Sashe 88
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/10, 19:49] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 77*
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
A nutse ya ajiye mug din hannunsa,don dama ya gama breakfast dinsa,ita gejin cikinsa kenan.
Maganan zuwansa da ya amsa a jiyan yana sane dashi,kuma koda bata aiko ba tunda ya amsa zaije din zaije. Inda baiyi niyyan zuwa ba,baiga dalilin da zai sanyashi ya amsa mata ba.
"Ta dakaci zuwana daga yanzu zuwa kowanne lokaci". Ya amsa masa yana jawo wayarsa dake gefe. Mutum ne shi ma'abocin son cika alqawari,kyautatawa da kyakkyawar mu'amala tsakaninsa da duk wanda yake rayuwa a qarqashinsa. Ballantana nanay dinsa,da niyyar kiran saamee ya tashi,ya kuma gamsu da ya kirata din saboda farantawa nanay rai,da kuma samar da relief ga Yarinyar. Duk da ta bangarensa baya duban hakan a matsayin maslaha sam.....baya son abinda zai sanya ta sake aza ranta ga komai daya shafeshi.
*SAAMEE*
A hankali ta waiwaya tana duban wayarta dake ajiye saman abun sallar da take kai daga gefanta. Idanunta ta ware sosai,zuciyarta tana wani irin bugawa da ganin sunan dake harbawa a fuskar wayartata.
"Captain obbo" Ta karanta sunan a fili tana jin yadda zuciyarta ke bugawa b'al b'al kamar zata huda qirjinta. Wani yanayi ne daban.....wani abune na daban me matuqar shammata da bata taba zaton faruwarsa ba.
Ko ina na jikinta rawa yakeyi,ta daga wayar ta karata a kunnenta. Sallama tayi masa,irin sallamar dake bayyana yadda muryarta ke sake raunana da wani irin rawa na zallar kwarjinin da yake mata.
"Barka da warhaka Obboleettii" Ta fada a sanyaye bayan ya amsa sallamartata.
"Barkanki sameera.....ya jikin naki?" Sai data lumshe idanunta a hankali,dadin muryarsa yana ratsata. Wani irin amo mejan hankali daya saukar mata da wata irin nutsuwa,har batasan ta saki siririyar ajiyar zuciya ba.
"Alhamdulillah obbo....da sauqi".
"Ma sha Allah" Ya fadi sannan shuru na wasu sakanni ya biyo baya kafin ya dora.
"A rayuwar dan adam gaba daya lafiya itace gaba da komai....yana da kyau ki sanya lafiyarki gaba da kowa da kuma komai.....ki zabi kanki kafin komai da kowa......sannan ki kusanta kanki fiye da baya da karatun qur'ani,domin da ambaton Allah kadai zukata suke samun nutsuwa".
"Na gode obbo" Ta fadi da wani irin sanyi,tana jin dadi yana sauka mata a ranta. Ba'a banza zuciyarta take nacewa da soyayyarsa ba,ba'a banza takejin ta kowanne taqi na rayuwarta yayi mata ba,ba'a banza takejin da ita kadai ya dace ba. Miji take nema dan gaske me kamala koda shigen tasa ce.....mijin da zai kama hannunta ya kusantata zuwa ga Allah da kuma dokokin Allah,sai akayi sa'a idanunta suka sauka a kanshi. Duk kuwa da cewa zuciyarta tasha gargadarta akan cewa haisam din ya mata NISA.....ya mata TAZARA ya d'ara ajinta. Tana jin kamar ba zata sameshi ba......tanajin ita din sam ba ajinsa bace,to amma kuma ta rasa ta yadda zata fara tanqwara zuciyarta ta cire hakan daga ranta.
"Ki kula da nutsuwar ruhinki,abinci sannan magani". Ya furta cikin yanayin kulawar daya sanya murmushi qwace mata.
"In sha Allah obbo,na gode" Da godiyar tata da bataji abinda ya fadi ba kiran nasa ya tsinke,tana jin kamar ta tambayeshi yaushe zai dawo?,yaushe zata ganshi?.
Rungume wayar tayi a qirji tana lumshe idanunta. Wani irin murmushi ne kawai yake fita saman fuskarta. A iya maganganunsa na yanzun takejin basai ta sake shan wani magani ba kuma a yau din. Bata zata ba ta tsinci muryar nanay saman kanta.
"Ikon Allah......bacci kike ko idanunki biyu?" Nanay ta tambayeta tana ci gaba da leqa fuskarta dake shimfide da wani kalar murmushi. Da sauri ta miqe ta zauna tana sunkuyar da kanta.
"Idona biyu nanay,sallah na gama yi". Kallo Nanay tabi hannunta dashi,sai ta ganta damqe da wayarta,murmushi ya subuce mata. Da alama sirrin walwalarta haisam ne,taji hakan a jikinta,don ta tabbatar haisam din bazai tsallake alfarmar data nema ba dama.
"Shikenan yi kwanciyarki,zamu fita gidan marayu ne,nace bari na leqo naga jikinki"
"Saikin dawo nanay,Allah ya bada sa'a,na gode sosai" Ta fadi still tana kasa hada idanu da ita,itama saita juya ta fice ranta yana mata dadi ganin karon farko yanayin saamee din yana daidaita.
*HAISAM*
Samansa kawai ya koma,ya kuma wuce bathroom yana fidda kayan jikinsa. Faffada kuma lallausan towel ya daura a qugunsa,abinda ya bawa lafiyayyar qirar jikin nan nasa dama fitowa sosai. Faffadan qirji me dauke da mayalwatan kafadu......muscles da suka cika dantsensa wadanda yawan daga qarfe ya sanya suka zauna masa sosai. Tun daga saman cikinsa har zuwa qirjinsa lallausan gashi ne baqi sidik da ya yiwa fatar jikinsa qawanya,hakanan gwiwar hannunsa har zuwa tsintsiyar hannunza,kaman yadda cinyoyinsa har zuwa idanun sahunsa sassalkar gargasa ce dake qara nuna ainihin qirar cikakken lafiyayyen namiji.
Bai wani damu da adadin lokutan daya dauka ba,ya shirya fes cikin daya daga cikin throbe din da wani company daga qasar oman. Silk ce irin silk dinnan me asalin tsada da daukan idanu,sai ya daura amam a kansa da wani irin yanayi me birgewa,irin salon nadin matasan qasar saudiyya. Kusan deal ne tsakaninsa da fitattun kamfanonin throbe(jallabiyya) dake qasashen sudan,oman,saudiyya,dubai,Morocco,qatar,Kuwait. Duk bayan watannin da sukan fidda sabbin design na throbe na maza shine mutum na farko a Ethiopia gaba daya dake fara sanya new arrivals na throbe dinsu. Kusan duk wani malami ko diyan sarauta dake ji da kansa cikin Ethiopia da zagayenta yana kwaikwayo ne da sheikh muhammad haisam aba jifar. Yana da wani irin salo na iya ado tamkar dawisu,adon da har a yanzu a agadez bai canza ba. Dressing dinsa a koda yaushe unique ne,cikin wani irin yanayi da idanu basu saba ganinsa ba. Ya zamewa yaran sarakuna da yawa a Ethiopia role model,wajen qurewa ado gudu ba'a kaishi ba.
Tun daga kan cloak thobe.....jubahs da fitattaun kurta pyjamas a gurinsa ake fara ganin sample. Hakan kuma ya zame masa jiki. Tun yana da shekara goma a duniya ya zama DAN SARKI DA YASHA BANBAM DA SAURAN YARAN SARAKUNA.....kuma har yanzun da yake kan ganiyar samartakarsa ba abinda ya canza,saima sake daukan hankulan 'ya'yan manya dana malamai da yake sakeyi cikin qasar tasa.
Qamshin nan dai nasa da shi kadai ya mallakeshi ke tashi a jikinsa,ya zura wasu budaddun takalma masu wani irin aji a zubi da tsarinsu.
Yana saukowa daga sama idanun omar a kansa,suka hada ido sai ya janye dubansa yana duban maleek da ya miqe qafafunsa saman center table na glass yana aiki cikin system dinsa.
"Nidai kawai jikina yake bani akwai abubuwa da yawa da ake binnewa.....jiya bobbo dawud ya kirani yace komin dare na hadaka dashi......amma koda nazo tun daga babbar qofar shigowa sabuwar dokarka cikin masarautar nan ta hanani daman shigowa" Duk da ba haka yaso ba,amma yaji dadin jin hakan,hakan yana nuna masa da gaske ana tafi da dokar yadda ta dace kenan kamar yadda ya shimfida.
Sai daya gama saukowa gaba daya sannan maleek ya dauke idanunsa daga kan system din ya maida kan haisam sanda ya dauki dabino bakwai cikin wanda ke zube a wani qawataccen gold plate dake ajiye a gurin.
"Sai ina?" Maleek ya tambaya kai tsaye,don yanason ya zauna suyi magana da haisam akan falaak. Abinda yakeji tattare da ita ya girmeshi,yana jin kamar kwanakin da motii ya dauka be dawo ba suna da nisan gaske.
"Zanje.....zaituna nason ganina" Haisam ya fadi yana cire qwallon dabinon daya dauka din. Sosai omar ya koma ya zauna yana duban haisam.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Kiranka kuma?,to ko nazo muje?" Sosai maganan ta bashi dariya,amma sai ya saki murmushi sanda yake jefa dabinon bakinsa yana taunashi a hankali. Ya yadda qwarai da gaske garin suna da albarkar dabino suma kamar qasarsu,a wasu abubuwan hana hangen kamanceceniya kadan kadan.
"Ka rakani?,saboda me?"
"Saboda tsaro mana haisam" Omar ya furta da dukkan gaskiyarsa. Murmushi ya kuma saki,sannan ya fara takawa a hankali da alama yana nufar hanyar fita ne.
"Shi zaki koda ba'a cikin gandun dajinsa ba ya tsinci kansa yana yin farautarss ne yadda yaga dama,duk wani kira.....duk wani kebewa,duk wani magana da zata nemi tayi dani yana zamantowa kaman qarin dama ce a tare dani,qarin daman da zan samu na buda mata hanyar da zata dilmiya kanta da kanta" Ya qarasa maganar a huce kuma hankali kwance.
"Amma ko connection ya kamata ka hada dani"
"Babu buqata.....saina dawo" Ya fadi yana saka qafafunsa waje.
Ajiyar zuciya maleek ya sauke,ya kuma maida dubansa ga omar da har yanzu yabar bakinsa a sake.
"Duk inda kake ajiye haisam ya wuce nan gurin.....ya wuce hasashena da naka,hakanan ya zarta tunaninmu,duk wani motsi da taku da zaiyi lissafinsa daban yake da namu.....yanayin jarumtarsa yana bani tsoro a wasu lokuta. Baisan tsoro ba....baissn fargaba ba,baya banbamce guri me hadari da akasin hakan a duk sanda ya sanya gabansa gaba a kan aikinsa.....yana da yaqini cikakke ga mahaliccinsa......zai dawo omar.....zai dawo lafiya ina da yaqini da hakan.....addu'a ta ratsashi fiye da zatonmu da kallon da muke masa,a kwanakin nan ni kaina nasan da haka,shi yasa baya shakkar kowa da komai,baya kuma shakkar tunkarar komai din" Sosai omar ke jinjina kansa,yana kuma sake gamsuwa dari bisa dari da maganganun maleek.
*MAMMINA*
Wannan karon kuma a wannan lokacin da kanta take takawa zuwa bakin iyakar gurin,cikin salo na kai kawo tare da tarin tsammanin jiran isowar haisam din.
Har wani zabalbala takeji jininta yana yi idan ta tuna cewa yau itace ke maimaita kiran wani d'ana adam dake rayuwa cikin masarautar agadez qarqashin alfarmarta?,bayan yayi watsi da kiran kuma har sai ya zabi lokacin zuwa?.
Ranta yana son ya cimma qololuwar baci,amma kuma tana danne hakan daga ranta,don a yanzu ba fusata ko tursasawa take buqata suyi mata aiki ba. Kwantar da kai,maida komai ba'a bakin komai ba da kuma nuna masa zallar karamci da tarin abun duniyar da zai iya rabauta dashi,su kadai ne makaman da tafi buqata a yanzu.
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/10, 19:49] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 77*
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
A nutse ya ajiye mug din hannunsa,don dama ya gama breakfast dinsa,ita gejin cikinsa kenan.
Maganan zuwansa da ya amsa a jiyan yana sane dashi,kuma koda bata aiko ba tunda ya amsa zaije din zaije. Inda baiyi niyyan zuwa ba,baiga dalilin da zai sanyashi ya amsa mata ba.
"Ta dakaci zuwana daga yanzu zuwa kowanne lokaci". Ya amsa masa yana jawo wayarsa dake gefe. Mutum ne shi ma'abocin son cika alqawari,kyautatawa da kyakkyawar mu'amala tsakaninsa da duk wanda yake rayuwa a qarqashinsa. Ballantana nanay dinsa,da niyyar kiran saamee ya tashi,ya kuma gamsu da ya kirata din saboda farantawa nanay rai,da kuma samar da relief ga Yarinyar. Duk da ta bangarensa baya duban hakan a matsayin maslaha sam.....baya son abinda zai sanya ta sake aza ranta ga komai daya shafeshi.
*SAAMEE*
A hankali ta waiwaya tana duban wayarta dake ajiye saman abun sallar da take kai daga gefanta. Idanunta ta ware sosai,zuciyarta tana wani irin bugawa da ganin sunan dake harbawa a fuskar wayartata.
"Captain obbo" Ta karanta sunan a fili tana jin yadda zuciyarta ke bugawa b'al b'al kamar zata huda qirjinta. Wani yanayi ne daban.....wani abune na daban me matuqar shammata da bata taba zaton faruwarsa ba.
Ko ina na jikinta rawa yakeyi,ta daga wayar ta karata a kunnenta. Sallama tayi masa,irin sallamar dake bayyana yadda muryarta ke sake raunana da wani irin rawa na zallar kwarjinin da yake mata.
"Barka da warhaka Obboleettii" Ta fada a sanyaye bayan ya amsa sallamartata.
"Barkanki sameera.....ya jikin naki?" Sai data lumshe idanunta a hankali,dadin muryarsa yana ratsata. Wani irin amo mejan hankali daya saukar mata da wata irin nutsuwa,har batasan ta saki siririyar ajiyar zuciya ba.
"Alhamdulillah obbo....da sauqi".
"Ma sha Allah" Ya fadi sannan shuru na wasu sakanni ya biyo baya kafin ya dora.
"A rayuwar dan adam gaba daya lafiya itace gaba da komai....yana da kyau ki sanya lafiyarki gaba da kowa da kuma komai.....ki zabi kanki kafin komai da kowa......sannan ki kusanta kanki fiye da baya da karatun qur'ani,domin da ambaton Allah kadai zukata suke samun nutsuwa".
"Na gode obbo" Ta fadi da wani irin sanyi,tana jin dadi yana sauka mata a ranta. Ba'a banza zuciyarta take nacewa da soyayyarsa ba,ba'a banza takejin ta kowanne taqi na rayuwarta yayi mata ba,ba'a banza takejin da ita kadai ya dace ba. Miji take nema dan gaske me kamala koda shigen tasa ce.....mijin da zai kama hannunta ya kusantata zuwa ga Allah da kuma dokokin Allah,sai akayi sa'a idanunta suka sauka a kanshi. Duk kuwa da cewa zuciyarta tasha gargadarta akan cewa haisam din ya mata NISA.....ya mata TAZARA ya d'ara ajinta. Tana jin kamar ba zata sameshi ba......tanajin ita din sam ba ajinsa bace,to amma kuma ta rasa ta yadda zata fara tanqwara zuciyarta ta cire hakan daga ranta.
"Ki kula da nutsuwar ruhinki,abinci sannan magani". Ya furta cikin yanayin kulawar daya sanya murmushi qwace mata.
"In sha Allah obbo,na gode" Da godiyar tata da bataji abinda ya fadi ba kiran nasa ya tsinke,tana jin kamar ta tambayeshi yaushe zai dawo?,yaushe zata ganshi?.
Rungume wayar tayi a qirji tana lumshe idanunta. Wani irin murmushi ne kawai yake fita saman fuskarta. A iya maganganunsa na yanzun takejin basai ta sake shan wani magani ba kuma a yau din. Bata zata ba ta tsinci muryar nanay saman kanta.
"Ikon Allah......bacci kike ko idanunki biyu?" Nanay ta tambayeta tana ci gaba da leqa fuskarta dake shimfide da wani kalar murmushi. Da sauri ta miqe ta zauna tana sunkuyar da kanta.
"Idona biyu nanay,sallah na gama yi". Kallo Nanay tabi hannunta dashi,sai ta ganta damqe da wayarta,murmushi ya subuce mata. Da alama sirrin walwalarta haisam ne,taji hakan a jikinta,don ta tabbatar haisam din bazai tsallake alfarmar data nema ba dama.
"Shikenan yi kwanciyarki,zamu fita gidan marayu ne,nace bari na leqo naga jikinki"
"Saikin dawo nanay,Allah ya bada sa'a,na gode sosai" Ta fadi still tana kasa hada idanu da ita,itama saita juya ta fice ranta yana mata dadi ganin karon farko yanayin saamee din yana daidaita.
*HAISAM*
Samansa kawai ya koma,ya kuma wuce bathroom yana fidda kayan jikinsa. Faffada kuma lallausan towel ya daura a qugunsa,abinda ya bawa lafiyayyar qirar jikin nan nasa dama fitowa sosai. Faffadan qirji me dauke da mayalwatan kafadu......muscles da suka cika dantsensa wadanda yawan daga qarfe ya sanya suka zauna masa sosai. Tun daga saman cikinsa har zuwa qirjinsa lallausan gashi ne baqi sidik da ya yiwa fatar jikinsa qawanya,hakanan gwiwar hannunsa har zuwa tsintsiyar hannunza,kaman yadda cinyoyinsa har zuwa idanun sahunsa sassalkar gargasa ce dake qara nuna ainihin qirar cikakken lafiyayyen namiji.
Bai wani damu da adadin lokutan daya dauka ba,ya shirya fes cikin daya daga cikin throbe din da wani company daga qasar oman. Silk ce irin silk dinnan me asalin tsada da daukan idanu,sai ya daura amam a kansa da wani irin yanayi me birgewa,irin salon nadin matasan qasar saudiyya. Kusan deal ne tsakaninsa da fitattun kamfanonin throbe(jallabiyya) dake qasashen sudan,oman,saudiyya,dubai,Morocco,qatar,Kuwait. Duk bayan watannin da sukan fidda sabbin design na throbe na maza shine mutum na farko a Ethiopia gaba daya dake fara sanya new arrivals na throbe dinsu. Kusan duk wani malami ko diyan sarauta dake ji da kansa cikin Ethiopia da zagayenta yana kwaikwayo ne da sheikh muhammad haisam aba jifar. Yana da wani irin salo na iya ado tamkar dawisu,adon da har a yanzu a agadez bai canza ba. Dressing dinsa a koda yaushe unique ne,cikin wani irin yanayi da idanu basu saba ganinsa ba. Ya zamewa yaran sarakuna da yawa a Ethiopia role model,wajen qurewa ado gudu ba'a kaishi ba.
Tun daga kan cloak thobe.....jubahs da fitattaun kurta pyjamas a gurinsa ake fara ganin sample. Hakan kuma ya zame masa jiki. Tun yana da shekara goma a duniya ya zama DAN SARKI DA YASHA BANBAM DA SAURAN YARAN SARAKUNA.....kuma har yanzun da yake kan ganiyar samartakarsa ba abinda ya canza,saima sake daukan hankulan 'ya'yan manya dana malamai da yake sakeyi cikin qasar tasa.
Qamshin nan dai nasa da shi kadai ya mallakeshi ke tashi a jikinsa,ya zura wasu budaddun takalma masu wani irin aji a zubi da tsarinsu.
Yana saukowa daga sama idanun omar a kansa,suka hada ido sai ya janye dubansa yana duban maleek da ya miqe qafafunsa saman center table na glass yana aiki cikin system dinsa.
"Nidai kawai jikina yake bani akwai abubuwa da yawa da ake binnewa.....jiya bobbo dawud ya kirani yace komin dare na hadaka dashi......amma koda nazo tun daga babbar qofar shigowa sabuwar dokarka cikin masarautar nan ta hanani daman shigowa" Duk da ba haka yaso ba,amma yaji dadin jin hakan,hakan yana nuna masa da gaske ana tafi da dokar yadda ta dace kenan kamar yadda ya shimfida.
Sai daya gama saukowa gaba daya sannan maleek ya dauke idanunsa daga kan system din ya maida kan haisam sanda ya dauki dabino bakwai cikin wanda ke zube a wani qawataccen gold plate dake ajiye a gurin.
"Sai ina?" Maleek ya tambaya kai tsaye,don yanason ya zauna suyi magana da haisam akan falaak. Abinda yakeji tattare da ita ya girmeshi,yana jin kamar kwanakin da motii ya dauka be dawo ba suna da nisan gaske.
"Zanje.....zaituna nason ganina" Haisam ya fadi yana cire qwallon dabinon daya dauka din. Sosai omar ya koma ya zauna yana duban haisam.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Kiranka kuma?,to ko nazo muje?" Sosai maganan ta bashi dariya,amma sai ya saki murmushi sanda yake jefa dabinon bakinsa yana taunashi a hankali. Ya yadda qwarai da gaske garin suna da albarkar dabino suma kamar qasarsu,a wasu abubuwan hana hangen kamanceceniya kadan kadan.
"Ka rakani?,saboda me?"
"Saboda tsaro mana haisam" Omar ya furta da dukkan gaskiyarsa. Murmushi ya kuma saki,sannan ya fara takawa a hankali da alama yana nufar hanyar fita ne.
"Shi zaki koda ba'a cikin gandun dajinsa ba ya tsinci kansa yana yin farautarss ne yadda yaga dama,duk wani kira.....duk wani kebewa,duk wani magana da zata nemi tayi dani yana zamantowa kaman qarin dama ce a tare dani,qarin daman da zan samu na buda mata hanyar da zata dilmiya kanta da kanta" Ya qarasa maganar a huce kuma hankali kwance.
"Amma ko connection ya kamata ka hada dani"
"Babu buqata.....saina dawo" Ya fadi yana saka qafafunsa waje.
Ajiyar zuciya maleek ya sauke,ya kuma maida dubansa ga omar da har yanzu yabar bakinsa a sake.
"Duk inda kake ajiye haisam ya wuce nan gurin.....ya wuce hasashena da naka,hakanan ya zarta tunaninmu,duk wani motsi da taku da zaiyi lissafinsa daban yake da namu.....yanayin jarumtarsa yana bani tsoro a wasu lokuta. Baisan tsoro ba....baissn fargaba ba,baya banbamce guri me hadari da akasin hakan a duk sanda ya sanya gabansa gaba a kan aikinsa.....yana da yaqini cikakke ga mahaliccinsa......zai dawo omar.....zai dawo lafiya ina da yaqini da hakan.....addu'a ta ratsashi fiye da zatonmu da kallon da muke masa,a kwanakin nan ni kaina nasan da haka,shi yasa baya shakkar kowa da komai,baya kuma shakkar tunkarar komai din" Sosai omar ke jinjina kansa,yana kuma sake gamsuwa dari bisa dari da maganganun maleek.
*MAMMINA*
Wannan karon kuma a wannan lokacin da kanta take takawa zuwa bakin iyakar gurin,cikin salo na kai kawo tare da tarin tsammanin jiran isowar haisam din.
Har wani zabalbala takeji jininta yana yi idan ta tuna cewa yau itace ke maimaita kiran wani d'ana adam dake rayuwa cikin masarautar agadez qarqashin alfarmarta?,bayan yayi watsi da kiran kuma har sai ya zabi lokacin zuwa?.
Ranta yana son ya cimma qololuwar baci,amma kuma tana danne hakan daga ranta,don a yanzu ba fusata ko tursasawa take buqata suyi mata aiki ba. Kwantar da kai,maida komai ba'a bakin komai ba da kuma nuna masa zallar karamci da tarin abun duniyar da zai iya rabauta dashi,su kadai ne makaman da tafi buqata a yanzu.