Sashe 17
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"La....la....la,wanne irin abun kunya kike shirin bari?,hawayen sarauniyar agadez haka a fili a araha?" Mammina ta fada tana goge mata fuskarta dake kwance saman kafadarta. Wani qwarin gwiwa taji yana hauro mata kamar yadda ta saba ji.......tabbas mammina itace qwarin gwiwarta. Duk wani pattern da take rayuwa akai tsarin mammina ne. Ta nuna darajar matsayin da Allah ya bata,ta nuna mata girman da take dashi......ta karantar da ita cewa ITA TA MUSAMMAN CE.....tana da banbanci da sauran yara......tana da banbanci da sauran duk wani halitta dake rayuwa cikin masarautar. Wannan motsa mata izzar tata da tayi ya sanya ta hadiye kukanta,ta kuma bi mammina wadda ke riqe da hannunta tana takawa da ita zuwa wani kebantaccen guri dake da tarin kima a gurin mammina dama duk mutumin da zata gana dashi a gurin.
Hannayensa zube cikin aljihun wandonsa yana nazartar gurin cike da tarin mamaki. Yana da kusan dukkan map na gidan amma bai taba lura da wanzuwar gurin ba.
A yanzun da yake nazartar gurin da idanunsa da zaka dauka a rufe suke.....yana iya hangen yadda gurin zai iya linking nasa da wancan kebantaccen dakin ajiyar da ya zama guri na biyu da yake buri da muradin shiga ya duba wasu abubuwa da jikinsa ya jima yana bashi akwai bayanan da zai iya buqata cikin gurin.
Lokutan da agogo ke bashi yakeso yayi amfani dasu a tsakanin lokutan,ya tabbatar yana cikin lokutan da dan bibiyarsa ba lallai ya sake kasancewa dashi ba har zuwa awa daya a gaba. Zai iya ci gaba da kasancewa dashi daga awa dayar har zuwa awannin biyun da zai samu tabbacin ya kwanta......daga nan kuma zai dora aikinsa ne bayan ya tabbatar asubahi tayi,wadannan sune hasashen jadawalin lokutan daya tabbatar zaiyi amfani dasu gurin bibiyarsa. Bazai dawo nan kusa ba saboda yayi motsin da ya fuskanci yaja hankalinsa har ya miqe ya maida qofarsa ya rufe A ZATONSA baisan cewa TARKO bane kawai haisam din ya D'ANA MASA don tabbatar da cewa sun fara aiki da umarninta?.
Motsin sawayen da yaji ya sanyashi sake nutsuwa da kyau......muryarta kuma ta zama abu na farko daya fara shiga kunnensa.
"Kin taba ganin inda uwa ta iya qyale yarinyarta tasha wahala?.....kin taba ganin inda d'iya tayi fushi da uwarta?". Ya haddace muryarta da kyau,sautinta yana da banbamci da sauran sautukan da yake ji cikin masarautar,duk da yadda yake qure qoqarinta gurin daidaita harshenta dana kowa su saje a ma'auni guda daya......ma'aunin da sai kana da qwaqwalwa da fikira irin tasa zaka iya sansani banbance banbance a tsakanin abinda aka gauraya guri daya.
Ta ganshi a ranar nan,a yanzun kuma bazai zama lokacin daya dace ta sake ganinsa ba,don bai shirya ajiye zargi ko kokwanto a kansa a zuciyar kowa ba,don haka ya taka a hankali ya shiga tsakanin bishiyar dogayen yaro masu tsahon gaske guda biyu dake gurin.
Wayarsa ya zaro a hankali jin alamun shigowar saqo,ya rage hasken sosai yana duba saqon daya shigo masa. Bobbo muhammad dawud ne,ya sani akwai tattaunawa da zasuyi,duk da ta chart ne ta kebantacciyar manhajar da sukanyi musayar tattaunawa,amma bai dauka zai nemeshi haka da wuri ba. Tsaiwarsa ya gyara yana maida hankalinsa kan wayarsa,ya soma maida messages din bobbo din,duk da ba hakan yaso ba,yaso yana daki a nutse,amma idan yace zaya jira kaucewar kowa baisan yawan tsahon lokacin da zai dauka ba.
"Zauna a nan ki saurareni da kyau" Mammina ta fada tanawa akhnan nuni da daya daga cikin kujerun dake ajiye a gurin.
A nutse ta qarasa ta zauna,sannan mammina din ta taka itama zuwa kujerar dake daura da ita.
Dukkanin hannuwan akhnan ta kama ta aza saman cinyarta,ta sanya idanunta sosai cikin nata.
"Inaso ki saurareni sosai da kunnen basira......inaso ki bani duk wani hankali naki da kike dashi" Kai ta gyada a hankali,batajin akwai wani sauran abu da mammina zata buqata daga gareta ta kasa yi mata shi.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/7, 19:49] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 16*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
__________________________
"Kisa a ranki ni din tamkar mahaifiya nake a gurinki ba UWA ba.......ba wani tsanani da zaizo da zan iya juya miki baya.....to amma dole wataran kaza take taka d'anta badon bata sonshi ba.....aah,saidai kawai ta bashi wata tarbiyya.....idan nace a komai na rayuwarki zanci gaba da zaqewa.....zanci gaba da kasancewa a gaba gaba hakan zai iya zame mana matsala......" Takai qarshen maganar tana sauke numfashi.
"Duk wank hukunci naki da zabi naki ina tare dashi biftu......duk wani kalan abu da zai saka rayuwarki a nishadi ina tare dashi biftu.......zakiyi aure kamar yadda sultane yake da buqata.....zaki aure amma zaki auri mijin da zai zamana qarqashin juyawarki umarninki da kuma haninki......zaki auri mijin da kece zaki shirya ki kuma tsara kalar rayuwar da kike buri da mafarki......mijin da bai isa ya sakaki ko ya hanaki ba,zai kasance qarqashin sarrafawarki". Idanu akhnan ta lumshe tana sake budesu lokaci guda hade da wani irin lafiyayyen murmushi.
Lallai ba shakka duk wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi.......duk wanda ya girmeka ya girmeka har abada. Abadan duk duniya bata da wani masoyi daya d'ara mammina.....a wannan gabar har cikin tsakiyar zuciyarta da ruhinta tana jin cewa koda sultane SAI YA JIRA a soyayyar mammina a gareta......ta sake gasgata cewa idan ba MAMMINA babu ita AKHNAN.....tabbas ba zata taba kai labari ba idan ba mammina na gefanta ba.
To wai me yasa tun baya ita batayi irin wannan tunanin ba?......namijin da zai zama miji a idanun sultane kawai amma cikakken HOTO a idanunta da bazai hanata aiwatar da komai da ta tsara cikin kundin rayuwarta ba?.
"Kina jina?" Muryar mammina ta dawo da ita daga tunanin data fara nisan zango a cikinsa. Kai ta gyada mata tana sauke blue eyes dinta da rashin wadataccen haske ya sake sanyawa ya zama wani me qyalli da daukan idanu.
Sama ta daga kanta mammina din,saboda digar yayyafi da taji cikin jikinta gami da haskawar walqiya,alamu ke nuna ruwan saman farko zai sauka kenan da yardar me duka yau a qasar agadez. Idanunta ta mayar kan akhnan,wadda yayyafin ruwan bai sanyata ta qifta idonta daga kan mammina ba.
"Ki nemo mijin ki kawo......zan tsaya don tabbatuwar dukka wadannan sharud......"
"Mammina manaaaa......" Ta furta da wani sassanyan yanayinta daya fusgi hankalinsa daga inda yake tsaye,inda hankalinsa yayi nisa sa maganganunsu ya tura dukka hankalinsa da nutsuwarsa zuwa ga bobbo muhammad dawud.
Kyawawan idanunsa ya daga yana kallon gabanshi,duk da bai iya ganin komai sai alamunsu a mazaunin dake gaba kadan dashi. Tafin hannunsa ya sanya yana goge yayyafin ruwan daya sauka saman screen din wayar nasa yana kuma qoqarin hanashi ci gaba da sarrafa wayar saboda yadda yake dan qara yawa.
Baisan me yasa sautin nata ya fusgi hankalinsa ba.......sai ya sanya tafin hannun nasa yana yiwa wayar rumfa da xummar rage saukan ruwan saman screen din,saidai a wannan karon kunnuwansa sun gaza kaucewa daga tsintar maganganunsu.
"Da gaske nake mammina......na baki wuqa da nama......ki kawo duk wanda kikaga ya miki.......fatana na rayu cikin 'yanci,irin 'yancin da kowacce mace maras igiyar aure a kanta zata rayu dashi......ban taba sha'awar soyayya ko tarayya da kowanne namiji ba.....don har yanzu bana zaton an halicci irin ajina daya dace da MARTABATA".
Har cikin jinin dake harbawa a jikinsa yakejin zancansu bai shefeshi ba,burinsa su matsa shima ya wuce ciki kafin ruwan yakai ga bata masa waya ko katse muhimmiyar maganar da yakeyi da bobbo......amma a wannan gurbin baisan sanda yaja wani siririn tsaki ba.
Haka kawai yakejin wani bacin rai kadan kadan yana tasiri a ransa. Banda girman kan dake dawainiya da ita yana tunanin akwai tasirin jahilci. Wacce irin uwar goyo ya rabauta da ita wadda ke goyon bayan duk wani shirin shirme nata maras ma'ana?.
"Zai kasance ni na zaboshi......amma ki koyawa kanki nunawa duniya cewa shine zabinki......idan hakan bata faru ba,bana tunanin zan sake zama cikin matsalolinki irin wannan har abada". Kai ta girgiza sanda ruwan ya fara damunta saboda yanayin saukarsa daya qara yawa.
"Komai zai kasance kamar yadda kika buqata mammina ta......na gode da kasancewarki cikin rayuwata" Ta furta sanda suka miqe a tare,ta kuma matsa tana rungume mammina din sosai da tarin soyayyarta danqare cikin zuciyarta.
A hankali mammina din ta zareta daga jikinta tana sakar mata murmushi.
"Nan da kwana uku kawai zan gabatar miki da duk wanda nake ganin zaibi umarninki ne kawai".
" Ba buqatar hakan......koda zamu qare zamanmu ban ganshi ba bana buqata mammina.......buqatata daya na amintar da sultane.....na fita daga fushinsa"
"Idan har kikayi hakan kowa ma zai iya fahimtar komai" Amsar data bawa akhnan kenan ta soma takawa don barin gurin duba da yadda ruwan yayi qarfi lokaci daya.
Idanunsa ya maida ya lumshe yana jin yadda bishiyar ta gaza rufe saukar ruwan duka cikin kansa,duk da ta tare wani kaso da bai taka kara ya karya ba.
Maganganunsu na qarshe ne suka maimaita kansu cikin kansa,yayin da zuciyarsa ta yunquro da wani qaqqarfan yunquri tana gaya masa.
"Not your business haisam......not your business". Kansa ya gyada a hankali,har cikin zuciyarsa yana jin hakane,zuciyarsa gasiya ta gaya masa,wani sashen kuma na zuciyar tasa tana cike da wani irin yaqini da zargi me qarfi akan MAMMINA.
Yanajin tana sake cika dukkann wasu sharuddan zargi da zato me qarfin gaske a tattare da ita......yana jin a duniya a yanzu itace bakin zaren ZATONSU ta farko.......a jikinsa yake jin akwai wani abu binne.
Hannayensa zube cikin aljihun wandonsa yana nazartar gurin cike da tarin mamaki. Yana da kusan dukkan map na gidan amma bai taba lura da wanzuwar gurin ba.
A yanzun da yake nazartar gurin da idanunsa da zaka dauka a rufe suke.....yana iya hangen yadda gurin zai iya linking nasa da wancan kebantaccen dakin ajiyar da ya zama guri na biyu da yake buri da muradin shiga ya duba wasu abubuwa da jikinsa ya jima yana bashi akwai bayanan da zai iya buqata cikin gurin.
Lokutan da agogo ke bashi yakeso yayi amfani dasu a tsakanin lokutan,ya tabbatar yana cikin lokutan da dan bibiyarsa ba lallai ya sake kasancewa dashi ba har zuwa awa daya a gaba. Zai iya ci gaba da kasancewa dashi daga awa dayar har zuwa awannin biyun da zai samu tabbacin ya kwanta......daga nan kuma zai dora aikinsa ne bayan ya tabbatar asubahi tayi,wadannan sune hasashen jadawalin lokutan daya tabbatar zaiyi amfani dasu gurin bibiyarsa. Bazai dawo nan kusa ba saboda yayi motsin da ya fuskanci yaja hankalinsa har ya miqe ya maida qofarsa ya rufe A ZATONSA baisan cewa TARKO bane kawai haisam din ya D'ANA MASA don tabbatar da cewa sun fara aiki da umarninta?.
Motsin sawayen da yaji ya sanyashi sake nutsuwa da kyau......muryarta kuma ta zama abu na farko daya fara shiga kunnensa.
"Kin taba ganin inda uwa ta iya qyale yarinyarta tasha wahala?.....kin taba ganin inda d'iya tayi fushi da uwarta?". Ya haddace muryarta da kyau,sautinta yana da banbamci da sauran sautukan da yake ji cikin masarautar,duk da yadda yake qure qoqarinta gurin daidaita harshenta dana kowa su saje a ma'auni guda daya......ma'aunin da sai kana da qwaqwalwa da fikira irin tasa zaka iya sansani banbance banbance a tsakanin abinda aka gauraya guri daya.
Ta ganshi a ranar nan,a yanzun kuma bazai zama lokacin daya dace ta sake ganinsa ba,don bai shirya ajiye zargi ko kokwanto a kansa a zuciyar kowa ba,don haka ya taka a hankali ya shiga tsakanin bishiyar dogayen yaro masu tsahon gaske guda biyu dake gurin.
Wayarsa ya zaro a hankali jin alamun shigowar saqo,ya rage hasken sosai yana duba saqon daya shigo masa. Bobbo muhammad dawud ne,ya sani akwai tattaunawa da zasuyi,duk da ta chart ne ta kebantacciyar manhajar da sukanyi musayar tattaunawa,amma bai dauka zai nemeshi haka da wuri ba. Tsaiwarsa ya gyara yana maida hankalinsa kan wayarsa,ya soma maida messages din bobbo din,duk da ba hakan yaso ba,yaso yana daki a nutse,amma idan yace zaya jira kaucewar kowa baisan yawan tsahon lokacin da zai dauka ba.
"Zauna a nan ki saurareni da kyau" Mammina ta fada tanawa akhnan nuni da daya daga cikin kujerun dake ajiye a gurin.
A nutse ta qarasa ta zauna,sannan mammina din ta taka itama zuwa kujerar dake daura da ita.
Dukkanin hannuwan akhnan ta kama ta aza saman cinyarta,ta sanya idanunta sosai cikin nata.
"Inaso ki saurareni sosai da kunnen basira......inaso ki bani duk wani hankali naki da kike dashi" Kai ta gyada a hankali,batajin akwai wani sauran abu da mammina zata buqata daga gareta ta kasa yi mata shi.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/7, 19:49] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 16*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
__________________________
"Kisa a ranki ni din tamkar mahaifiya nake a gurinki ba UWA ba.......ba wani tsanani da zaizo da zan iya juya miki baya.....to amma dole wataran kaza take taka d'anta badon bata sonshi ba.....aah,saidai kawai ta bashi wata tarbiyya.....idan nace a komai na rayuwarki zanci gaba da zaqewa.....zanci gaba da kasancewa a gaba gaba hakan zai iya zame mana matsala......" Takai qarshen maganar tana sauke numfashi.
"Duk wank hukunci naki da zabi naki ina tare dashi biftu......duk wani kalan abu da zai saka rayuwarki a nishadi ina tare dashi biftu.......zakiyi aure kamar yadda sultane yake da buqata.....zaki aure amma zaki auri mijin da zai zamana qarqashin juyawarki umarninki da kuma haninki......zaki auri mijin da kece zaki shirya ki kuma tsara kalar rayuwar da kike buri da mafarki......mijin da bai isa ya sakaki ko ya hanaki ba,zai kasance qarqashin sarrafawarki". Idanu akhnan ta lumshe tana sake budesu lokaci guda hade da wani irin lafiyayyen murmushi.
Lallai ba shakka duk wanda ya rigaka kwana dole ya rigaka tashi.......duk wanda ya girmeka ya girmeka har abada. Abadan duk duniya bata da wani masoyi daya d'ara mammina.....a wannan gabar har cikin tsakiyar zuciyarta da ruhinta tana jin cewa koda sultane SAI YA JIRA a soyayyar mammina a gareta......ta sake gasgata cewa idan ba MAMMINA babu ita AKHNAN.....tabbas ba zata taba kai labari ba idan ba mammina na gefanta ba.
To wai me yasa tun baya ita batayi irin wannan tunanin ba?......namijin da zai zama miji a idanun sultane kawai amma cikakken HOTO a idanunta da bazai hanata aiwatar da komai da ta tsara cikin kundin rayuwarta ba?.
"Kina jina?" Muryar mammina ta dawo da ita daga tunanin data fara nisan zango a cikinsa. Kai ta gyada mata tana sauke blue eyes dinta da rashin wadataccen haske ya sake sanyawa ya zama wani me qyalli da daukan idanu.
Sama ta daga kanta mammina din,saboda digar yayyafi da taji cikin jikinta gami da haskawar walqiya,alamu ke nuna ruwan saman farko zai sauka kenan da yardar me duka yau a qasar agadez. Idanunta ta mayar kan akhnan,wadda yayyafin ruwan bai sanyata ta qifta idonta daga kan mammina ba.
"Ki nemo mijin ki kawo......zan tsaya don tabbatuwar dukka wadannan sharud......"
"Mammina manaaaa......" Ta furta da wani sassanyan yanayinta daya fusgi hankalinsa daga inda yake tsaye,inda hankalinsa yayi nisa sa maganganunsu ya tura dukka hankalinsa da nutsuwarsa zuwa ga bobbo muhammad dawud.
Kyawawan idanunsa ya daga yana kallon gabanshi,duk da bai iya ganin komai sai alamunsu a mazaunin dake gaba kadan dashi. Tafin hannunsa ya sanya yana goge yayyafin ruwan daya sauka saman screen din wayar nasa yana kuma qoqarin hanashi ci gaba da sarrafa wayar saboda yadda yake dan qara yawa.
Baisan me yasa sautin nata ya fusgi hankalinsa ba.......sai ya sanya tafin hannun nasa yana yiwa wayar rumfa da xummar rage saukan ruwan saman screen din,saidai a wannan karon kunnuwansa sun gaza kaucewa daga tsintar maganganunsu.
"Da gaske nake mammina......na baki wuqa da nama......ki kawo duk wanda kikaga ya miki.......fatana na rayu cikin 'yanci,irin 'yancin da kowacce mace maras igiyar aure a kanta zata rayu dashi......ban taba sha'awar soyayya ko tarayya da kowanne namiji ba.....don har yanzu bana zaton an halicci irin ajina daya dace da MARTABATA".
Har cikin jinin dake harbawa a jikinsa yakejin zancansu bai shefeshi ba,burinsa su matsa shima ya wuce ciki kafin ruwan yakai ga bata masa waya ko katse muhimmiyar maganar da yakeyi da bobbo......amma a wannan gurbin baisan sanda yaja wani siririn tsaki ba.
Haka kawai yakejin wani bacin rai kadan kadan yana tasiri a ransa. Banda girman kan dake dawainiya da ita yana tunanin akwai tasirin jahilci. Wacce irin uwar goyo ya rabauta da ita wadda ke goyon bayan duk wani shirin shirme nata maras ma'ana?.
"Zai kasance ni na zaboshi......amma ki koyawa kanki nunawa duniya cewa shine zabinki......idan hakan bata faru ba,bana tunanin zan sake zama cikin matsalolinki irin wannan har abada". Kai ta girgiza sanda ruwan ya fara damunta saboda yanayin saukarsa daya qara yawa.
"Komai zai kasance kamar yadda kika buqata mammina ta......na gode da kasancewarki cikin rayuwata" Ta furta sanda suka miqe a tare,ta kuma matsa tana rungume mammina din sosai da tarin soyayyarta danqare cikin zuciyarta.
A hankali mammina din ta zareta daga jikinta tana sakar mata murmushi.
"Nan da kwana uku kawai zan gabatar miki da duk wanda nake ganin zaibi umarninki ne kawai".
" Ba buqatar hakan......koda zamu qare zamanmu ban ganshi ba bana buqata mammina.......buqatata daya na amintar da sultane.....na fita daga fushinsa"
"Idan har kikayi hakan kowa ma zai iya fahimtar komai" Amsar data bawa akhnan kenan ta soma takawa don barin gurin duba da yadda ruwan yayi qarfi lokaci daya.
Idanunsa ya maida ya lumshe yana jin yadda bishiyar ta gaza rufe saukar ruwan duka cikin kansa,duk da ta tare wani kaso da bai taka kara ya karya ba.
Maganganunsu na qarshe ne suka maimaita kansu cikin kansa,yayin da zuciyarsa ta yunquro da wani qaqqarfan yunquri tana gaya masa.
"Not your business haisam......not your business". Kansa ya gyada a hankali,har cikin zuciyarsa yana jin hakane,zuciyarsa gasiya ta gaya masa,wani sashen kuma na zuciyar tasa tana cike da wani irin yaqini da zargi me qarfi akan MAMMINA.
Yanajin tana sake cika dukkann wasu sharuddan zargi da zato me qarfin gaske a tattare da ita......yana jin a duniya a yanzu itace bakin zaren ZATONSU ta farko.......a jikinsa yake jin akwai wani abu binne.