← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 101

Sashe 11

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Daukar fansa yafi ciwo a sanda aka manta......yafi ciwo a sanda aka saki jiki.....yafi ciwo a sanda zamani da shekaru suka cilla......a sanda akayi imanin komai bazai canza ba......komai bazai kuma faru ba" Ta yadda da wannan magana ta zuciyarta.......kuma itace take mata jagoranci a dukka tsahon shekarun nan kawo yanzu. Safeena zallar muguwa ce.....muguwar da bata da kamanceceniya,salon muguntar da batajin idan zata dawo duniya ta mutu sau dubu hakan zai sassauta abinda takeji a kanta kota yafe mata,a sanda ta tabbatar rabuwa tazo tsakaninta da sultane......a sannan ma bata barta ba,bata bar sultane ba,saida tayi abinda ya sake jawo mata asarar matsayinta,ya kuma kusa sake jawo mata rasa sultane din rashi na har abada,ta yaya zata manta da dukka wadannan abubuwa?,ta yaya zata yafe cikin sauqi?,don dai ita ta kawo wawanci duniya?.

Yadda taga akhnan na kallonta ya sanyata sakin sassanyan murmushi

"Ina tunanin irin halin da zan shiga yanzu iwarhaka inda na rasaki......biftu......kina taba tunanin inda muradinki ya cika masarautar agadez gawa biyu zasu sallata?" Kai ta kada tana duban mammina. Batasan me yasa a wannan lokacin mammina ta gaza yarda ba ita ta aikatawa kanta haka ba?.

Ta lura da irin kallon da akhnan din ke mata,don haka ta nuna gefanta dab da ita.

"Zauna a nan" Bata musanta ba ta zauna din,mammina ta zuba mata ido tana tattara nutsuwarta a kanta.

"Munci sa'a,munci kuma nasara.......sultane ya janye maganan hakeem a kanki......labarin abinda ya faru ya isa kunnensu,don haka sun janye,nasara taki ce". Manyan idanun nan da sukan rusuna wani lokaci kamar name jin bacci ta ware gaba daya. Labarin yazo mata a bazatar da bata taba kawota nan kusa ba,ta rasa me zata yiwa mammina?,kawai saita shige jikinta gaba daya tana mata wani wawar runguma.

Wacce irin qauna ce haka mammina ke mata?,anya yadda mammina ke sonta ko mahaifiyarta idan ta dawo duniya zata qaunaceta irin haka kuwa?.

"Bansan me zance miki ba,bansan wanne kalar godiya zanyi miki ba" Akhnan ta fada idanunta suna cika da hawaye,tana jin kamar an warware mata wani qaton dauri da aka yiwa rayuwarta gaba daya.

Rungumar data matan tana mata kamanceceniya da sanya buhun qarfe na wuta a jikinta,amma hakan bai hanata shafa bayan akhnan din ba,kafin ta janyeta a jikinta a nutse da tausasawa tana cewa.

"Da abu guda daya tal zaki biyani". Tsaida idanunta akhnan tayi kan fuskar mammina tana kallonta.

"Sultane yayi rantsuwa ba abinda zai fasa ko ya hana daura miki aure nan da watanni biyu masu zuwa.......amma da zabin kanki da zaki kawo........saboda haka karki bani kunya......yadda na tsaya akan al'amarin nan har aka fasashi......inaso ke kuma cikin qasa da wata biyun ki fidda miji ki kaiwa sultane kaman yadda ya buqata". Idanunta ta sake warewa a karo na biyu tana duban mammina a hargitse.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/5, 19:10] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 11*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________

Bata ko tsaya neman flip-flops dinta ba ta soma taka tattausan tafin qafanta kan carpet din tana qoqarin cusa gashinta me tsaho da sulbi cikin bonnet da take mahadin kayan jikinta.

Yadda take saukowa daga stairs din a gaggauce ya sake sanya mammina cilla plan dinta da qara masa wani adadi.

Ido ta lumshe tana sake budesu akan akhnan din,wani irin kishi yana ci mata zuciya. Har tana jin kamar wani ciwo ciwo na dunqulewar da zuciyarta tayi guri daya.

Wani irin sassanyan kyau yarinyar ke dashi,kyan data tabbata banda wasu dalilai ba abinda zai sanya akhnan ta rufa shekaru goma ba tare da an aureta ba zuwa ga ahali mafi daraja da sukafi na mahaifinta. Ita kanta akhnan tana mata kyau,saidai kyan yana tsaye mata a rai da wani irin ciwo saboda tuna daga inda ta samo ASALIN KYAN nata. Daga gurin safeena ne......wannan kyan nata da tayi imani yana daya daga cikin abinda ya sanya ta rasa wannan martabar.......ta rasa wannan darajar.......ta kuma rasa wannan MATSAYIN da TAMBARIN na MATAR FARI a gurin sultane.

Bayan kyan ya mata wannan sanadin......wannan KYAN HALIN da a wajenta ba komai bane face zallar kissa da kisisina ya sake zame mata silar qara rasashi a KARO NA BIYU,ya sake cillata can nesa da matsayin zamowa MATA TA BIYU ga sultane din.

Ware idanunta tayi akan akhnan sanda take kusa isowa da inda take. Tuna baya kadan da tayi ya sake rura wata sabuwar wutar a zuciyarta. Ta zubawa akhnan idanu,tana tuna fuskar safeena da wani lokaci zaka ganta shimfide akan fuskar akhnan din.

Sau da dama tana mamakin kanta na yadda ta tsaya bin akhnan ta wannan doguwar hanyar. Tana ganin imaninta da yawa idan ta tuna shekarun data dauka kawai tana dakon ta dauki FANSA akan abinda tana iya aiwatar dashi cikin kwana uku kacal. To amma zuciyarta tasha gaya mata cewa.

"Daukar fansa yafi ciwo a sanda aka manta......yafi ciwo a sanda aka saki jiki.....yafi ciwo a sanda zamani da shekaru suka cilla......a sanda akayi imanin komai bazai canza ba......komai bazai kuma faru ba" Ta yadda da wannan magana ta zuciyarta.......kuma itace take mata jagoranci a dukka tsahon shekarun nan kawo yanzu. Safeena zallar muguwa ce.....muguwar da bata da kamanceceniya,salon muguntar da batajin idan zata dawo duniya ta mutu sau dubu hakan zai sassauta abinda takeji a kanta kota yafe mata,a sanda ta tabbatar rabuwa tazo tsakaninta da sultane......a sannan ma bata barta ba,bata bar sultane ba,saida tayi abinda ya sake jawo mata asarar matsayinta,ya kuma kusa sake jawo mata rasa sultane din rashi na har abada,ta yaya zata manta da dukka wadannan abubuwa?,ta yaya zata yafe cikin sauqi?,don dai ita ta kawo wawanci duniya?.

Yadda taga akhnan na kallonta ya sanyata sakin sassanyan murmushi

"Ina tunanin irin halin da zan shiga yanzu iwarhaka inda na rasaki......biftu......kina taba tunanin inda muradinki ya cika masarautar agadez gawa biyu zasu sallata?" Kai ta kada tana duban mammina. Batasan me yasa a wannan lokacin mammina ta gaza yarda ba ita ta aikatawa kanta haka ba?.

Ta lura da irin kallon da akhnan din ke mata,don haka ta nuna gefanta dab da ita.

"Zauna a nan" Bata musanta ba ta zauna din,mammina ta zuba mata ido tana tattara nutsuwarta a kanta.

"Munci sa'a,munci kuma nasara.......sultane ya janye maganan hakeem a kanki......labarin abinda ya faru ya isa kunnensu,don haka sun janye,nasara taki ce". Manyan idanun nan da sukan rusuna wani lokaci kamar name jin bacci ta ware gaba daya. Labarin yazo mata a bazatar da bata taba kawota nan kusa ba,ta rasa me zata yiwa mammina?,kawai saita shige jikinta gaba daya tana mata wani wawar runguma.

Wacce irin qauna ce haka mammina ke mata?,anya yadda mammina ke sonta ko mahaifiyarta idan ta dawo duniya zata qaunaceta irin haka kuwa?.

"Bansan me zance miki ba,bansan wanne kalar godiya zanyi miki ba" Akhnan ta fada idanunta suna cika da hawaye,tana jin kamar an warware mata wani qaton dauri da aka yiwa rayuwarta gaba daya.

Rungumar data matan tana mata kamanceceniya da sanya buhun qarfe na wuta a jikinta,amma hakan bai hanata shafa bayan akhnan din ba,kafin ta janyeta a jikinta a nutse da tausasawa tana cewa.

"Da abu guda daya tal zaki biyani". Tsaida idanunta akhnan tayi kan fuskar mammina tana kallonta.

"Sultane yayi rantsuwa ba abinda zai fasa ko ya hana daura miki aure nan da watanni biyu masu zuwa.......amma da zabin kanki da zaki kawo........saboda haka karki bani kunya......yadda na tsaya akan al'amarin nan har aka fasashi......inaso ke kuma cikin qasa da wata biyun ki fidda miji ki kaiwa sultane kaman yadda ya buqata". Idanunta ta sake warewa a karo na biyu tana duban mammina a hargitse.

Wani sabon tashin hankalin takeji yana saukar mata yana maye gurbin nutsuwa da walwalar data samu na sakannin baya da suka wuce. Wanne irin daurin talala ne wannan?......wanne irin d'aurin goro sultane yake mata?,wanne irin bahagon hukunci ne?,wanda banbamcinsa da hukuncin baya daya janye kadanne?.

"Mammina....." Ta kira sunanta labbanta suna rawa kadan,idanunta a kanta wani kalan tashin hankali yana sauko mata.

Tsareta mammina tayi da idanu.......irin abinda takeson gani shine a kwance saman fuskar akhnan din. Irin yanayin nan take buqatar gani,kuma ta ganshi,wannan shine abinda yake sake tabbatar mata da qarfi da kuma kaifin nasararta.

"....banaso kice komai biftu.....muddin abinda zaki fada din bai dace da hukuncin sultane ba" Ta qarasa maganan tana girgiza mata kai.

Itama kai take girgizawa tana duban mammina din.

"Mammina.....meye bambancin wannan hukuncin da wanda sultane ya janye?,.......ina zan samo miji cikin watanni biyu?.......ya manta wace akhnan?......khadeeja muhammad hammud?......ya manta cewa rayuwar wani d'a namiji bata cancanci ta gauraya da rayuwata ba?.....ya manta cewa ba musaye nakeso ba?......ba dakatarwa kadai nake buqata ba?.......nesantawa nakeso.......ya nesanta rayuwata daga rayuwar kowanne d'a namiji".

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Kai mammina ke girgizawa tana dubanta.

"A yanzu.....a kuma qadamin da sultane yake kai komai zai iya faruwa......wannan ra'ayin naki dole ki saukeshi.......wannan tsarin naki dole ki warwareshi......dole ki fuskanta kibi dukkan abinda yake tsarin sultane.......mun fara kaiwa wata gaba dashi......gab'ar dana fuskanci sai munyi da gaske zamu b'ulle......sai da takatsantsan zamu sha a hannunsa,saboda tunaninsa a yanxu ba nashi bane shi kadai.....ba shi kad'ai yake tunaninsa ba".

"Amma mammina........me yasa?....."

"Ya isa akhnan" Mammina ta furta a hankali tana canza yanayin fuskarta,sai kuma ta miqe tsam tana zame jikinta.
Chapter 11 · 0% Book details