← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 101

Sashe 18

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sultane ne kawai ya gilma cikin tunaninsa da idanunsa......yana ji da dukkanin yaqininsa akwai wani abu da ba daidai ba......amma kuma yana gayawa zuciyarsa da kansa cewa ba huruminsa bane......BINCIKE YA KAWOSHU AGADEZ.....aiki yazo yi kawai ya koma,aikin da yake sanya rai yake kuma jin cewa kwanakinsa qalilan suka rage. Ya rage baccinsa......ya hana kansa jin dadi walwala da tafiye tafiyen da yakanyi don kawai sake gane girman buwayar Allah saboda aikin kadai. Ya kasa samun nutsuwa na tsahon shekaru....baccinsa yakan yanke idan ya tuna koda kowanne lokaci rayuwar MOTII zata iya fuskantar barazana.

Barazanar dake gabansa.......aikin dake gabansa yafi gaban wannan abun da yake gani a yanzu.....bayajin kuma yana da sauran abunyi akai.....abu daya ne yasa hankalinsa yake kaiwa gurin,jikinsa yana bashi matar itace zata zame musu tsani na samun wani abu ko yaya ne game da AJANI AHMED.

Sauka ruwan yake da wani irin yanayi daya tayar da qamshin qasa. Sassanyar iska dake kadawa da walqiya me tsananin haske tsakanin zubar ruwan da iskar. A haka yake takawa cikin cikakkiyar nutsuwarsa,kamar ba ruwan sama ke sauka saman kanshi ba. Abu daya kawai yayi.......zare kewayayyar hular dake saman kansa,ya riqeta a hannunsa,wannan ya bawa ruwan damar sake kwantar da sumar dake kansa me yawa da kuma sulbi.

Ruwan farko kenan da ake sanya ran ya kasance tafe da tarin albarka,yaci gaba da takawa yana furta ALLAHUMMA SAYYIBAN NAFI'AN da kyawawan jajayen labbansa masu sulbi.

Yanayin ya tuna masa ne da jimma........tana da wani irin dadi a yanayin damina irin haka. Kyawawan shukoki da tsirrai,guraren da zaka kebe kanka cikin nutsuwa wanda yake sanyashi nishadi a yawancin lokuta. Akwai guraren na musamman daya warewa kansa cikin masarauta,wanda shi daya yake rayuwa ya kuma kebe kansa a gurin idan yaso. Gurine da ba kowa ma ya taba samun daman shigarsa ba cikin masarautar.

Bai manta randa omar ya taba samunsa a daya daga cikin gurin. Sosai ya daga kai yana shaqar iskar me dadin dake kadawa a gurin,wani irin tattausan qamshi daya wanzu a gurin sakamakon yawaitar kyawawan furanni.

"Gurin nan sam bai dace dakai ba......gurin nan yafi kyau da zaman masoya......ko ma'aurata.....za'a mori soyayya sosai ta gurin nan" Ya fada da dukkan gaskiyarshi. A sannan harara ya watsawa omar,yana ganin damuwarsu kawai dukka bata wuce soyayya?,amma sannu a hankali sai tunanin ya fara zauna masa.....dole ya janye shiga gurin gudun faruwar karkatar hankalinsa daga mission dinsa zuwa wani tsari da bai shirya masa ba a sannan.

_AKHNAN_

Duk da warwarar matsalar tazo mata da wani gundumemen sharadin da bata taba tsammanin zai gindaya cikin rayuwarta ba,amma hakan bai hanata jin sassauci a zuciyarta ba yayin da take takawa zuwa hanyar da zata sadata da sassanta. Ba wani tsoro yau tattare da ita saboda tare da birra suke takawa zuwa sassan nata,duk da tsoron ruwan sama sa take dashi wanda ya samo asali tun daga yarinta. Kamar yadda bataso ya daketa ba tare da wani qwaqqwaran dalili ba......tun zazzabi daya taba saka mata sau daya......hakanan bata son saukarsa saboda tsananin tsoron tsawa da take dashi,amma a yau din yadda zuciyarta ta fara taurarewa da yanayin dake fuskantota,sai ta baiwa ruwan daman sauka a kanta haka kai tsaye,saidai yadda taga yana qara yawa ya sanya tadan qara saurin tafiyarta,tana kuma dakatar da birra dake qoqarin lulluba mata wata qaramar lema.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Hannu kawai ta miqa mata ta karbi sabon cherry din da aka ciro mata,wanda ya zame mata al'ada shan fruit kowanne dare bawai abinci ba.

"Zan kwanta da wuri idan na shiga......kina iya tafiya" Ta sallameta don tasan akwai buhaina da bushira da yau zasu kasance a sassannata. Birran na qoqarin mata bayanin basa kusa a yau din amma tuni tayi gaba zuwa sassan nata.

Ruwan na sauka da wani irin nau'in sanyi,sanyin daya ratsa fata da tsokarta,ya kuma taba zuciyarta a hankali kuma yana sauke mata maganan da suka soma yi dazu da safe da tamim.

"Kiyimin afuwa.....na gaza gano komai a kansa.....dukka iya bincike na,saidai ban dawo haka a banza ba,na samo launin fatarsa......qwayar idanunsa.......da tsahonsa.....launin gashinsa......sannan an bani tabbacin dan qasar Ethiopia ne yankin jimma......" Yayi maganan yana buda mata envelope din dake qunshe da komai a ciki.

Tsarin zubin halittarsa dake rubuce daki daki ta dinga kalla. Giant ne........launin fatarsa bata cika haske da yawa ba,saidai sam ba baqi bane.......idanunsa na da nau'in shape din almond......farin me haske sosai,baqinciki me duhu......fadin qirjinsa dana kafadunsa duka yana nuna halittar namijin daya kasance giant sosai.....me qirar qarfi kamar yadda ta shaida hakan daga riqon da yayi mata. Ta maida komai ta rufe tana kwantantawa da mutumin dake a mazaunin malami me karantaswa cikin masarautar mahaifinta. Akwai tarin kamaceceniya sosai a wadannan bayanan da abinda take iya gani tattare dashi......saidai har yanzu wadannan bayanan basu bata cikakkiyar gamsuwa da hujja me qarfi ba......amma ta rasa abinda yasa zuciyarta dari bisa dari taqi aminta da cewa bashi bane. Duk bata hangen wani qwarewa ko sanin rayuwa ga malamin addini da har zaisan yadda ake sarrafa doki haka da tarin hikima da kuma ilimin sanin sarrafa dabbobi,ta tabbatar ko waye zai aikata hakan dole akwai wani D'IGO na SARAUTA cikin jininsa.....koda ba ahalinta bane amma tabbas yana da alaqa da ita komai qanqantarsa.

Takan bata lokuta masu yawa tana nazarin......indai har shine yanzu c

Kai tsaye ta durfafi qofar sassan nata,saidai kuma ta samu a rufe take,da alama kuma me kula da wajen baya kusa. Sai a sannan ta tuna kusan ta sallami kowa sanda zata fita din. Tana da wani hali me kyau guda daya,a duk sanda bata buqatar komai takan sallami hadimanta na kusa dana nesa don suje su kwanta suma su huta,ba kasafai take barin kowa yayita tsaiwa akan hidimarta awa ashirin da hudu ba.

Wani siririn tsaki taja,gabanta yana wani irin faduwa saboda yadda rugugin hadari ya fara tasowa,wanda ta tabbatar zai wahala yazo ya wuce walqiya bata biyo baya ba.

Tsaiwan zai zama bata lokacine a wajenta,sai ta yanke bi ta qofa ta biyu ta sassanta dake dogon balcony din daya hada sashenta da sashen dake maqotaka da nata. Guri ne da takan dauki kwanaki bata bishi ba,musamman da yake ma ba mazauniyar agadez bace......saidai kuma idan tana buqatar kadaici,ko bata buqatar kowa ya ganta takan bi ta nan ta fice abinta zuwa dukka sassan da takeso.

*HAISAM*

Tun sanda ya fito da niyyar komawa ta qofar bayan ya fito. Tun sanda ya gama karantar duk wani lungu da saqo na sassan da kewayensa yasan da qofar,amma bai taba bi ta nan ba. Ba komai yake motsi ko wani action a kansa ba.....bayason yawaitar motsinsa akan abubuwa da yawa su jawo hankulan jama'a a kansa.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 17*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
_____________________________

Akwai abubuwan da yasan dasu,amma yayi kamar baisan da wanzuwarsu ba.....akwai abubuwan da ya sansu amma yanayi kamar baisan komai akai ba ko bai fahimta ba. Yau din ya shirya bi ta nan ne don yasan inane mahadar da ta hada nan shiyyar da kuma sashen da qofar ke a ajiye.

Har cikin jikinsa yau din yakejin sanyi da saukar ruwan. Yanason damina sosai,yana cikin sahun yanayiyyikan da yafi so a dukka wasu yanayi da muke dashi cikin rayuwarmu,saidai kuma damina da sanyi sukan zama wani yanayi dake farautar nutsuwar gangar jikinsa gaba daya. Suna sauke masa wani irin feeling me matuqar nauyin gaske,don haka sau tari killace kansa yakan qara yawa ne a duk sanda aka samu mamakon ruwan saman daya sanyaya gari....ko kuma yawaitar sanyi sosai cikin dare zuwa safiya.

Dukkaninsu da sassarfa suke tako stairs din dake kallon juna,wanda zata sadaka da gajeriyar veranda data hade fuskokin balcony dinsu da zai sada kowanne da ainihin sassansa ta baya. Yadda bata kula da shi ba tana kokawa da dankwalinta da ya nace saiya sauka daga kanta saboda santsin jiqaqqen gashinta.......daya hannun kuma tana rungume da Cherry's dinta da mistake kadan zatayi su zube......idan kuwa har suka zube ta tabbatar zai zama ba rabonta bane,don ba komai yake taba qasa ba tacishi ba,dare kuma yayi da ba yadda za'a sake shiga garden din a debo mata wani.

Saidai duk da yadda takai ga takatsantsan da sauri idanunta sun rufe,kuma cike suke da tsoron da har ta iso dab dashi a sanda hankalinsa shima ke kan keys din hannunsa yana duba wanda yake na qofar.

Bangazar juna sukayi,kuma a take cherry din da yake tattali ya watse daya daya a gurin.

"Subhanallah" Ya furta da deep voice dinnan nasa dake cike da sound na nutsuwa a cikinta yana yin taku biyu baya,kamar yadda itama taja baya da sauri cikin matsanancin tsoro,bugun zuciyarta ya sake ninkuwa ta ware manyan idanunta sosai a cikin sassauqan hasken da bame yawa ba,tana jin wani irin yanayi yana shigarta a hankali saboda shaqar wannan qamshin da tayi. Wannan qamshin dai da har yanzu ta gaza gane waye ainihin mamallakinsa?.....wannan malamin dake a gabanta yanzu?......ko abokin tserenta ne daga hippodrome?. Wannan qamshin dai daya tsaye mata a kwanya......ya yiwa kansa kyakkyawan gurin zama tsakanin tunaninta zuciyarta dama kafofin hancinta.

Dukka idanunta ta ware ta zuba masa,duk da cewa bata iya ganinsa tarwai,amma tana iya ganin yadda sumarsa me santsi ta kwanta sosai har saman goshinsa ta kuma sauka sosai a qeyarsa.
Chapter 18 · 0% Book details