Sashe 47
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin matsanancin bugawa kawai zuciyarta takeyi,cike da wani irin matsanancin tsoro da bata taba jin irinsa ba. Ta fidda manyan blue eyes dinta tana duban bulama din da haisam ya watsar a gurin,saidai yana riqe da hannayensa da ya banqaresu ta baya,wanda azabar irin wannan riqon da haisam yayi masa ya sanyashi fidda wani irin nishi a wahalce.
Iyakar saninta da hadiman gidan gaba daya batasan bulama ba. Batasan wayeshi ba,batasan kuma wannan fuskar ba......me ya kawoshi nan?,cikin duhun da babu komai cikinsa sai hasken walqiya?,cikin duhun bishiyoyin da ba wanda zai iya labewa ciki sai wanda ke dauke da alama da tambari na rashin gaskiya?. Ba ita ba......hatta da maleek dake kallon komai daga nesa.......amma zama da haisam da dadewarsu tare ya sanya yake fahimtar lokutan da haisam din yake buqatar wanzuwa a guri shi kadai,don haka sai ya tsaya daga ness yana kallon komai. Da fari hankalinsa da nazarinsa gaba daya yana kan akhnan din. Ya cika da wani irin tarin mamakin yadda haisam yake iya hadiye maganganunta,ya sani,yana da wani irin kaifin hangen nesa da qoqarin hadiye bacin rai,saidai kuma sam sam baya daukan raini ko qanqani. Yanayin tsiwarta ya daure masa kai sosai,dukkan wannan izzar a yanzun da take magana da haisam din sai yaga ta kwaranye ta barta da iya tsiwar. Akwai wani abu da yake hanga daga can cikin dabi'unta da yake ganin zuwansa daidai da wani salon ra'ayi na haisam din.
JARUMTA......irin salon jarumtar nan ta babu gudu babu ja da baya......wani irin qarfin hali da TSAIWA saman ra'ayi,sai ya saki wani sassanyan murmushi,wanda suke murmushin nasa keda wuya ya hangi yadda haisam din ya motsa cikin wani irin zafin nama ya kuma finciko bulama din.
Abun ya matuqar zuwa masa a bazata da kuma bashi mamaki. Baiga wani alamun wanzuwar dan adam a gurin ba......ta yaya haisam din ya fahimci hakan?,bayan kuma da kwanyarsa ta tuna masa SHEIKH HAISAM din sai mamakinsa ya dinga raguwa,ya fara tunanin me mutumin yakeyi a tsakanin duhuwar gurin?.
Kamar baisan waye bulaman ba,kamar kuma baisan wanne aiki yakeyi ya banqare hannunsa ta baya da kyau,da wani irin yanayi me cike da zafi yake duban fuskar bulama din wadda ke shimfide a qasa.
"Bazan tsaya bata bakina ina tambayarka wa kake bibiya ko me kakeyi ba a nan gurin a irin wannan lokacin......kaman yadda bani da lokacin tsayawa tambayarka WAYR YA SANYAKA......Amma zan aikeka da saqo guda days ka shaidawa wanda ya sanyaka din cewa......ni muhammad ina me shaida masa,yana wasa ne da FARAR WUTA wadda cikin ruwan sanyi take qona dukkan wanda ya raina raina LAUNINTA". Sai ya saki hannuwan bulaman,wanda hakan ya bashi daman qarasa zubewa a qasa cikin wani irin matsanancin radadi da kafadunsa da gadon bayansa gaba suke masa,sannan ya yunqura da wani qaramin hanzarin da qarfin hali ne kawai ya tattara masa ragowar kuzarin,da wata irin sassarfa yake jan qafafunsa yana bacewa daga gurin.
Taku uku kawai yayi ya koma zuwa bakin qarfen data sameshi a gurin,ya kuma juya mata baya yana kafe gwiwar hannunsa jikin qarfen ya koma salon durqushen da yayi dazu yana ci gaba da duban tsirran da sukaci gaba da kadawa da sauri sosai saboda qaruwar iskar data ci gaba da kadawa gami da damshin ruwa daya fara sauka yaf yaf mara qarfi.
Idanu ta zubawa bayansa tana sake jin wani tsoro yana sake shigarta na wanzuwar shuru a gurin,bata ganin kowa sai shi da ita,don omar ma tun sanda yaga yanayin reaction din haisam ya matsa yana kutsawa zuwa kewayen gidan ko zai samu wani evidence motsi ko wani dake tare da bulama din.
Runtse idanunta tayi da qarfi daga duban faffadan bayansa da yabar mata saboda sririyar walqiyar data haska sararin samaniya,ta kuma nuna yawan hadarin da take dauke dashi. Tsoro me qarfi dake cakude da bacin rai taji yana shigarta. Nadamar rashin amsar tayin da yayi mata tun farko na tafiya taji yana ratsata. Me yasa bata tafi ba sanda taga wani abu me nauyi cikin qwayar idanunsa?,me yasa bata tafi ba a sanda yayi mata kallo na kai tsaye......kallon cikin qwayar idanunta.....bayan taso wani kallo ne da bai taba yi mata irinsa ba.
To amma duk haka ita din,GIMBIYA AKHNAN MUHAMMAD HAMMUD.....har rashin darajar da zai gwada mata yakai ya juya mata baya yana ci gaba da al'amuransa kamar baisan Allah yayi tsironta a gurin ba?. Yana qarqashin cin alfarma ta mahaifinta?,yana rayuwa cikin iko na mahaifinta?. Wayeshi?,banda ordinary mutum kamar kowa?......banda ordinary hadimi kaman sauran hadiman cikin gidan,wanda suke rayuwa cikin tattalin farincikinta.....kare dokokinta da iyakokinta,yau gata a tsaye a yashe......tamkar ba itace wannan gimbiyar da ganinta yake zama GAGARUMAR SA'A GA DUK MUTUMIN DA IDANIYARSA TA SAMU NASARAR GANINTA.
A cikin jikinsa yakejin tsaiwarta a gurin,saidai bayaso ya waiwaya gareta harta kalli irin nasa fushin. Yana jin tsaiwarta har cikin b'argonsa,bai kuma san abinda ya hanashi tafiya yabar gurin ba,saidai wani sashe na zuciyarsa yana nanata masa MARTABAR SULTANE ce ta jawo haka.
A duk sanda zai kwanta yana jin sauti da kuma maimaicin sautin sultane a maganarsu ta qarshe cikin airport.
"Dukkan masarauta......da dukkan wanda ke cikin ta na baka amanarsa......idan nace kowa da komai ciki harda AKHNAN. marainiya ce data taso batasan dadin mahaifiya ba,duk da ta shekara hudu da ita,amma kona shekara hudunma batasan dadin safeena ba,saboda ciwon hauka da safeena tayi daga randa akhnan tayi kwana arba'in a duniya.......safeena batayin cikakken wata uku da lafiya,saidai kuma a wata ukun duk sanda take a daidaita bata bari kowa yayi hidima ga biftu,kamar tasan tafiya zatayi ta barta,kamar tasan tafiyar bame nisa bace.
Yana iya hangen qwayar idanun sultane a sanda yake masa maganar,yana iya ganin raunin dake tattare da sultane din ta cikin qwayar idanun nasa,raunin dake gaya masa wannan feelings din bame sauqi bane......me tsananin nauyi ne,nauyin daya gaza ture yaringar daga zuciyarsa,duk da girma da adadin kura kurenta a tare dashi,daci gaba da bijirewa zuwa ga umarninsa.
Damqe qarfen yayi da kyau yana jin yadda ruwan ke qara yawa. Yanason ya waiwaya ya tambayeta me ya hanata tafiya?,amma ya tabbatar idan yayi hakan zai sake gayyatowa kansa fushin da yake yaqi dashi. Kalamanta sun soki zuciyarsa sosai,sun masa wani irin rami da ya tabbatar zaibar gurbi da miki cikin zuciyarsa.
Iya adadin jurar tsaiwar da zaiyi ya kaita,sai ya zame hannunsa daga qarfen a hankali ya fara takawa. Taku hudu kawai yayi,idanunsa a gabanshi ba tare da ya ko waiwayeta ba,ya motsa labbansa da muryarsa da tayi wani irin zurfi yace.
"Ba iya mulki iko da ginin doguwar katanga bane ke lullube da masarauta ba.......akwai tarin abubuwan dake buqatar zurfafa tunani da kyau.....ba dukkan murmushi bane ke nuna kulawa......ba kowacce farar fuska bace me dauke da kyakkyawar zuciya fara qal.....ka fara kula da kanka kafin kowa ya kawo maka daukin kula da kai" Ya qarashe maganan yana tafiya kai tsaye ga steps din da zasu sadashi da balcony dinsa zuwa babban sashensa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Tafiyarsa cikin izza duk da ruwan dake jiqa rigar jikinsa......da bata tabbacin barinta a gurin a yashe yafi qona mata rai da tsaye mata cikin idanuwanta da tunaninta. Maganganunsa basu kasance abun maida hankalinta ba.......face aikinsa da ya sanya taji ya sake zama LAMBA DAYA cikin manyan halittun data tsana a duniya.
Ko a yanzun da birra ke taimaka mata tana rage kayan jikinta,shehnaz dake daga kwance tana qarewa fuskarta ne kawai kallo.
Wani irin kwantaccen fushi ne kawai ke yawo saman fuskartata,fushin dake qara jefa shehnaz a duniyar mamaki. Me yasa komai na sheikh haisam take zafafarsa fiye da na kowa?.....me yasa ta gaza maida hankali ga aurenta dake matsowa?,take sanyawa ranta damuwa akan kowanne aiki ko hukunci da zai zartas?.
Ko a yanzun da duniya ta karade da sautin saukar mamakon ruwan sama me nauyin gaske,akhnan din na gaban glass door saman sofa,sanye da wata sweeter me sulbi oversized,peach color ce data dorata saman sleeping gown din da birra ta dauko mata. Wani qawataccen blanket birra ta dora mata saman kafadunta kafin ta musu sallama ta fice bayan ta ajewa akhnan din hular sanyi me laushin gaske a gefanta. Komai na rayuwarta yi mata akeyi idan ka dauke wanka da sallah,har yanzu shehnaz tana mamakin yadda bata iya yin komai wa kanta ba.
A yadda ta zauna ta wani cure guri daya,wani zama tayi me shigen tsugunno cikin kujerar wanda yawancin lokuta shi takeyi idan har ranta yana a bace. Dukka idanunta suna kallon glass dinne da yadda ruwan kebi ta jikinsa yana sauka qasa. Gajiya da kallonta shehnaz tayi,ta yunqura ta sauka daga saman lallausan gadon nasu,ta tako a hankali ta dawo gabanta tana zama saman wata qaramar ottoman.
"Tunanin meye haka biftu?" Shehnaz ta tambayeta a tausashe. Kaman ba zata kalli shehnaz din ba,sai kuma ta cira kanta a hankali tana maido dubanta ga shehnaz din,kafin ta sauke dauke idonta. Ta motsa labbanta a nutse.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/27, 19:22] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 43*
"Sultane yayi sadakar mutuncina irin wanda bai taba yi ba tunda ya haifeni........inda nasan haka zai sadaka da martabata har ta bawa wani bagidajen malami daman takata ko zama a kanta......tabbas dana yarda na auri duk wanda sultane yake da ra'ayi.......KIMATA da DARAJATA shehnaz......ba wani abu da yayi daidai da ita" Ta furta tana jinjina kai,abinda ke tabbatarwa da shehnaz wannan EGO din nata baya tabuwa.
"Biftu......a ganina yanzu lokacine da zaki maida hankali akan aurenki ba wadannan tunanikan bafa"
"Aure?" Shehnaz din ta waiwayo tana jifan shehnaz da tambayar. Kai shehnaz ta gyada tana dubanta itama kai tsaye.
"Eh aure......nan da kwanaki bakwai zuwa goma fa....."
Iyakar saninta da hadiman gidan gaba daya batasan bulama ba. Batasan wayeshi ba,batasan kuma wannan fuskar ba......me ya kawoshi nan?,cikin duhun da babu komai cikinsa sai hasken walqiya?,cikin duhun bishiyoyin da ba wanda zai iya labewa ciki sai wanda ke dauke da alama da tambari na rashin gaskiya?. Ba ita ba......hatta da maleek dake kallon komai daga nesa.......amma zama da haisam da dadewarsu tare ya sanya yake fahimtar lokutan da haisam din yake buqatar wanzuwa a guri shi kadai,don haka sai ya tsaya daga ness yana kallon komai. Da fari hankalinsa da nazarinsa gaba daya yana kan akhnan din. Ya cika da wani irin tarin mamakin yadda haisam yake iya hadiye maganganunta,ya sani,yana da wani irin kaifin hangen nesa da qoqarin hadiye bacin rai,saidai kuma sam sam baya daukan raini ko qanqani. Yanayin tsiwarta ya daure masa kai sosai,dukkan wannan izzar a yanzun da take magana da haisam din sai yaga ta kwaranye ta barta da iya tsiwar. Akwai wani abu da yake hanga daga can cikin dabi'unta da yake ganin zuwansa daidai da wani salon ra'ayi na haisam din.
JARUMTA......irin salon jarumtar nan ta babu gudu babu ja da baya......wani irin qarfin hali da TSAIWA saman ra'ayi,sai ya saki wani sassanyan murmushi,wanda suke murmushin nasa keda wuya ya hangi yadda haisam din ya motsa cikin wani irin zafin nama ya kuma finciko bulama din.
Abun ya matuqar zuwa masa a bazata da kuma bashi mamaki. Baiga wani alamun wanzuwar dan adam a gurin ba......ta yaya haisam din ya fahimci hakan?,bayan kuma da kwanyarsa ta tuna masa SHEIKH HAISAM din sai mamakinsa ya dinga raguwa,ya fara tunanin me mutumin yakeyi a tsakanin duhuwar gurin?.
Kamar baisan waye bulaman ba,kamar kuma baisan wanne aiki yakeyi ya banqare hannunsa ta baya da kyau,da wani irin yanayi me cike da zafi yake duban fuskar bulama din wadda ke shimfide a qasa.
"Bazan tsaya bata bakina ina tambayarka wa kake bibiya ko me kakeyi ba a nan gurin a irin wannan lokacin......kaman yadda bani da lokacin tsayawa tambayarka WAYR YA SANYAKA......Amma zan aikeka da saqo guda days ka shaidawa wanda ya sanyaka din cewa......ni muhammad ina me shaida masa,yana wasa ne da FARAR WUTA wadda cikin ruwan sanyi take qona dukkan wanda ya raina raina LAUNINTA". Sai ya saki hannuwan bulaman,wanda hakan ya bashi daman qarasa zubewa a qasa cikin wani irin matsanancin radadi da kafadunsa da gadon bayansa gaba suke masa,sannan ya yunqura da wani qaramin hanzarin da qarfin hali ne kawai ya tattara masa ragowar kuzarin,da wata irin sassarfa yake jan qafafunsa yana bacewa daga gurin.
Taku uku kawai yayi ya koma zuwa bakin qarfen data sameshi a gurin,ya kuma juya mata baya yana kafe gwiwar hannunsa jikin qarfen ya koma salon durqushen da yayi dazu yana ci gaba da duban tsirran da sukaci gaba da kadawa da sauri sosai saboda qaruwar iskar data ci gaba da kadawa gami da damshin ruwa daya fara sauka yaf yaf mara qarfi.
Idanu ta zubawa bayansa tana sake jin wani tsoro yana sake shigarta na wanzuwar shuru a gurin,bata ganin kowa sai shi da ita,don omar ma tun sanda yaga yanayin reaction din haisam ya matsa yana kutsawa zuwa kewayen gidan ko zai samu wani evidence motsi ko wani dake tare da bulama din.
Runtse idanunta tayi da qarfi daga duban faffadan bayansa da yabar mata saboda sririyar walqiyar data haska sararin samaniya,ta kuma nuna yawan hadarin da take dauke dashi. Tsoro me qarfi dake cakude da bacin rai taji yana shigarta. Nadamar rashin amsar tayin da yayi mata tun farko na tafiya taji yana ratsata. Me yasa bata tafi ba sanda taga wani abu me nauyi cikin qwayar idanunsa?,me yasa bata tafi ba a sanda yayi mata kallo na kai tsaye......kallon cikin qwayar idanunta.....bayan taso wani kallo ne da bai taba yi mata irinsa ba.
To amma duk haka ita din,GIMBIYA AKHNAN MUHAMMAD HAMMUD.....har rashin darajar da zai gwada mata yakai ya juya mata baya yana ci gaba da al'amuransa kamar baisan Allah yayi tsironta a gurin ba?. Yana qarqashin cin alfarma ta mahaifinta?,yana rayuwa cikin iko na mahaifinta?. Wayeshi?,banda ordinary mutum kamar kowa?......banda ordinary hadimi kaman sauran hadiman cikin gidan,wanda suke rayuwa cikin tattalin farincikinta.....kare dokokinta da iyakokinta,yau gata a tsaye a yashe......tamkar ba itace wannan gimbiyar da ganinta yake zama GAGARUMAR SA'A GA DUK MUTUMIN DA IDANIYARSA TA SAMU NASARAR GANINTA.
A cikin jikinsa yakejin tsaiwarta a gurin,saidai bayaso ya waiwaya gareta harta kalli irin nasa fushin. Yana jin tsaiwarta har cikin b'argonsa,bai kuma san abinda ya hanashi tafiya yabar gurin ba,saidai wani sashe na zuciyarsa yana nanata masa MARTABAR SULTANE ce ta jawo haka.
A duk sanda zai kwanta yana jin sauti da kuma maimaicin sautin sultane a maganarsu ta qarshe cikin airport.
"Dukkan masarauta......da dukkan wanda ke cikin ta na baka amanarsa......idan nace kowa da komai ciki harda AKHNAN. marainiya ce data taso batasan dadin mahaifiya ba,duk da ta shekara hudu da ita,amma kona shekara hudunma batasan dadin safeena ba,saboda ciwon hauka da safeena tayi daga randa akhnan tayi kwana arba'in a duniya.......safeena batayin cikakken wata uku da lafiya,saidai kuma a wata ukun duk sanda take a daidaita bata bari kowa yayi hidima ga biftu,kamar tasan tafiya zatayi ta barta,kamar tasan tafiyar bame nisa bace.
Yana iya hangen qwayar idanun sultane a sanda yake masa maganar,yana iya ganin raunin dake tattare da sultane din ta cikin qwayar idanun nasa,raunin dake gaya masa wannan feelings din bame sauqi bane......me tsananin nauyi ne,nauyin daya gaza ture yaringar daga zuciyarsa,duk da girma da adadin kura kurenta a tare dashi,daci gaba da bijirewa zuwa ga umarninsa.
Damqe qarfen yayi da kyau yana jin yadda ruwan ke qara yawa. Yanason ya waiwaya ya tambayeta me ya hanata tafiya?,amma ya tabbatar idan yayi hakan zai sake gayyatowa kansa fushin da yake yaqi dashi. Kalamanta sun soki zuciyarsa sosai,sun masa wani irin rami da ya tabbatar zaibar gurbi da miki cikin zuciyarsa.
Iya adadin jurar tsaiwar da zaiyi ya kaita,sai ya zame hannunsa daga qarfen a hankali ya fara takawa. Taku hudu kawai yayi,idanunsa a gabanshi ba tare da ya ko waiwayeta ba,ya motsa labbansa da muryarsa da tayi wani irin zurfi yace.
"Ba iya mulki iko da ginin doguwar katanga bane ke lullube da masarauta ba.......akwai tarin abubuwan dake buqatar zurfafa tunani da kyau.....ba dukkan murmushi bane ke nuna kulawa......ba kowacce farar fuska bace me dauke da kyakkyawar zuciya fara qal.....ka fara kula da kanka kafin kowa ya kawo maka daukin kula da kai" Ya qarashe maganan yana tafiya kai tsaye ga steps din da zasu sadashi da balcony dinsa zuwa babban sashensa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Tafiyarsa cikin izza duk da ruwan dake jiqa rigar jikinsa......da bata tabbacin barinta a gurin a yashe yafi qona mata rai da tsaye mata cikin idanuwanta da tunaninta. Maganganunsa basu kasance abun maida hankalinta ba.......face aikinsa da ya sanya taji ya sake zama LAMBA DAYA cikin manyan halittun data tsana a duniya.
Ko a yanzun da birra ke taimaka mata tana rage kayan jikinta,shehnaz dake daga kwance tana qarewa fuskarta ne kawai kallo.
Wani irin kwantaccen fushi ne kawai ke yawo saman fuskartata,fushin dake qara jefa shehnaz a duniyar mamaki. Me yasa komai na sheikh haisam take zafafarsa fiye da na kowa?.....me yasa ta gaza maida hankali ga aurenta dake matsowa?,take sanyawa ranta damuwa akan kowanne aiki ko hukunci da zai zartas?.
Ko a yanzun da duniya ta karade da sautin saukar mamakon ruwan sama me nauyin gaske,akhnan din na gaban glass door saman sofa,sanye da wata sweeter me sulbi oversized,peach color ce data dorata saman sleeping gown din da birra ta dauko mata. Wani qawataccen blanket birra ta dora mata saman kafadunta kafin ta musu sallama ta fice bayan ta ajewa akhnan din hular sanyi me laushin gaske a gefanta. Komai na rayuwarta yi mata akeyi idan ka dauke wanka da sallah,har yanzu shehnaz tana mamakin yadda bata iya yin komai wa kanta ba.
A yadda ta zauna ta wani cure guri daya,wani zama tayi me shigen tsugunno cikin kujerar wanda yawancin lokuta shi takeyi idan har ranta yana a bace. Dukka idanunta suna kallon glass dinne da yadda ruwan kebi ta jikinsa yana sauka qasa. Gajiya da kallonta shehnaz tayi,ta yunqura ta sauka daga saman lallausan gadon nasu,ta tako a hankali ta dawo gabanta tana zama saman wata qaramar ottoman.
"Tunanin meye haka biftu?" Shehnaz ta tambayeta a tausashe. Kaman ba zata kalli shehnaz din ba,sai kuma ta cira kanta a hankali tana maido dubanta ga shehnaz din,kafin ta sauke dauke idonta. Ta motsa labbanta a nutse.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/27, 19:22] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 43*
"Sultane yayi sadakar mutuncina irin wanda bai taba yi ba tunda ya haifeni........inda nasan haka zai sadaka da martabata har ta bawa wani bagidajen malami daman takata ko zama a kanta......tabbas dana yarda na auri duk wanda sultane yake da ra'ayi.......KIMATA da DARAJATA shehnaz......ba wani abu da yayi daidai da ita" Ta furta tana jinjina kai,abinda ke tabbatarwa da shehnaz wannan EGO din nata baya tabuwa.
"Biftu......a ganina yanzu lokacine da zaki maida hankali akan aurenki ba wadannan tunanikan bafa"
"Aure?" Shehnaz din ta waiwayo tana jifan shehnaz da tambayar. Kai shehnaz ta gyada tana dubanta itama kai tsaye.
"Eh aure......nan da kwanaki bakwai zuwa goma fa....."