Sashe 19
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Walqiyar data gilma me tsananin haske ita ta bata daman hango wadannan idanun.......wadannan idanun dai da suka hanata sukuni.....wadannan idanun dai dake sake bata qaimi cikin kowanne taqi da taku nason cimma mamallakinsa ta masa hukunci me tsauri.....wadannan idanun da ba abinda take hanga a cikinsu face kallon raini da qanqanci da suke mata,tun daga wancan ranar har zuwa yanzun da walqiyar shima ta bashi daman ganinta sosai,amma a nutse taga ya janye idanunsa daga dubanta kamar yaga wani abu mafi muni ko qyama.
Yanayin kallon daya jefa mata,ya kuma dauke idanunsa hankali kwance kaman baiga barnar da yayi mata ba ya tunzura zuciyarta sosai. Ba wani d'a namiji daya isa ya tsaya gabanta kamar haka koda baiyi mata barna irin haka ba,ballantana shi daya watsar da cherry din da bata taba daukar wani abu daga takun daya haura goma ba sai yau.
"Kamar dai baka gani......kamar dai makaho ne kai?" Ta fada cikin hasala tana laluben maganganun da zata fada masu zafi.
Tun daga wancan ranar da taga yadda sultane ke nan nan dashi wani kakkaifan haushi da tsana sauka sauka a ranta game dashi,daga sanda ta fahimci da gaske sultane ya bashi matsayin da nata ne ita kadai ta sake jin bata da sauran ABOKIN ADAWA da yayi saura duk duniya saishi.
Da gaske tana da kishin a dauki son da ake mata ko kalar kulawar da ake mata a bawa wani. Tsarinta ne haka,ta taso ta tarar komai nata ne.....komai ita daya akewa......ita kadai ake saurara......so ba zata juri hada komai da kowa ba.....koda kuwa falaak ce......bata lamunta ta tsaya matsayi d'aya daidai dana falaak din.
Tana ganin sam bai cancanci matsayin da sultane ya bashi ba......malami fa?,me karantarwa?.....me sultane zaici dashi?,me sultane zai qaru dashi?,banda shi din da zai sake zamewa sultane din kayan nauyi?.
Tana tunanin zaya daga kai yayi mata kallo na biyu ne.....wanda yake fatan hakan ta kasance ko don ta samu hanya ta biyu da zata sake fadin magana me zafi,wataqila ta rage haushin dakw zuciyarta,amma ga mamakinta bai ko yi niyyar karkatar da kallonsa a kanta ba......tamkar ba wani halitta me rai dake tsaye a wajen,sai ya tsugunna a nutse yasa hannunsa yana tattare cherry din guri daya.
Ta fahimci so yake ya tattare mata ya bata abinta ba tare da komai ya sake cewa ba......a yanzun ba wannan take buqata ba.......ko yaya tanaso ta gaya masa magana me zafi da zata damu ransa,don haka sai taja siririn tsaki.
"Koda ka tattarasu........kimata ta wuce naci abinda ya watse haka a qasa" Cak ya dakata daga tattarawar da yakeyi,ya sanya tafin hannunsa saman gwiwarsa ya miqe cikin tarin nutsuwarsa ba tare da ya daga kai ya dubi inda take tsaye ba.
A nutse ya fara takawa yana nufar balcony dinsa. Tarin mamaki ya kusa daskarar da ita. Wanne irin mutum ne shi?,dame yake taqama?,ya manta qarqashin alfarmar mahaifinta yake rayuwa?,ya manta wace ita?,matsayinta?,da girman ikon fada aji da take dashi da bazai mata yadda dukka sauran hadimai ke treating dinta ba?.
Inda daya daga cikin mutanen dake rayuwa cikin gidanne,wadanda suke qarqashin ikonsu da kulawarsu kamar yadda yake shi din a yanzu ya aika mata haka,lallai da yanzu yana durqushe cikin feshin ruwan yana hurwar ta yafe masa,amma sai gashi shi cikin nutsuwa ma yake barin gurin.
Wannan fusatacciyar zuciyartata ke gaya mata.
"Waye shi da zai aikata mata hakan kuma ya wuce lafiya salin alin?" Wannan fusatar ita ta sanyata takawa d'af d'af,ta kuma sha gabansa sanda yake shirin dora qafansa saman step din da zai shiga balcony dinsa.
Da dukkanin blue eyes dinta take kallonsa da wani irin kwantaccen fushi. Tana son bashi assignment da har ya gama rayuwarsa cikin gidan bazai gama dashi ba.......idan har girman kai yakeji tanason ta yage wannan rigar girman kan. Ba jiya ko shekaran jiya ba......ta hangi wani tasiri na izza tattare da dabi'arsa,wanda take ganin baikai ace akwai wannan cikin jininsa ba,a matsayinsa na malamin da baisan komai ba sai karantarwa. Qasqantar da kai ne kawai ya kamaceshi ga masu mulki da sarauta irinsu,bawai nuna izzar da sam bai mallaketa ba,baibi hanyarta ba,baima san ina muhallinta da zai ajiyeta cikin qualities dinsa yake ba.
Tsakiyar idanunta yake kalla da kyau,duk da qarancin hasken dake wajen amma bai hanashi gano zallar girman kai da tsiwar dake dawainiya da ita ba. Walqiyar da aka sakeyi mai madaidaicin haske ita ta sake haska masa fuskarta sosai. Kwantacciyar sumarta data sauka har gadon bayanta da kuma kafadunta ta bayyana sosai saman zagayayyar fuskarta dake da wani irin sirrintaccen kyau me wani irin sanyi. Mayafin dake saman kan nata ya koma rabi saboda santsin gashin da kuma yadda iska ke kadashi kadan kadan.
Idanunsa ya zare daga kanta da wani irin mutuwar dukka gabbansa yana maida dubansa gefe daya. Tsaiwarta a gurin wani abu ne da zai iya masa tasirin da baya buqata,dukan da ruwa ya yiwa jikinta ya sanya doguwar rigar silk material din mannewa a jikinta sosai,ta kuma fidda shape na gurare da yawa a jikinta,shin ita bata ganin hakane?. Yaji tambayar tazo kansa.
Idanunsa ya lumshe sannan ya budesu,yana jin yadda feshin ruwa ke sauka saman fuskar tasa,yana kuma jin yadda taci gaba da qananun mitoci wanda ya cakuda da sautin ruwan dake sauka saman roofing din veranda din. Siririyar muryar dake da wani irin taushi......taushin da bai hana bayyanar tsiwarta qarara ta cikin maganganunta ba.
Dare ne......wanda saukar ruwan sama kan iya hana kowanne mutum dake nesa dasu qarar kowanne sauti komai girman sautin. Tana tsaye gaba kadan dashi da tazarar da bame yawa ba......duk wanda ya gansu a haka a irin wannan lokacin a kuma irin yanayin da ita take ciki ba shakka ba abinda bazai iya ayyanawa ba a ransa.
Baya son ya sake aza idanunsa a kanta,don ya tabbatar duk yadda zaiyi don ya kaucewa kallon guraren da bai halatta ya gani din ba abune me wahalan gaske,don kusan rabin sumarta a bude yake.
"Zaki iya matsawa kiban guri na wuce princess?" Ya fada calmly ba tare daya waiwayo ko ya aza idanunsa a kanta ba,saidai kuma can qasan ransa fushinsa ne yake motsawa kadan kadan,wanda bayason yayi wani motsi da zai tasirantu a kanta. Fushinsa na yadda ta tsare masa hanyar shiga sassansa,duk da akwai sauran space da zai iya wucewa din,saidai yayi qanqantar da zai wahala ya wuce lafiya ba tare da sun gogi jikin juna ba.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Ranta ya sake baci,ta sake zubawa gefan fuskarsa da kwantaccen qasumbarsa me tsari ta sake kwanciya saboda jiqewa da tayi idanu. Abinda take magana akai daban?,abinda yake fadi daban?,damuwarsa kawai ya wuce?.....tana magana dashi yana dauke idanu zuwa wani sashen na daban?.
Ko waye ko kuma meye sultane ya daukeshi wannan karon sai ta sanya an hukunta matashi,irin hukuncin da nan gaba bazai sake mararin koda hada hanya da ita ba.
Daidai sanda ta bude qaramin bakinta daidai lokacin wata irin walqiya me kashe idanu da wata irin tsawa gauraye ta karade sararin samaniya. Idanunsa ya lumshe yana motsa labbansa a hankali da addu'ar tsawa da ma'aiki ya koyar
"Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra'adi bi hamdihi.....walmala'ikatu min kifatih". A hankali ya bude idanunsa suka kuma sauka a kanta. Tana tsugunne a qasa ta cure guri daya. Ko ina na jikinta rawa yake,wanda yake bayyanar da tsananij tsoro a tattare da ita me yawan gaske.
Idonsa ya sake daukewa ya maida gefe,sai ya qara sautinsa yana maimaita addu'ar a fili daidai da yadda zata iya ji.
Duk da muradinsa shine ya wuceta abinsa kafin bacin ransa yakai ga bayyana......amma fuskar sultane yake iya hanga a gurin......kebantattun maganganunsa da sukayi......maganganun da suka tilasta masa aminta da alfarmar da sultane ya nema a tare dashi bai ko iya musa masa ba.
"Ko yaya idan akhnan na cikin hadari.....nakanji wani abu a jikina,nauye nauye sunyimin yawa.......bazata samu kulawata yadda ya kamata ba,don Allah ko yaya koda sau daya ka zama me kula da lamarin daya shafeta daidai yadda zaka iya,ba don kowa ba saidon GIRMAN ZATIN ALLAH" Sautukan dake dawo masa kenan a yanzu.....yana kuma sake ji da ganin yadda dan qaramin amincin dake tsakaninsa da sultane keson takurashi.
A tsanake ya juya a hankali yana nufar sashen qofar balcony din nata bayan wasu sakanni. Maqullansa ya zaro,cikin hikima irinta qwarrarun jami'ai da suka goge ta fannin aikin tsaro binciken sirri dana qwaqwafi ya bude qofar. Takowa yayi a nutse yana dawowa nashi qofar,tsugunnawarta ya bashi space sosai da ya samu ya wuce a tsanake,ya isa qofar balcony din nasa ya zura key ya bude qofar ya turata sanna ya sanya qafarsa a hankali bakinsa dauke da addu'ar shiga gida.
Da sauri ta daga kanta sannan ta waiwaya zuwa bayanta,daidai sanda yake maida qofarsa ya kulle abinsa.
Zumbur ta miqe tana waiwayen hagunta da damanta. A yanzun ba kowa a gurin,a yanzun ita daya ce sai ruwan saman dake sauka,wani tsoro ya sake mamayarta,ba shiri ta fara tattakawa da sassarfa tana nufar qofartata wanda ta sameta a bude,da hanzari ta shige sannan ta maidata ta rufe tana maida numfashi a jejjere kamar wadda tayi tseren gudu.
Sai data kusa kashe a qalla mintuna goma sannan numfashinta ya daidaita,ta saka hannu ta zare yalolon mayafinta daya jiqe ta yar a gefe,ya kuma sauka daidai kwandon Cherry dinta dake dauke da Cherry din. Wani tsaki taja baqinciki yana taso mata.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 18*
_________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
__________________________
Yanayin kallon daya jefa mata,ya kuma dauke idanunsa hankali kwance kaman baiga barnar da yayi mata ba ya tunzura zuciyarta sosai. Ba wani d'a namiji daya isa ya tsaya gabanta kamar haka koda baiyi mata barna irin haka ba,ballantana shi daya watsar da cherry din da bata taba daukar wani abu daga takun daya haura goma ba sai yau.
"Kamar dai baka gani......kamar dai makaho ne kai?" Ta fada cikin hasala tana laluben maganganun da zata fada masu zafi.
Tun daga wancan ranar da taga yadda sultane ke nan nan dashi wani kakkaifan haushi da tsana sauka sauka a ranta game dashi,daga sanda ta fahimci da gaske sultane ya bashi matsayin da nata ne ita kadai ta sake jin bata da sauran ABOKIN ADAWA da yayi saura duk duniya saishi.
Da gaske tana da kishin a dauki son da ake mata ko kalar kulawar da ake mata a bawa wani. Tsarinta ne haka,ta taso ta tarar komai nata ne.....komai ita daya akewa......ita kadai ake saurara......so ba zata juri hada komai da kowa ba.....koda kuwa falaak ce......bata lamunta ta tsaya matsayi d'aya daidai dana falaak din.
Tana ganin sam bai cancanci matsayin da sultane ya bashi ba......malami fa?,me karantarwa?.....me sultane zaici dashi?,me sultane zai qaru dashi?,banda shi din da zai sake zamewa sultane din kayan nauyi?.
Tana tunanin zaya daga kai yayi mata kallo na biyu ne.....wanda yake fatan hakan ta kasance ko don ta samu hanya ta biyu da zata sake fadin magana me zafi,wataqila ta rage haushin dakw zuciyarta,amma ga mamakinta bai ko yi niyyar karkatar da kallonsa a kanta ba......tamkar ba wani halitta me rai dake tsaye a wajen,sai ya tsugunna a nutse yasa hannunsa yana tattare cherry din guri daya.
Ta fahimci so yake ya tattare mata ya bata abinta ba tare da komai ya sake cewa ba......a yanzun ba wannan take buqata ba.......ko yaya tanaso ta gaya masa magana me zafi da zata damu ransa,don haka sai taja siririn tsaki.
"Koda ka tattarasu........kimata ta wuce naci abinda ya watse haka a qasa" Cak ya dakata daga tattarawar da yakeyi,ya sanya tafin hannunsa saman gwiwarsa ya miqe cikin tarin nutsuwarsa ba tare da ya daga kai ya dubi inda take tsaye ba.
A nutse ya fara takawa yana nufar balcony dinsa. Tarin mamaki ya kusa daskarar da ita. Wanne irin mutum ne shi?,dame yake taqama?,ya manta qarqashin alfarmar mahaifinta yake rayuwa?,ya manta wace ita?,matsayinta?,da girman ikon fada aji da take dashi da bazai mata yadda dukka sauran hadimai ke treating dinta ba?.
Inda daya daga cikin mutanen dake rayuwa cikin gidanne,wadanda suke qarqashin ikonsu da kulawarsu kamar yadda yake shi din a yanzu ya aika mata haka,lallai da yanzu yana durqushe cikin feshin ruwan yana hurwar ta yafe masa,amma sai gashi shi cikin nutsuwa ma yake barin gurin.
Wannan fusatacciyar zuciyartata ke gaya mata.
"Waye shi da zai aikata mata hakan kuma ya wuce lafiya salin alin?" Wannan fusatar ita ta sanyata takawa d'af d'af,ta kuma sha gabansa sanda yake shirin dora qafansa saman step din da zai shiga balcony dinsa.
Da dukkanin blue eyes dinta take kallonsa da wani irin kwantaccen fushi. Tana son bashi assignment da har ya gama rayuwarsa cikin gidan bazai gama dashi ba.......idan har girman kai yakeji tanason ta yage wannan rigar girman kan. Ba jiya ko shekaran jiya ba......ta hangi wani tasiri na izza tattare da dabi'arsa,wanda take ganin baikai ace akwai wannan cikin jininsa ba,a matsayinsa na malamin da baisan komai ba sai karantarwa. Qasqantar da kai ne kawai ya kamaceshi ga masu mulki da sarauta irinsu,bawai nuna izzar da sam bai mallaketa ba,baibi hanyarta ba,baima san ina muhallinta da zai ajiyeta cikin qualities dinsa yake ba.
Tsakiyar idanunta yake kalla da kyau,duk da qarancin hasken dake wajen amma bai hanashi gano zallar girman kai da tsiwar dake dawainiya da ita ba. Walqiyar da aka sakeyi mai madaidaicin haske ita ta sake haska masa fuskarta sosai. Kwantacciyar sumarta data sauka har gadon bayanta da kuma kafadunta ta bayyana sosai saman zagayayyar fuskarta dake da wani irin sirrintaccen kyau me wani irin sanyi. Mayafin dake saman kan nata ya koma rabi saboda santsin gashin da kuma yadda iska ke kadashi kadan kadan.
Idanunsa ya zare daga kanta da wani irin mutuwar dukka gabbansa yana maida dubansa gefe daya. Tsaiwarta a gurin wani abu ne da zai iya masa tasirin da baya buqata,dukan da ruwa ya yiwa jikinta ya sanya doguwar rigar silk material din mannewa a jikinta sosai,ta kuma fidda shape na gurare da yawa a jikinta,shin ita bata ganin hakane?. Yaji tambayar tazo kansa.
Idanunsa ya lumshe sannan ya budesu,yana jin yadda feshin ruwa ke sauka saman fuskar tasa,yana kuma jin yadda taci gaba da qananun mitoci wanda ya cakuda da sautin ruwan dake sauka saman roofing din veranda din. Siririyar muryar dake da wani irin taushi......taushin da bai hana bayyanar tsiwarta qarara ta cikin maganganunta ba.
Dare ne......wanda saukar ruwan sama kan iya hana kowanne mutum dake nesa dasu qarar kowanne sauti komai girman sautin. Tana tsaye gaba kadan dashi da tazarar da bame yawa ba......duk wanda ya gansu a haka a irin wannan lokacin a kuma irin yanayin da ita take ciki ba shakka ba abinda bazai iya ayyanawa ba a ransa.
Baya son ya sake aza idanunsa a kanta,don ya tabbatar duk yadda zaiyi don ya kaucewa kallon guraren da bai halatta ya gani din ba abune me wahalan gaske,don kusan rabin sumarta a bude yake.
"Zaki iya matsawa kiban guri na wuce princess?" Ya fada calmly ba tare daya waiwayo ko ya aza idanunsa a kanta ba,saidai kuma can qasan ransa fushinsa ne yake motsawa kadan kadan,wanda bayason yayi wani motsi da zai tasirantu a kanta. Fushinsa na yadda ta tsare masa hanyar shiga sassansa,duk da akwai sauran space da zai iya wucewa din,saidai yayi qanqantar da zai wahala ya wuce lafiya ba tare da sun gogi jikin juna ba.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Ranta ya sake baci,ta sake zubawa gefan fuskarsa da kwantaccen qasumbarsa me tsari ta sake kwanciya saboda jiqewa da tayi idanu. Abinda take magana akai daban?,abinda yake fadi daban?,damuwarsa kawai ya wuce?.....tana magana dashi yana dauke idanu zuwa wani sashen na daban?.
Ko waye ko kuma meye sultane ya daukeshi wannan karon sai ta sanya an hukunta matashi,irin hukuncin da nan gaba bazai sake mararin koda hada hanya da ita ba.
Daidai sanda ta bude qaramin bakinta daidai lokacin wata irin walqiya me kashe idanu da wata irin tsawa gauraye ta karade sararin samaniya. Idanunsa ya lumshe yana motsa labbansa a hankali da addu'ar tsawa da ma'aiki ya koyar
"Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra'adi bi hamdihi.....walmala'ikatu min kifatih". A hankali ya bude idanunsa suka kuma sauka a kanta. Tana tsugunne a qasa ta cure guri daya. Ko ina na jikinta rawa yake,wanda yake bayyanar da tsananij tsoro a tattare da ita me yawan gaske.
Idonsa ya sake daukewa ya maida gefe,sai ya qara sautinsa yana maimaita addu'ar a fili daidai da yadda zata iya ji.
Duk da muradinsa shine ya wuceta abinsa kafin bacin ransa yakai ga bayyana......amma fuskar sultane yake iya hanga a gurin......kebantattun maganganunsa da sukayi......maganganun da suka tilasta masa aminta da alfarmar da sultane ya nema a tare dashi bai ko iya musa masa ba.
"Ko yaya idan akhnan na cikin hadari.....nakanji wani abu a jikina,nauye nauye sunyimin yawa.......bazata samu kulawata yadda ya kamata ba,don Allah ko yaya koda sau daya ka zama me kula da lamarin daya shafeta daidai yadda zaka iya,ba don kowa ba saidon GIRMAN ZATIN ALLAH" Sautukan dake dawo masa kenan a yanzu.....yana kuma sake ji da ganin yadda dan qaramin amincin dake tsakaninsa da sultane keson takurashi.
A tsanake ya juya a hankali yana nufar sashen qofar balcony din nata bayan wasu sakanni. Maqullansa ya zaro,cikin hikima irinta qwarrarun jami'ai da suka goge ta fannin aikin tsaro binciken sirri dana qwaqwafi ya bude qofar. Takowa yayi a nutse yana dawowa nashi qofar,tsugunnawarta ya bashi space sosai da ya samu ya wuce a tsanake,ya isa qofar balcony din nasa ya zura key ya bude qofar ya turata sanna ya sanya qafarsa a hankali bakinsa dauke da addu'ar shiga gida.
Da sauri ta daga kanta sannan ta waiwaya zuwa bayanta,daidai sanda yake maida qofarsa ya kulle abinsa.
Zumbur ta miqe tana waiwayen hagunta da damanta. A yanzun ba kowa a gurin,a yanzun ita daya ce sai ruwan saman dake sauka,wani tsoro ya sake mamayarta,ba shiri ta fara tattakawa da sassarfa tana nufar qofartata wanda ta sameta a bude,da hanzari ta shige sannan ta maidata ta rufe tana maida numfashi a jejjere kamar wadda tayi tseren gudu.
Sai data kusa kashe a qalla mintuna goma sannan numfashinta ya daidaita,ta saka hannu ta zare yalolon mayafinta daya jiqe ta yar a gefe,ya kuma sauka daidai kwandon Cherry dinta dake dauke da Cherry din. Wani tsaki taja baqinciki yana taso mata.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 18*
_________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
__________________________