← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 101

Sashe 68

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/3, 20:17] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 60*

*MORSA SAFIYYA*

Duk da cewa wani sashe na zuciyarta yana riqe da lissafin daga yanzu zuwa kowanne lokaci akhnan tana iya qaura tana iya barin gidan zuwa gidan mijin da har yanzu batasan wani mutum guda daya daya jibancesu da zai iya shaida fuskarsa ba........amma tana jin wani irin sassauci daga damuwarta data fara shiga a farkon maganar.

Batasan me ya kawo sassaucin ba......batasan hujja ko dalili ba,saidai tana kyautata zaton ADDU'O'IN da take shafe dare tana yi ne. Babu wani dare da zai keto sararin subhana ta kwanta tayi bacci ta kuma qarar dashi tas ba tare data tsaida duga duganta gaban mahaliccinta ba.

Tana saman dining hadimarta samiya tana shirya mata abincin rana,wanda bata samu zama ta cishi ba saboda sallamar baqi dake gabanta da suka samu halartar biki. Duk da bikin ba'a cikashi da kalolin bidi'a ba,amma kuma ahalin diory hamani sun nuna kara,sun kuma nuna zallar zumuntar data kasance abu mafi girma da qarfi a tsakaninsu.

A nutse ta amsa sallamar armelle da wannan kamilar fuskartata ma'abocin tarbar dukkan wanda yazo gareta da girmamawa.

"Qaraso mana armelle" Ta fada tana yin bismillah hadi da soma kai lomar abincin bakinta. Kamar yadda ta buqata haka armelle din ta qaraso,ta samu daya daga cikin kujerun dake nesa kadan da morsa safiyya din ta zauna akai. Wani abu dake bawa kusan kowa mamaki,tana da wani irin sauqin kai.....bata da izzar da zaka kiranta matar babban mutum me daraja ta daya a yankin wato sultane of agadez. Ta dauki hadimanta a matsayin nata,hadimanta wasu mutane ne da take ganin kimarsu sosai,girmamawa da mutuntawa take musu kamar yadda zata karrama kowanne dan adam.

"Lafiya dai ko armelle?"Morsa ta tambayeta tana tattara hankalinta a kanta. Dub daya ta yiwa morsa safiyyan,ta kalli abincin kuma dake ajiye a gabanta,sai wani irin tausayinta ya kamata. Ta sani ta dauki darare da kwanaki masu yawa bata zauna ta sanya abinci haka a cikinta ba,ta tabbatar a yanzu idan har ta isar mata da saqon da take dauke dashi to ba shakka wannan abincin ya haramta a tare da ita. Murmushi ta sakar mata.

"Ba komai....wata maganace nakeso muyi,amma da fari uwargijiyata ki kammala cin abincinki,don na tabbatar kin jima baki zauna haka don kawai kici abinci ba" Dan qaramin murmushi morsa safiyya ta saki,murmushin da ya narkar da zuciyar armelle gaba daya. Murmushinan dake dauke da tarin alkhairi.....murmushin nan dake qunshe da kyautatawa,murmushin kuma da ya sake bayyana kamanninta da SAFEENA SOSAI.

Safeenar da babu wata zuciya me alkhairi da zata iya mancewa da ita....safeenan da komai butulcinka cikin gidan baka isa kace bakaci arziqinta ba.....safeenar da aka tilastawa zukata masu yawan gaske lullube sunanta....danne ambaton alkhairinta.....tunata,ambatarta,dama ambatar dukkan abinda ya shafeta,saidai ita zuciyar da alkhairi ya cikata......zai wahala wani abu ya danne ganin alkhairin waninta.

Hawaye taji sun cika mata idanu sanda morsa safiyya ke cewa.

"Yau lelena akeyi armelle,shikenan bari nayi na kammala saimu zauna" Saita maida kai sosai tana qara hanzarin cin abincin,tasan kuma tayi hakanne kawai don ta saurareta,abinda ya saukar da wani abu me nauyi saman zuciyar armelle wanda ta kasa daureshi,har sai da tayi qasa da kanta tana boye hawayenta.

"Na kammala armelle.....amma koma meye abinda ke tafe dake da alama yana da girma" Morsa ta furta cikin nuna kulawarta ga armelle din.

Idanunta da suka sauya launi kadan ta daga,ta kuma kalli morsa dashi.

"Yana da girma uwar gijiyata,don na jima banga ko banji abu me girma kamar wannan ba....." Kai ta gyada ta kasa cewa komai tana ci gaba da kallonta.

"Ko.meye zaki jishi daga bakina ina me roqarki ki karbeshi da sauqi ta sigar yadda zai sauka a zuciyarki.....amma ki tashi da dukkan zafinki wajen ganin komai bai sake maimaita kanshi ba"

"In sha Allah armelle.....in sha Allah" Ta fada cikin mutuntawa da dattako,don armelle din na cikin tsaffin hadiman gidan dake da wani irin girma na musamman.

"Auren akhnan ya mutu awa daya data wuce,mijin daya aureta ya saketa har saki uku" Wani irin abu me nauyin gaske morsa safiyya taji yana sauko mata. Banda armelle ce ga fada....banda ba wasa a tsakaninsu,banda kuma kuma ita din ba abokiyar wasanta bace bata yadda za'ayi maganan ya shiga kunnenta ya samu mazauni a zuciyarta,duk da haka sai data rutsa armelle da kallo kamar me kokwanto,kafin yanayin armelle din ya gasgata mata abinda ta fada din shine dai kwance kuma rubuce cikin idanunta.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Shine abinda morsa safiyya ta maimaita har sau uku,tana sanya hannuwanta gami da dafe kanta.

*MAMMINA*

Tun a cikin motar tafisu ke zaune gaban mammina,tana kuma shafa mata man zafi a qafarta data fara kumbura kadan. Saidai sam ciwon da takeji a cikin qafafunta baikai koda quarter din wanda takeji a jikinta da zuciyarta ba. Ta kammala sanya mata maganin ta maidashi jikin wani abu dake maqale jikin kujerun dake a gabansu,ta daga idanunta tana duban mammina din.

"Ta ina zamu fara gyara da fuskantar wannan matsalar?" Mammina tayi maganan kai tsaye ba tare data dubi tafisu ba. Numfashi ta sauke tana murza yatsunta,fuskarta da dukka yanayinta yana nuna itadin cikakkiyar baqar ba'abzina ce.

"Meye hasashenki uwar gijiyata,kada na miki azarbabi......amma banajin dama ya kamata mubar wannan ranar ta wuce ba tare da hasashen komai da zai iya faruwa ba da yadda zamu tunkareshi ba. Kai mammina ta jinjina,sannan tace.

"Da farko ban yanke zuwa gurin akhnan da wuri ba,domin hakan zai sanya zargi da dama a zukatan wadanda ke farautar motsina". Shuru kadan tafisu tayi sannan ta amsa mata.

" Zuwanki da wuri.yana da ma'ana da alfanu,kamar yadda jinkirin zuwanki shima zai zama yana da nasa alfanun,amma a wannan gabar na bar miki dukkan zabi". Idanu mammina ta sauke a kan tafisu.

"Dukka wannan ba wani damuwa bace me girma a guna,koda akhnan taga kyautatawar zuwana da wuri ko bata gani ba.....abi mafi girman damuwa a gurina shine sultane.......banaso na rasa YARDA daga gurin sultane.... Lokacin rasa yardata a tare dashi baiyi ba.....har yanzu akwai GABAR da ban isa gareta ba,muddin na rasa yarda da aminci daga sultane na rasa rabin shiri na,zai zabtare ne ya zube ya barni da tarin burikana......ta wacce hanya zan amintar da sultane tafisu?.....ta wacce hanya ce zanyi abinda zai sake karkatar da hankalin sultane zuwa gareni?,na kuma sake samun yardarsa da aminci?"

"Ta hanyar amintaccensa ranki ya dade" Tafisu ta furta tana qanqantar dakai cikin girmamawa. Duban tafisu kawai takeyi cikin rashin fahimta kafin ta iya buda baki ta tambayeta.

"Me kike nufi tafisu?". Murmushi ta saki sannan ta dubi mammina.

"Qwaqwalwarki tafi tawa aiki nesa ba kusa a dukka shekarun da muka kwashe,amma bansan me yasa a yanzu komai nake yake sanyi sanyi ba......kinfi kowa sanin WAYE sultane wajen miqa soyayya da yarda gami da aminci ga duk wanda ya zaba da mallakawa hakan......kana sake samun aminci ne daga dan adam ta hanyar abinda ya amincewa......a yanzu ba wata hanya da zaki hana yaduwar labarin mutuwar auren akhnan......ba wata hanya da zaki hana rade radin isa ga kunnuwan sultane......amma ki tabbatar ke kika fara sanar masa.....kika hada masa kuma da mafitar komai,kinsan hikimar haka?" Kai mammina ta girgiza.

"Ban fahimta ba tafisu,mafita kuma ta ina?,maida auren almaz da akhnan dai kinsan abune daya haramta.....za'a shaidawa sultane haka,ko ba ta bakin kowa ba saita bakin malaman dake zagaye dashi,malaman ma irinsu wancan SHEIKH din days mallakawa dukkan yardarsa" Murmushi sosai me kama da dariya tafisu ta saki kafin ta dago ta kalli mammina.

"A idanun sultane din ke wankakkkiya ce......don bashi da wata masaniya ta kusa kota nesa akan cewa kece kika zabarwa akhnan miji.........zaki bayyana masa illar zaben da ya bari akhnan ta yiwa kanta na miji,zaki kuma kafa hujja da qoqarin da kika nuna na lallai yayi bincike akan almaz kafin daura auren......a nan kuma kin sake samun wata daman ta TARWATSA dukkan wani yarda kusanci da aminci da wancan SHEIKH din ya samu daga gareshi....nasan zaki tambayi ta wacce hanya ko?" Kai mammina ta jinjina da sauri,tana jin kamar tafisu na buda mata falle fallen littafi sosai a gabanta.

"Zakiyi ruwa da tsaki ta yadda sultane zai AURAWA akhnan malamin....." Wani abu mammina taji ya saukar mata kamar ana fusgarta,ta qanqance idanunta sosai tana duban tafisu.

"Kina hayyacinki kuwa tafisu?,ta yaya kike tsammanin akhnan zata auri malami?" Dariya kadan tafisu ta saki.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"A yanzu MAFITA ake nema.....ba yarda aminci ko gamsuwar akhnan nan ba.....duka daga baya zamuji da wannan" Ta fadi tana taqaitawa. Dubu bisa dubu mammina ta yarda da tafisu,tasha bata mafita da shawarwari kuma ko daya ba wanda ta taba faduwa a kansa.

"Ina jinki" Wannan tunanin ya sanya ta bawa tafisu daman ci gaba da magana.

"Zaku nunawa sultane a yanzu akhnan ta kawo zabinta,zabinta dinnan kuma bai haifar da d'a me ido ba,saboda haka ba wanda ya cancanci ma sultane ya sake bawa akhnan din sai amintaccensa wato malamin nan.....kinga a nan zaki sake haske a idanun sultane......zaki sake fari a idanunsa,kimarki zata dagu fiye da yadda kike tunani". Sosai mammina ke gyada kanta tana jin gamsuwa da gabar farko na bayanan tafisu.

"Gaba ta biyu kuma wannan wani sirrintaccen aiki ne.....kinsan ba wanda yakai malama dake zaune basa aikin komai sai karantaswa son banza?"

"Qwarai kuwa" Mammina ta amsawa tafisu kai tsaye saboda tuna wani yanki na rayuwarta na baya,mijinta na farko a rayuwarta. Kai tafisu ta jinjina.

"Wannan shine dalilin da ya sanya nace miki ki zabeshi a matsayin wanda zai auri AKHNAN.......bisa sharadai da tarin dukiya me yawan gaske da zaki alqawarta masa,ki fara mallaka masa wata,idan ya cika watannin da zai saki akhnan ya saketa.......ki cika masa dukiyarsa ki sallameshi......a nan kin samu mafita biyu" Dubanta kawai mammina keyi har yanxu tanason jin qarshen bayanan tafisu.
Chapter 68 · 0% Book details