← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 101

Sashe 86

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ina saurarenka ranka ya dade" Ya fadi da hausarsa dake gauraye da yanayin yaren oromo daya kama harshensa da kyau,kai kace bafillacen nigeria ne.

Numfashi sultane ya sake,yana ji lokaci yayi da zai fidda dukkan abinda yake ransa,yana jin lokaci yayi da zaiyi wannan aikin,wannan hobbasar,lokaci yayi da zai samawa diyarsa GARKUWA BANGO KUMA MAJINGINA. Yanaji a jikinsa rayuwar akhnan haka kadai ba tare da samun TSAYAYYEN bango majingina ba.....kamar wani abu yana dab da samun rayuwarta ya kuma lalatata. Zai iya jure komai amma banda shafewar JINI kuma irin safeena daga duniya. Ya jure salwantar Ahmad saboda a sannan yana sanya rai safeena zata rayu dashi,rayuwa me tsaho,zata kuma haifa masa wasu yaran da zasu shafe fiye da rabin gurbin rasa ahamd da sukayi,walau maza ko mata,sai gashi ashe duka duka rayuwar tata gajeriya ce.....ashe ba dogon zama a tsakaninsu.

"Muhammad......kana cikin mutanen dake da masaniyar komai daya shafi akhnan.....koda ban zauna maka dogon sharhi ba,tunda kusan tun daga zabar miji har zuwa mutuwar auren abune daya faru gaban idonka". Kai ya gyada a nutse,yana jin a ransa me ya hado zancan yarinyar dashi?,qasan ransa yana fata ba wani jagorancin ko nauyin sultane zai sake aza masa ba akan lamuranta.

"Gaskiya ne" Ya fada a nutse.

"Wannan abun daya faru wani baqon abune da bai taba faruwa ba ga diyoyinmu kaf tarihin kafa masarautar agadez haisam......inajin kamar na gaza wajen bayarwa ko yin abinda ya dace da bawa gobenta kariya a matsayina na mahaifi" Maganan ya taba haisam,tako ina jarumatar sultane yake gani da salon mulkinsa,mutum ne me jajircewa qwarai da juriya,a duk wani bincike da zaiyi akan salon mulkinsa tsarikansa da tsarin da masarautarsa take tafiya akai yana matuqar burgeshi,saidai dukkan dan adam tara yake bai cika goma ba,hakanan duk abinda akace GAIBU ne,yafi yiwa dan adam illa akan komai.......kamar yadda BOYAYYEN MAQIYI yafi komai zama dafi da guba me tsananin zafi da quna a rayuwar dan adam.....zai iya illata kowa ta inda ba'a taba zato ba.

"Ina fata ubangiji ya shiga lamarin" Ya furta a nutse,har yanzu kuma yana zurfafa hasashensa kan maganganun sultane.

"Ameen" Sultane ya amsa da wani irin yanayi,yanayin da sanya haisam ya sansano akwai maganan da sultane din keson fadi wadda da alama tana masa nauyi ne.

"Muhammad......bazan rufeka ko na boye maka ba,tunda ka shigo masarautata nake bibiye da motsinka,dabi'unka....da halayenka......kuma tashin farko na fahimci cewa kai din ba mutum ne kamar kowa ba.....akwai tarin kamala a tattare da kai,akwai wadansu irin kebantattun gwala gwalan dabi'u da suke wahalar samu daga gurin matashi kamarka.......komai naka yana da banbamci dana dukkan wani matashi dana sani......hatta da dattijai ma masu shekaru ba kowa keda wannan baiwar ba.....kai din mutum ne da bai zabi girmamawa ba.....girmamawa da kanta ce ta zabi nagartarsa". A nutse haisam ya sauke dubansa zuwa saman qafafunsa,yana jin nauyin yabon da sultane yake masa saman dukka kafadun da zuciyarsa. Duk da cewa ba'a bakinsa kawai ya fara jin ire iren wadannan kalmomin ba.....amma a yau sai yakejinsu tamkar wasu sababbin kalmomi ne daban da bai taba jinsu ba.

"Kamar darajata bata kai girman kalamanka ba ranka ya dade" Sakin murmushi sultane yayi.

"Kalamaina sun gaza ne kawai gurin fadin cikakkiyar nagartarka muhammad.....ka wuce duk yadda zan fada ko na musalta ka.....zan zarce zuwa ga dalilin kirana haisam kai tsaye" Sultane ya fadi yana jin nauyi.....yana jin kamar bai kamata ya azawa haisam nauyin da baisan dashi ba......yanajin kamar zaiyi abinda zai takura haisam din da walwalarsa gaba daya.....saidai kuma can cikin zuciyarsa yana jin wani aminci da sakewa wajen magana da haisam din......yana jin wani yaqini na cewa damuwarsa akan akhnan din tattare da haisam ne kawai zai maganceta.

"Ina neman ALFARMA......inaso kuma ka taimaki rayuka biyu KAYIMIN ALFARMAR". Wani motsawa zuciyar haisam tayi,saboda alfarmar da yake fadi sai yaji kamar tayi girma ya furta shi haisam yayima kamilin dattijo irinsa ALFARMA,saidai sam a muryarsa da yanayinsa ba zaka fahimci motsawar da zuciyartasa tayi ba.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Indai alfarmar da nake da iko da ita ne....kayi magana kanka tsaye ranka ya dade,kamar yadda zakayi da d'iyan cikinka daka haifa". Wani lumshe ido sultane yayi,yana jin hawaye yana taruwar masa a idanunsa. Wani girman haisam yana ninkuwa a idanu da zuciyarsa. Ko iya haka haisam ya tsaya,ko a iya haka haisam yace bazai auri akhnan ba tabbas ya girmamashi. Ko a iya accepting da yayi yake kallonsa a matsayin UBA ba shakka ya gama masa komai.....bazai taba baqi a idanunsa ba.....bazai kuma taba canza masa matsayi ba.

"Ina nemawa akhnan ALFARMA....nima ina neman ALFARMARKA......ina nemawa diyata akhnan AURENKA......ina neman amincewarka ka karbi auren diyata akhnan" Wani irin daukewa wuta tayi daga kowanne sassa na jikin haisam,wani irin shuru ya gilma cikin kansa dama cikin sadarwarsa da sultane,wani irin yanayi da yakejinsa kamar ya tashi daga duniyar gaske zuwa duniyar mafarki,wani irin yanayi daga gaza gasgata gaskiyarshi.

Wayar hannunsa yayi jarumtar riqewa sosai cikin kunnensa. Kowanne lafazi daga bakinsa ya nema ya rasa,ya bace masa bat daga kansa. Saidai kuma wannan mazantakar.....wannan jarumtar......wannan asalin jinin ABA JIFAR din dake yawo a jikinsa na musamman ne.....kamar yadda jinin KHADEEJATU YUNNUS JALLATA yake zagaye da duk wani gaba ta jikinsa. JININ SARAUTA guda biyu ke gauraye a jikinsa,manyan masarautun da asalin tarihinsu aka kafashi da JARUMTA RASHIN TSORO DA KUMA ZALLAR HIKIMA.

"Ranka ya dade......al'amari irin wannan ba qarami bane....."

"Na sani muhammad" Sultane ya tari numfashin haisam din yana jin wata qanqanuwar fargaba tana saukar masa.

"Aure ba kyautatawa bace kawai.....yana dauke da haqqoqi da nauye nauye masu yawan gaske....."

"Wannan dalilin ya sanya nazo gareka" Ya sake fadi haisam yana sauke maganansa. Idanunsa ya maida ya lumshe a hankali,yana jin wani abu yana ratsa sassan jikinsa. Wani baqon yanayi dake qulle da cakudewar tunani. Shuru ya sake wanzuwa me dan tsaho,har sai da kowannensu yayi tsammanin d'an uwansa ya sauka daga kan layi,kafin muryar haisam me zurfin nan ta sake motsawa.

"Bazan iya amsawa da komai ba a daren nan.....bazan iya cewa komai ba ranka ya dade" Murmushi me dan sauti sultane ya saki.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/10, 19:48] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 76*

*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX

"Ba da qaramar magana nazo maka ba muhammad da zan zaci ko sanya ran samun amsarka a yanzu yanzu ba......ka dauki dukka lokacin da yayi maka kayi tunani a kai.....amma ina roqarka alfarma kada ya zarta kwanaki uku,saboda ina dab da barin madeena.......nayi magana da muhammad dawud.....na kuma buqaci yayi magana da ahalinka akan batun,saidai kasan ko yaushe namiji baya buya a bayan wani namijin....shi yasa na yanke nayi magana dakai kai tsaye kaima,kada ka damu muhammad.....idan har amsarka itace A'AH.....idan har amsarka itace BAZAN IYA AUREN AKHNAN ba,kada kaji komai,kada kuma kaji wani nauyi,ka shaidamin kanka tsaye,zan fahimceka muhammad,zan kuma amsheta da girmamawa da mutuntawa,hakan kuma bazai canza komai a tsakaninmu ba......idan kuma har ka amsa min da ZAN KARBI AUREN DIYARKA.....ZAN KARBI AKHNAN a mazaunin MATA.......amsar zata zamemin mafi kyawun kalma dana taba ji a kunnuwana.......zan samu nutsuwa da aminci koda a yau na fadi na mutu,saboda na kubutar da wani tsagin ruhi.....wani bangare na gangar jiki da rayuwar SAFEENA zuwa ga wani amintaccen hannu.....zan baka akhnan wadda ba zata kasance MATA kawai a tare dakai ba.....aah na tabbatar zakaci gaba da kallonta a matsayin MARAINIYA wadda ke rayuwa qarqashin alfarmarka.....sannan ba zaka gushe ba zaka kalleta da sunan DIYAR SULTANE".

Inda a sannan za'a auna nauyin maganganun sultane a mizanin awo a sannan haisam yasan zasu rinjayi komai da za'a azasu a kai. Sun kammala waya da sultane amma maganganunsa sun masa wani tsaiwar mashi saman zuciyarsa,sun hadu sun cakude da maganganun morsa safiyya da duk motsin da zaiyi sai ya dinga jin kamar maganace kai tsaye data fita daga bakin nanay dinsa.

Yana takawa zuwa sassansa amma jikinsa yayi wani irin mutuwa. Yayi imani da qaddara a rayuwar dan adam gaba daya.....amma a yanzun ya samu kansa da tambayar kansa da kansa AKWAI QADDARAR DATA SHIGO DASHI AGADEZ?. Daga can qasan zuciyarsa ake amsa masa da EH.....amma yana qoqarin ture wannan.

Sassan nasa ba wani motsin da zai dameshi,don daga hadimai masu kula da buqatunsa da sassan nasa,sai kuma abdii daya baro a dakinsa a qasa.

Duk da ya jima bai budr balcony din bedroom dinsa ba tun a wancan ranar na qarshe daya gama fahimta cewa gurin tsaiwarta ne,kuma suna maqwafataka ta kusa da kusa da balcony din nasu,bai sake buda gurin ba bare ya shiga. Ya taka a hankali yana qarasawa gaban qarfen balcony din,ya aza hannunsa saman qarfen a nutse,sai yaji ya sauka saman lallausan wani abu,abinda ya sanyashi sauke dubansa kenan akai.

Mayafinta ne na wancan ranar,bai kwance ba har yanxu yana daure a jiki kamar yadda ya daure shi,ya manta dashi kwata kwata a gurin,sai ya janye hannunsa a hankali gefe,abinda ya faru a ranar yana dawo masa.

Me yasa qaddara takeson tursasasu bisa dole,me yasa qaddara ta dage saita hada tarayyarsa da tata guri daya?. Bayan akwai nisan tazara me yawa tsakaninsu. Ya santa sanin da ita kanta bata taba tunani ba,yayi zuzzurfan bincike game da dabi'unta abinda baisan dalilin daya kaishi ga aikata haka ba. Baiga wata dabi'a tata guda daya data masa ba banda ciyarwar JUMA'A data wajabtawa kanta. Ta kowacce fuska dabi'arta bame kyau bace,dabi'arta bata siffantu da kalar dabi'ar macen da za'a kwadaitu ga aurenta bane.
Chapter 86 · 0% Book details