haisam din ya fadi qasa qasa cikin girmamawa. Kai sultane ya girgiza yana murmushi.
"Akwai sauran maganganun da bamu kammala ba ai,baka gayamin yuwuwar tafiyar tamu ba ko dagata zuwa wani lokaci?". Sultane yayi.maganan daidai qarasowar mammina. Sake dauke idonta tayi daga kansa daga kallon qurillar data sake shiga a kansa akaro na biyu.
Zamewa tayi cikin tsananin biyayyar nan da ba abinda ya sauyata tun daga wadancan shekarun xuwa yanzu ta soma gaidashi da salon gaisuwar da koda cikin bacci yake yasan ZAITUNA CE. Ta laqanci wani irin tarin girmamawa da sirrikan sake lulawa cikin zuciyarsa da samum matuqar girmamawa fiye da kowanne dan adam,saidai har yanzu wannan abun ya gaza canza MATSAYIN SAFEENA a rayuwarsa,abu daya daya fahimci mammina ta jima tana son samu kenan MATSAYIN SAFEENA daga bisani kuma ya karanci ta watsar da wannan ta shiga fafutukar gina nata matsayin,wanda ya ginu din kuwa da wani irin girma da kima.
"Daya biyu uku hudu" Can qasan zuciyarsa yake lissafa adadin tsahonta sanda ta miqe daga gaban sultane tana laluben muhallin daya dace da zamanta,gurbin da zai bata daman ganin komai daidai da lissafi da hasashenta. Da wani irin yanayi yake iya hangenta,wanda zaka rantse da Allah bai damu da kowa ba sai wayarsa dake hannunsa,saidai bayan ta gaba idanunsa ta gefen hagu da dama na idanunsa ya samu wani irin horo da yake iya monitoring motsi da reaction na komai da kowa.
Tsaf lissafinsa ya tuqe ga adadin tsahon mace ta biyu cif da cif.....daidai sanda take zama saman kujerar cikin wata nau'in izza dake cakude da taqama idanunta a kansa tana fadada fara'arta da zummar fara dasa harsashin farko a kansa na fara bashi kulawa ta musamman don shiga cikin komarta cikin sauqi.
Da rusunannun idanunta ta qaraso tana yiwa kanta muhallin zama daura da falaak. Numfashinta take qoqarin daidaituwa,tana jin yadda dakin gaba daya ya gauraye da wannan qamshin dai. Wannan qamshin da har yanzu ta rasa makamancinsa......qamshin nan daya zame mata tamkar jarrabi tun daga hippodrome kawo yau......qamshin da har yanzu ta rasa waye ainihin mamallakinsa?......wanne irin turare ne wannan me kassara gabobi?.
"Barka da safiya yaa biftu" Falaak ta gaidata cikin girmamawa qauna da kulawa irin ta 'yan uwantaka. Motsa labbanta tayi da qyar tana maidawa falaak.
"Barkanki.......barka da safiya bappi" Ta furta tana rusunar da idanunta da kanta don nuna girmamawa ga sultane din.
"Barkanki kadai khadeejatu". Ya kirata da asalin sunanta,sunan da ya sauka sosai saman zuciyar haisam ya kuma maimaitashi cikin qirjinsa har sau biyu
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 26*
Sunan wani suna ne da yake da tarin daraja martaba da kima a idanunsa,sunan NANAY dinsa......halittar 'ya mace ta farko daya soma so da qauna a rayuwarsa,yake kuma qauna har yanzu,yake martaba dukkan wanda yake da irin sunan bama ita kanta din ba.
Dauke idanunsa sultane yayi daga kan akhnan din data koma wani cool,yana karantar duk wani yanayi nata da motsinta,yana kuma ankare da yadda bata gaida haisam din.
"To kaji muhammad......ita kuma qanwar naka canjin course din da takeso tayi kenan" Sultane ya fada da murmushi saman fuskarsa yana duban haisam cikin tarin kulawa da kuma kwadayin shigar haisam din kowanne al'amari daya shafi iyalinsa. Ya fuskanci har yanzu haisam din bai shiga lamarin iyalinsa da zurfi yadda yakeso ya shiga ba. Yanaso ya saje dasu ya dinke dasu sosai,ya zama ba wani banbamci ko kadan a tsakaninsu.
Wani miskilin murmushi daya kashe zuciyar falaak ya kuma sanya gabanta tsananta faduwa ya saki,ya tashi ya gyara zamansa sosai yana duban sultane.
"Ana iya bata dama a ganina.......abinda ta buqata bai sabawa ra'ayinka da burinka ba......bai kuma sabawa addini da al'adarta......ubangiji zai sanya albarka sosai a ciki".
"Gaskiya ne" Sultane ya fadi cikin tsananin gamsuwa yana gyada kanshi. Daga qasan ransa yana jin kamar akwai wani saqo da yakeson isarwa ne me matuqar muhimmanci.
Iska ta zuqa sosai cikin kiyayewa da fitar numfashinta,ta qanqance idanunta kadan tana jin saukar maganarsa cikin tsakiyar zuciyarta,tana jin maganarsa kai tsaye tana tunkarota da wani irin yanayi me qarfin gaske. A hankali zuciyarta ta fara maimaita mata DAKE YAKE,maganan ta soma takura zuciyarta tana son tilasta mata jin muzanci,muzancin da alfaharinta da izzarta suka hana ya mamayeta.
"Zan baka mamaki......zan kuma kunyataka gaban sultane tabbas.......sai sultane yasan kaine namiji na farko daka fara hada jiki da diyar da yafi qauna duk duniya har sau uku!" Ta dire alwashin cikin zuciyarta tana jin qwarin gwiwar kiran sunan sultane din.
"Bappi......" Ta kirashi tana sunkuyar da kanta
"Khadeejatu" Ya amsa mata kai tsaye.
"Zan iya samun mintuna biyar?". Idanu sultane ya dan zuba mata sannan ya waiwaya ga falaak.
"Tashi kije mamana......zamu qarasa maganan". Gyada kai falaak tayi,sannan cikin girmamawa ta rusuna
"A fito lafiya" Tace da sultane da kuma haisam da hankalinsa yayi nisa wajen bin CCTV camera din dake sassansa wanda yayi linking nata da wayar hannunsa. Wani motsi yake gani very suspicious ta daukan da yaja hankalinsa sosai.
Numfashi ta sauke me nauyi,me yasa sultane ya gaza fahimtarta?,ba falaak take buqatar ya sallama ba......ba falaak take nufi ta matsa daga gurin ba,shine bata son gani a tsakaninsu.......shine bata qaunar wanzuwarsa a gurin.....tanason lokutan babanta ita kadai ne,tanaso ta kebe da mahaifinta ita kadai ba tare dashi a gurin ba. Tana ganin ya cancanci ya sallameshi......ya kamata ya fahimci akwai SIRRI cikin rayuwarta da wani bare bai kamata yaji ba.......magana ce data shafi rayuwarta da sirrinta,BATA SHAFI WANNAN SHEIKH DIN BA DAN GIRMAN KAI irin girman kan da take ganin yana batawa kansa lokaci ne.....irin girman kan da take gani bai kamata ya dorawa kansa shi ba a matsayinsa na ba kowan kowa ba,a matsayinsa na wanda baisan komai ba,baisan me rayuwa ke ciki ba. Tayi imanin koda cikin gida koda cikin fada tace zata zagaya dashi wasu guraren sai qauyancinsa da rashin wayewarsa sun bayyana muraran.
Shurun da tayi batace komai ba ya sanya sultane dauke dubansa a kanta,ba tare daya buqaci tayi magana ba ya aza kan haisam.
"Umra nake buqatar zuwa d'ana.......wannan lokacin na dauki lokaci me tsaho banje ba,ina buqatar zuwa gurinnan" Sultane ya fadi yana duban haisam.
Daidai sanda ya gama gane gilmawar wanda ya gani,ya kuma tsaida daukan a daidai inuwarsa,ya daga manyan fararen idanunsa yana duban sultane cikin girmamawa. Kai ya jinjinawa sultane din,ya sani koda sultane bai fadi ba,sultane din yana buqatar yawan zuwa gurin don ajiye buqatunsa.......ya kuma yarda ya aminta shi din me yawan zuwa gurinne......wataqila shi yasa gagarumar gobarar dake ci cikin gidansa ta qarqashin qasa ubangiji ya hanata tayi tasirin da zata qona gidan qurmus ta kuma hadiye hardashi.
Masarautar qunshe take da manyan al'amuran da idanun sultane basa iya gani.......tana dauke da manyan sirrika da manyan qullikan da haisam yakeji a jikinsa sun haura wadanda idanunsa suke gani. Inda shigowa rayuwarsu shine manufarsa.......inda ace shigowa rayuwarsu shine abinda target dinsa da farko,ya tabbatar akwai sirrikan da zai tonasu masu azaban doyi da rashin kyan gani. To amma tashi masarautar itace a gaba........tasa masarautar itace ta fiddoshi daga ainihin nashi izzar nashi sarautar da nashi qafin ikon dana mulki,ta maidashi wani malami dake zaune qasan alfarmar wasu cikin yanayi na karantarwa kadai.
"Idan zai yuwu wannan karon inaso mu tafi tare,don inaso nayi kalan umrar da ban taba yi ba tare dakai d'ana,inason sanin gurare masu muhimmanci da zan gudanar da addu'o'in dake tari tari a zuciyata,ban sani ba ko zuwan qarshe zanyi,qila shi yasa Allah ya jefoka cikin rayuwata". Sultane ya fadi still murmushin nan baibar saman fuskarsa ba.
Wani irin abune ya harba cikin qirjinta tana jin iskar da take shaqa wadda tun dazu ke gauraye da turarensa tana matse mata. Tun daga ranar data mallaki hankalin kanta itace take riga kowa sanin plan din sultane,tun daga sanda tasan meye ma'anar umara da aikin hajji ita sultane yake fara gayawa Lokacin da yakeson zuwa,su zauna kuma su tsara lokacin tafiyar.......ta dauki hutu daga company ta rakashi suje su dawo........yau duka wannan malamin ya samu nasarar ture dukka wadannan muqamai nata da sauri haka?.......anya baiyi amfani da asirin da taji da yawansu suna dashi ba wajen mallakar sarakuna ko juya akalar tunaninsu ba?. Dole ta zame cikin dabara ta zauna sosai,tana ji har cikin jininta yadda yau sultane ya maidata wata baquwa daban a gabansa,ya jawo bare......wanda babu dangin iya ko na baba a tsakaninsu yake fadimasa abinda ita ya kamata ita ya cancanta ta fara ji daga bakinsa. Baima maida hankali ga batun da tazo dashi ba......hankalinsa dukka yana kai wannan malamin da ayanzu jikinta ya fara bata akwai abinda ya yiwa sultane na janye hankali.
"Na tsaneka......na tsaneka,tabbas saina nisantaka da mahafina......mahaifina nawa ne ni kadai.....sirrakansa da komai nasa......nan din layikana ne da babu me tsallakeminsu na zuba masa ido" Tayi maganganun qasan ranta tana hadiyar yawu da qyar saboda wani abu daya tsaye mata a wuya.
Sallamarta da muryarta data fita fes da wani irin confidence shine abinda ya dakatar da maganan da sultane yayi niyyar fada ya waiwaya yana amsa sallamar tata,kamar yadda haisam da bai waiwaya ba ko motsawa daga zamansa ba ya motsa labbansa yana amsa sallamar muryarsa can qasa da sautin da bazaka jishi ba.
Shine mutum na farko da idanunta suka fara sauka a kansa,ta zube idanunta fes a kansa,zuciyarta na wani irin motsawa. Tana jin inama zata ita sanin zahirinsa da badininsa da iya kallonsa kawai da takeyi a yanzu?.
"KUSANCI" Abinda zuciyarta ta fara ayyana mata a kanshi kenan,tana qoqarin sarrafa kalmar ya daga fararen idanunsa a nutse,abinda ya harba wani irin faduwar gaba a sassan zuciyarta ya sanya janye idanunta da sauri a kansa,saidai hakan bai hanashi fahimtar kallon qurillar data zube masa ba wanda tuni ya jishi a jikinsa tun daga shigowarta gurin.
"Zan iya tafiya idan hakan ya zamana ba damuwa a tattare da sultane?" Haisam din ya fadi qasa qasa cikin girmamawa. Kai sultane ya girgiza yana murmushi.
"Akwai sauran maganganun da bamu kammala ba ai,baka gayamin yuwuwar tafiyar tamu ba ko dagata zuwa wani lokaci?". Sultane yayi.maganan daidai qarasowar mammina. Sake dauke idonta tayi daga kansa daga kallon qurillar data sake shiga a kansa akaro na biyu.
Zamewa tayi cikin tsananin biyayyar nan da ba abinda ya sauyata tun daga wadancan shekarun xuwa yanzu ta soma gaidashi da salon gaisuwar da koda cikin bacci yake yasan ZAITUNA CE. Ta laqanci wani irin tarin girmamawa da sirrikan sake lulawa cikin zuciyarsa da samum matuqar girmamawa fiye da kowanne dan adam,saidai har yanzu wannan abun ya gaza canza MATSAYIN SAFEENA a rayuwarsa,abu daya daya fahimci mammina ta jima tana son samu kenan MATSAYIN SAFEENA daga bisani kuma ya karanci ta watsar da wannan ta shiga fafutukar gina nata matsayin,wanda ya ginu din kuwa da wani irin girma da kima.
"Daya biyu uku hudu" Can qasan zuciyarsa yake lissafa adadin tsahonta sanda ta miqe daga gaban sultane tana laluben muhallin daya dace da zamanta,gurbin da zai bata daman ganin komai daidai da lissafi da hasashenta. Da wani irin yanayi yake iya hangenta,wanda zaka rantse da Allah bai damu da kowa ba sai wayarsa dake hannunsa,saidai bayan ta gaba idanunsa ta gefen hagu da dama na idanunsa ya samu wani irin horo da yake iya monitoring motsi da reaction na komai da kowa.
Tsaf lissafinsa ya tuqe ga adadin tsahon mace ta biyu cif da cif.....daidai sanda take zama saman kujerar cikin wata nau'in izza dake cakude da taqama idanunta a kansa tana fadada fara'arta da zummar fara dasa harsashin farko a kansa na fara bashi kulawa ta musamman don shiga cikin komarta cikin sauqi.