Sashe 41
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Subhanallah". Budesu yayi a hankali hoton yana dawowa cikin idanunsa. Baby face dinnan nata dake cike da wani irin yanayi dake nuna zallar gajiyarta rauninta da kasawarta,saidai alamu na tsananin taurin kai kafiya da kuma qi fadi irin nata yasa takejin ita din tsayya ce da ba rauni ko gajiya a tattare da ita,wanda kai tsaye a kuma kallon farko yake iya hangen dukka wadannan abubuwan a tattare da ita. Abu guda daya da yayi masa tsaye a qirji......yadda take kewaye tsakiyar wata da'ira me fadin gaske.......yadda ake wasa da rayuwarta ake juya wannan kafaffen ra'ayin nata daga hagu zuwa dama ba tare da ita tasan hakan ba.......ba tare data fuskanci hakan ba. A nasa idanun wani abune me sassauqan fahimta da ganewa......to amma ya sani a karan kansa,shi dabanne.....shi kuma na dabanne da yake iya hangen komai daga nesa tarwai kamar yayewar hijabi.
Bayaso ya shiga wasan daba nashi ba......amma tabbas wasan zai bada ma'ana inda ace shine abinda ya shigo dashi agadez.......an taki bahaguwar sa'ar da baya kallon kowanne aiki sai nasa aikin.....wannan ya sanya wasan zai zame masa abun kallo yana daga zaune a inda yake. Yana raina izzarta......yana raina tsaiwarta da kafiyarta.....yana kuma raina mulki da sarautar da takeji tana yawo a jikinta. Ya sake raina jaririyar kwanyarta......data bari ake gara rayuwarta tamkar ball a hannun qananun yara tsakiyar fillin qwallo. Baizi agadez don kowa ba sai don MAI LAIFIN DA SUKE FARAUTA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON QASARSA ETHIOPIA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON MOTII DA NANAY DA AL'UMMARSA......baiga dalilin da zai sauka daga wadannan matakai da tsanin nasa ba.
Saidai duk da haka,duk da tarin wannan raunin......duk da tarin wannan siffofin,yana hangen wani YAQINI da JAJIRCEWA ta cikin dukka motsi da yanayinta. Da gaske ne ita din bata karbar FADUWA da gaske ne TSAYAYYA CE akan dukka quduri da burinta,saidai yanaji a jikinsa da sannu komai zai canza.....da sannu qilan za'a cimmata a rushe komai.....wataqila a sannan ya jima a jimma Ethiopia,har ma ya mance da wata qasa daya taba wanzuwa wato niger.
Kai tsaye suka dinga buda masa hanyoyi har zuwa inda zai riskar mammina. A kowanne taku akwai hadimi guda daya da zai masa jagora zuwa inda take mataki mataki. Tsarin sashenta daban yake,banbamcin da ya bayyana qarara da kowanne sashe na gidan. A zahiri karon farko kenan da ya taba bayyana cikin sassan,saidai a badini kuwa sashen ba baqonsa bane,saidai ya wawantar da kansa yadda ya kamata don yayi kama da mutumin da karon farko daya taba tsintar kansa a gurin.
A kowanne motsi da kuma kowanne taku yana hankalce da yadda ba wata doka data soma aiki a sassan mammina din. Kowanne shiyya na gidan ya samu cikakken rahoton fara wanzuwar dokar da fara aiki da ita,ciki kuwa harda shiyyar sultane duk da bayanan,da sashen morsa safiyya.
Yayi marking hakan da alama ta biyu da zaiyi nazari a kanta,yana sake maida hankalinsa da inda hadimar ke masa iso tana janyewa baya,da alamu iya tata iyakar kenan.
Tun daga nesa kafin ya qaraso ta tattara dukka nutsuwarta,ta kuma bude dukkan basirarta dake mata jagora zuwa fahimtar zurfin tunanin dan adam a sanda taso karantarsa.
"Wa'alaikumussalam......bismillah" Abinda tace da haisam kenan a sanda ya qaraso farfajiyar da take zaune.
A nutse ya taka yana isa gaban wata kujera qwaya daya data fita daban da sauran,yayi bismillah a hankali yana zama,saita daga kanta tana duban yalwa.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/22, 19:59] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 37*
"A marabceshi kamar kowa.....a kuma wadatashi da dukkan abun ci da abun sha" Ta furta da cikakkiyar izzar dake nuna girma da nisan inda ta dauki kanta da kuma kalar matsayin data bashi.
Idanunta ta daga a hankali,tana iya karantar zallar nutsuwar dake kwance saman fuskarsa,ba wani tsoro ko fargabar kasancewarsa a gabanta,duk da yadda takewa tarin mutane kwarjinin da ko cikakken zama a gabanta ba kowa ke iya yinsa. Wani adanannen kwarjini da tasa aka mata tattalinsa daga kowanne jini dake harbawa a jikinta.
"Sheikh haisam.....tuntuni na aika a kiramin kai......ba'a sanar maka bane?" Tayi tambayar da manufa tayin titsiye da kuma son ganin adadin girma da kwarjinin data yiwa idanunsa da zuciyarsa.
Kai ya gyada a nutse bayan ta ajiye tambayarta harma ta huta ta hanyar shaqar sabon numfashi,yana jin kamar nashi jinin OROMIA din yana shirin motsa masa,jinin ABA JIFAR amma yasa wani abu me nauyi ya danneshi yana daidaita yanayinsa da lokacin.
"Eh an sanar dani" Ya amsa mata a taqaice. Yadda ya amsa mata kai tsaye ba wani kwana kwana ko neman boye laifinsa ya tabata sosai,abinda bata taba gani ba,bata kuma saba gani ba,sai ta jinjina kai.
"An sanar dakai.....amma ka bata wasu mintuna da suka kusa tasamma jimillar awa guda cif,na kiraka ka wofantar da kiran?" Ta fadi da zafi zafi wannan karon a muryarta.
Kamar dazun,sai daya shaqi nutsatstsiyar iska sannan ya sake motsa labbansa.
"Akwai banbamci tsakanin wofantarwa da zuwa a makare......ba kowanne kira bane amsashi akan lokacin da aka yishi yake nuna girmamawa ba......manufar daya ce wanda aka kira ya amsa......gani na amsa a lokacin da yafi dacewa......idan kuma ba damuwa,kamar shiga cikin maganar kai tsaye zaifi,saboda mu ceci lokaci ni dake gaba daya" Yayi maganar kansa tsaye yana zube idanunsa cikin nata.
Kafeshi takeso tayi da idanunta,amma ta rasa wannan qwarin gwiwar,saita janye dubanta a kansa,zuciyar taqi yarda da kwarjini yayi mata,saidai tafi alaqanta hakan da fushin da takeji a kansa. Bata jin zata sakar masa wanna gabar da sauri haka ba tare data saukar masa da warning ba saboda gaba
"Cikin masarautar nan.....cikarta da batsewarta.......yana zama wajibi akan dukkan wanda na kirashi ya amsa kirana a sanda na buqata". Kansa ya juya a hankali,ya fahimci maganan rashin xuwa kiranta a sanda taso ta mata zafi sosai,hakan shi kuma yayi masa.
"A tawa al'adar da yaren.....girmamawa sifface ta dattako.....ga duk wanda ya amsa kiranka ya girmama koda baizo a sanda ka buqata ba" Ya amsa mata yana sassauta harshensa. Bayaso nan da nan tayi fusatar da zata rudar da hankalin omari daga fuskantar abinda haisam din yakeso ya fuskanta. Maganar tasa ya daketa ta kuma taso da wani tsohon al'ada da wata tsohuwar karin magana daga asalin nata yaran,ta kuma motsa idanunta kamar zata waiwaya gareshi ta kalleshi don tabbatar da abinda ya fada,amma koda ta tuna da nata mission din saita kauda hakan. Saidai hakan da tayi bai hanashi daukan haske ba.
"Ka zartar da wasu sabbi kuma baqin dokoki ba tare da neman ta bakina ko ganawa dani ba.....shin waye ya baka wannan izinin?". Murmushi ne dan siriri ya qwace masa,saidai ya tsaya iya labbansa,duk da hakan kuma bai hana tsarguwar mammina ba da rayawa a ranta kamar murmushin taga yayi ba,saidai bai bata dukkan dama ta gane hakan ba.
Ya kamata tambayar ta bashi mamaki,amma kuma yadda ya tsammaci tuhume tuhumenta zasu iso haka suka sameshi.
"Ba kowa".
"Ba kowa?" Ta tambaya a mamakance,tana jin ta samu gaba da zata soke kowacce doka hankali kwance.
"Eh.....ba kowa,saidai bayan na gama rubuta dukkan dokokin,na gabatarwa da sultane,inda hankalinki a nutse yake da zaki iya ganin stamp da sanya hannun sultane qasan kowacce doka" Ya fada da wani irin calmness yana sake tattara nazarinsa a kanta.
Wani shocked taji sosai har cikin jininta,jin da sanya hannun sultane aka wanzar da komai,ba tare da kuma sultane ya kirata yaji ta bakinta ba yadda suka saba sanya kowacce sabuwar doka a tare.
"Na tabbatar daukuwa da hankalin sultane yayi ne kan wannan tafiyar ya hanashi nemana......amma hakan bawai yana nufin kana da qarfin ikon zartar da doka kai kadai ba". Kansa ya sake juyawa a hankali,cikin Tarin nutsuwa idanunsa tsakiyar nata yace.
"Sanya hannun sultane ya wadatar........dokar bata an qirqireta bane saboda ke,an qirqireta ne saboda masarauta.....shi yasa ya zamana ba wani laifi don an kafata ko an zartar da ita bada saninki ba.....dukkanin dokar an yita ne saboda tsaron masarauta"
"Tsaro ga masarauta ko kuma neman ikon sarrafa komai da kowa?" Murmushi ya sakeyi kadan,na wannan karon yafi na dazu bayyana.
"Ikon sarrafa komai wannan siffar Allah ce mahalicci shi kadai.....ni dake da sultane duk bamu da hurumi a kanta". Maganar tasa sai taji kaman yana qoqarin tube mata rawanin ikonta ne,don haka cikin qanqance idanu tace masa.
" Kasan wacece ni kuwa?".
"Kowa nasan wayeshi.....kowa kuma nasan wa yake qoqarin zamantowa ko kasancewa kamar shi". Wani irin abu taji ya sauka yana sarar gabban jikinta. Wani irin gumi taji yana qoqarin tsatstsafo mata,saidai tasan barin hakan ya faru,barinsa ya karanci hakan babban kuskure ne a tare da ita,don zuwa yanzu cikin jikinta takejin BA HAKA KAWAI YA SHIGO AGADEZ BA....BA HAKA KAWAI YA SHIGO MASARAUTA BA.....BA GAMA GARIN MALAMI BANE.
"Amma kasan cewa masarautarmu a zaune take lafiya kafin shigowarka cikinta?" Ta sake fadi yanayinta yana nuna fara daukan zafi.
"Zaman lafiya ba shine shuru ba......wani lokaci shuru yana boye abubuwa masu nauyin gaske....cikin rashin sa'a saika dauka lafiya ce ta kurmantar da komai din" Ya amsa mata da wani irin nutsuwa a tattare dashi. A karo na biyu ta sake jin kamar dutse ya dauka ya jefeta dashi cikin tsakiyar kanta.
"Waye shi?" Ta samu kanta da tambayar kanta da kanta,zuciyarta da tunaninta suna neman zamewa. Zuciyarta ke mata wani irin tsalle,tana kuma cikata da shakku a kansa,sannan tana son jefa mata rudanin da bata shirya ko tunanin fuskantarsa ba a daidai lokacin.
"Akwai wani da kake zargi?....ko akwai wani abun zargi cikin masarautar damu muka gaza hangoshi sai kai?". Tayi tambayar cikin zafi,tambayar data sanya ita da kanta wuta dauke mata,don bata tsara ta fidda masa zafinta har haka akan komai ba.
Bayaso ya shiga wasan daba nashi ba......amma tabbas wasan zai bada ma'ana inda ace shine abinda ya shigo dashi agadez.......an taki bahaguwar sa'ar da baya kallon kowanne aiki sai nasa aikin.....wannan ya sanya wasan zai zame masa abun kallo yana daga zaune a inda yake. Yana raina izzarta......yana raina tsaiwarta da kafiyarta.....yana kuma raina mulki da sarautar da takeji tana yawo a jikinta. Ya sake raina jaririyar kwanyarta......data bari ake gara rayuwarta tamkar ball a hannun qananun yara tsakiyar fillin qwallo. Baizi agadez don kowa ba sai don MAI LAIFIN DA SUKE FARAUTA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON QASARSA ETHIOPIA......BAIZO AGADEZ BA SAI DON MOTII DA NANAY DA AL'UMMARSA......baiga dalilin da zai sauka daga wadannan matakai da tsanin nasa ba.
Saidai duk da haka,duk da tarin wannan raunin......duk da tarin wannan siffofin,yana hangen wani YAQINI da JAJIRCEWA ta cikin dukka motsi da yanayinta. Da gaske ne ita din bata karbar FADUWA da gaske ne TSAYAYYA CE akan dukka quduri da burinta,saidai yanaji a jikinsa da sannu komai zai canza.....da sannu qilan za'a cimmata a rushe komai.....wataqila a sannan ya jima a jimma Ethiopia,har ma ya mance da wata qasa daya taba wanzuwa wato niger.
Kai tsaye suka dinga buda masa hanyoyi har zuwa inda zai riskar mammina. A kowanne taku akwai hadimi guda daya da zai masa jagora zuwa inda take mataki mataki. Tsarin sashenta daban yake,banbamcin da ya bayyana qarara da kowanne sashe na gidan. A zahiri karon farko kenan da ya taba bayyana cikin sassan,saidai a badini kuwa sashen ba baqonsa bane,saidai ya wawantar da kansa yadda ya kamata don yayi kama da mutumin da karon farko daya taba tsintar kansa a gurin.
A kowanne motsi da kuma kowanne taku yana hankalce da yadda ba wata doka data soma aiki a sassan mammina din. Kowanne shiyya na gidan ya samu cikakken rahoton fara wanzuwar dokar da fara aiki da ita,ciki kuwa harda shiyyar sultane duk da bayanan,da sashen morsa safiyya.
Yayi marking hakan da alama ta biyu da zaiyi nazari a kanta,yana sake maida hankalinsa da inda hadimar ke masa iso tana janyewa baya,da alamu iya tata iyakar kenan.
Tun daga nesa kafin ya qaraso ta tattara dukka nutsuwarta,ta kuma bude dukkan basirarta dake mata jagora zuwa fahimtar zurfin tunanin dan adam a sanda taso karantarsa.
"Wa'alaikumussalam......bismillah" Abinda tace da haisam kenan a sanda ya qaraso farfajiyar da take zaune.
A nutse ya taka yana isa gaban wata kujera qwaya daya data fita daban da sauran,yayi bismillah a hankali yana zama,saita daga kanta tana duban yalwa.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/22, 19:59] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 37*
"A marabceshi kamar kowa.....a kuma wadatashi da dukkan abun ci da abun sha" Ta furta da cikakkiyar izzar dake nuna girma da nisan inda ta dauki kanta da kuma kalar matsayin data bashi.
Idanunta ta daga a hankali,tana iya karantar zallar nutsuwar dake kwance saman fuskarsa,ba wani tsoro ko fargabar kasancewarsa a gabanta,duk da yadda takewa tarin mutane kwarjinin da ko cikakken zama a gabanta ba kowa ke iya yinsa. Wani adanannen kwarjini da tasa aka mata tattalinsa daga kowanne jini dake harbawa a jikinta.
"Sheikh haisam.....tuntuni na aika a kiramin kai......ba'a sanar maka bane?" Tayi tambayar da manufa tayin titsiye da kuma son ganin adadin girma da kwarjinin data yiwa idanunsa da zuciyarsa.
Kai ya gyada a nutse bayan ta ajiye tambayarta harma ta huta ta hanyar shaqar sabon numfashi,yana jin kamar nashi jinin OROMIA din yana shirin motsa masa,jinin ABA JIFAR amma yasa wani abu me nauyi ya danneshi yana daidaita yanayinsa da lokacin.
"Eh an sanar dani" Ya amsa mata a taqaice. Yadda ya amsa mata kai tsaye ba wani kwana kwana ko neman boye laifinsa ya tabata sosai,abinda bata taba gani ba,bata kuma saba gani ba,sai ta jinjina kai.
"An sanar dakai.....amma ka bata wasu mintuna da suka kusa tasamma jimillar awa guda cif,na kiraka ka wofantar da kiran?" Ta fadi da zafi zafi wannan karon a muryarta.
Kamar dazun,sai daya shaqi nutsatstsiyar iska sannan ya sake motsa labbansa.
"Akwai banbamci tsakanin wofantarwa da zuwa a makare......ba kowanne kira bane amsashi akan lokacin da aka yishi yake nuna girmamawa ba......manufar daya ce wanda aka kira ya amsa......gani na amsa a lokacin da yafi dacewa......idan kuma ba damuwa,kamar shiga cikin maganar kai tsaye zaifi,saboda mu ceci lokaci ni dake gaba daya" Yayi maganar kansa tsaye yana zube idanunsa cikin nata.
Kafeshi takeso tayi da idanunta,amma ta rasa wannan qwarin gwiwar,saita janye dubanta a kansa,zuciyar taqi yarda da kwarjini yayi mata,saidai tafi alaqanta hakan da fushin da takeji a kansa. Bata jin zata sakar masa wanna gabar da sauri haka ba tare data saukar masa da warning ba saboda gaba
"Cikin masarautar nan.....cikarta da batsewarta.......yana zama wajibi akan dukkan wanda na kirashi ya amsa kirana a sanda na buqata". Kansa ya juya a hankali,ya fahimci maganan rashin xuwa kiranta a sanda taso ta mata zafi sosai,hakan shi kuma yayi masa.
"A tawa al'adar da yaren.....girmamawa sifface ta dattako.....ga duk wanda ya amsa kiranka ya girmama koda baizo a sanda ka buqata ba" Ya amsa mata yana sassauta harshensa. Bayaso nan da nan tayi fusatar da zata rudar da hankalin omari daga fuskantar abinda haisam din yakeso ya fuskanta. Maganar tasa ya daketa ta kuma taso da wani tsohon al'ada da wata tsohuwar karin magana daga asalin nata yaran,ta kuma motsa idanunta kamar zata waiwaya gareshi ta kalleshi don tabbatar da abinda ya fada,amma koda ta tuna da nata mission din saita kauda hakan. Saidai hakan da tayi bai hanashi daukan haske ba.
"Ka zartar da wasu sabbi kuma baqin dokoki ba tare da neman ta bakina ko ganawa dani ba.....shin waye ya baka wannan izinin?". Murmushi ne dan siriri ya qwace masa,saidai ya tsaya iya labbansa,duk da hakan kuma bai hana tsarguwar mammina ba da rayawa a ranta kamar murmushin taga yayi ba,saidai bai bata dukkan dama ta gane hakan ba.
Ya kamata tambayar ta bashi mamaki,amma kuma yadda ya tsammaci tuhume tuhumenta zasu iso haka suka sameshi.
"Ba kowa".
"Ba kowa?" Ta tambaya a mamakance,tana jin ta samu gaba da zata soke kowacce doka hankali kwance.
"Eh.....ba kowa,saidai bayan na gama rubuta dukkan dokokin,na gabatarwa da sultane,inda hankalinki a nutse yake da zaki iya ganin stamp da sanya hannun sultane qasan kowacce doka" Ya fada da wani irin calmness yana sake tattara nazarinsa a kanta.
Wani shocked taji sosai har cikin jininta,jin da sanya hannun sultane aka wanzar da komai,ba tare da kuma sultane ya kirata yaji ta bakinta ba yadda suka saba sanya kowacce sabuwar doka a tare.
"Na tabbatar daukuwa da hankalin sultane yayi ne kan wannan tafiyar ya hanashi nemana......amma hakan bawai yana nufin kana da qarfin ikon zartar da doka kai kadai ba". Kansa ya sake juyawa a hankali,cikin Tarin nutsuwa idanunsa tsakiyar nata yace.
"Sanya hannun sultane ya wadatar........dokar bata an qirqireta bane saboda ke,an qirqireta ne saboda masarauta.....shi yasa ya zamana ba wani laifi don an kafata ko an zartar da ita bada saninki ba.....dukkanin dokar an yita ne saboda tsaron masarauta"
"Tsaro ga masarauta ko kuma neman ikon sarrafa komai da kowa?" Murmushi ya sakeyi kadan,na wannan karon yafi na dazu bayyana.
"Ikon sarrafa komai wannan siffar Allah ce mahalicci shi kadai.....ni dake da sultane duk bamu da hurumi a kanta". Maganar tasa sai taji kaman yana qoqarin tube mata rawanin ikonta ne,don haka cikin qanqance idanu tace masa.
" Kasan wacece ni kuwa?".
"Kowa nasan wayeshi.....kowa kuma nasan wa yake qoqarin zamantowa ko kasancewa kamar shi". Wani irin abu taji ya sauka yana sarar gabban jikinta. Wani irin gumi taji yana qoqarin tsatstsafo mata,saidai tasan barin hakan ya faru,barinsa ya karanci hakan babban kuskure ne a tare da ita,don zuwa yanzu cikin jikinta takejin BA HAKA KAWAI YA SHIGO AGADEZ BA....BA HAKA KAWAI YA SHIGO MASARAUTA BA.....BA GAMA GARIN MALAMI BANE.
"Amma kasan cewa masarautarmu a zaune take lafiya kafin shigowarka cikinta?" Ta sake fadi yanayinta yana nuna fara daukan zafi.
"Zaman lafiya ba shine shuru ba......wani lokaci shuru yana boye abubuwa masu nauyin gaske....cikin rashin sa'a saika dauka lafiya ce ta kurmantar da komai din" Ya amsa mata da wani irin nutsuwa a tattare dashi. A karo na biyu ta sake jin kamar dutse ya dauka ya jefeta dashi cikin tsakiyar kanta.
"Waye shi?" Ta samu kanta da tambayar kanta da kanta,zuciyarta da tunaninta suna neman zamewa. Zuciyarta ke mata wani irin tsalle,tana kuma cikata da shakku a kansa,sannan tana son jefa mata rudanin da bata shirya ko tunanin fuskantarsa ba a daidai lokacin.
"Akwai wani da kake zargi?....ko akwai wani abun zargi cikin masarautar damu muka gaza hangoshi sai kai?". Tayi tambayar cikin zafi,tambayar data sanya ita da kanta wuta dauke mata,don bata tsara ta fidda masa zafinta har haka akan komai ba.