Sashe 8
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maganan ta daketa da zafin data saba dukanta,saidai kuma da wurwuri ta gano ta kuma fahimci akwai wani d'anannen tarko cikin maganan morsa safiyya,da biyu a yau ta maimaita maganan gaba sultane,gaban nanay da ta lura ita daya ta ankara da tsaiwarta daga qofa. Duk da cewa tarko ne maganar tata,amma ta hango tarin mafita a cikin tarkon......ta hango hanyar bullewarta.
"Ya isa safiyya" Sultane ya fada da sigar dakatar da momma safiyya,amma saita murmusa don har yanzu batakai gaci ba.
"Ka barni na gaya mata,zan gaya mata abinda yake shine.......illar bada tarbiyya ga macen da batasan ciwon haihuwa b........"
"Ya isheni haka safiyya!.....ya isheni!!!" Mammina ta magantu cikin wani irin fushi tana miqewa tsaye. Irin wannan fushin morsa safiyya ke fata da burin gani a tattare da ita......irin wannan fushin da take fata ya kaita ga yakice akhnan ta barta zuwa gareta......ta barta zuwa ga ainihin UWAr data cancanci rayuwarta........ta barta da AHALINTA na haqiqa........ta barta taju GARDIN soyayya da 'YAN UWANTAKA daga ahalinta na asali.......ahalinta na tsatso.
"Ki jima kina jifana da miyagun kalamai saboda haihuwa......kin dade kina fadamin dukka maganan da yazo bakinki akan akhnan......."
"Baki kyauta ba safiyya.......ba halinki bane,bai kuma kamata a yanzu ace kinyi ba,bai dace ki rama alkhairi da sharri ba" Muryar nanay dake bayyanar da zallar bacin rai ta iso gurin Nanay din tana takowa zuwa ciki gami da gaza jure ci gaba da tsaiwa daga bakin qofar don kada ta shigo ta yanke maganar da yakeyi da iyalin nasa. Amma ganin maganganu suna neman juyewa zuwa zafafan musayar yawu daka iya bada sakamako maras kyau taga ya dace ta qaraso ta kamawa d'an uwanta wannan rigimar da take hange cewa ta yau din ta dabance......ta yau din me girma ce.
Da sassarfa mammina ta taka tana cimma Nanay. Idanunta cike fal da hawaye ta kama hannunta.
"Don Allah ki gaya mata.......ki kuma tambayeta sai yaushe zata ga alkhairi na?.......sai yaushe zan zama MACEN ALKHAIRI a idanunta. Me takeso,me take buqata nayi bayan wanda nayi da zai gamsar da ita?" Mammina ta fada hawayen da ya tarar mata yana saukowa.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/2, 20:07] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 09*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________
"Tsahon shekaru ashirin da suka yita shudewa kawo yau.....ko meye ya kamata morsa safiyya ki fahimceshi......ko menene ya kamata ki yafeshi" Murmushi me dauke da wani nannuyan ciwo morsa safiyya ta saki. Tana hangen wani kwantaccen hali dabi'a zubi da tsari na musamman daga kowanne motsin mammina din. Abubuwan suna sake kwance mata kai,amma alqawari ne ta yiwa kanta,bakin rai bakin fama......ba zata taba sassautawa muradan mammina ba......ba zata taba rusuna musu ba......ba zata taba sauke mata kai ba......ba zata taba bari ta mulketa ba......ba kuma zata daina adawa da kowanne tsari da shiri nata ba muddin bata saki kurwa da rayuwar akhnan ba.
"Akwai wani lulluben duhu dake nannade cikin wasu irin yankuna masu tsananin duhun daya kusa fin duhun da suke boye dashi......ba zaku fahimci komai ba......wani yare ne da baya buqatar harshe ko motsi na labba ballantana akai ga fitar sauti.........abu daya data tambayeni kan me zatamin na yaba.....abu dayannan shine KI 'YANTA RAYUWAR AKHNAN.....KI RABU DA ITA DA DUK ABINDA YA SHAFETA".
Sosai kalmarta ta farko tayi duka me sauti a qirjin mammina.......bada hankali ga kalmar kuma na nufin d'arsuwar alamu masu tarin yawa ga zukata da kuma ayyuka,don haka ya zabi yin duk wani tattaki nata da fidda salon iya kauda hankalinta akan jimla ta biyu,don haka ta saki hannun Nanay a hankali,wani murmushi yana subuce mata maras armashi,tayi taku uku tana sake kusanta kanta da inda morsa safiyya ke zaune.
"Wannan shine cikar burinki......shine cikar burin da har ki mutu ba zaki sameshi ba muddin ba kyakkyawar niyya da nufi bane a zuciyarki......HAR ABADA bazan wulaqanta akhnan ta hanyar banzatar da ita da rayuwarta ba kaman yadda kike fata,jinin sultane yafi qarfin wulaqanci ko kuma tozarci na har abada a hannun zaituna.......idan baki da labarin soyayya KOMA KI TAMBAYA cikin hamshaqiyar qasar data tara isassun mata irin ZAITUNA.......Zan sadaukar da farincikina saboda farincikin akhnan.....zan iya yaqi da kowa don akhnan ta samu 'yancin da yayi daidai da rayuwarta........kamar yadda a yanzu nake tsugunnawa saman qafofina nake roqarka ka janye auren hakeem akan akhnan......ko don ka ceto rayuwar da qwaya daya tal da ita kadai SAFEENA ta iya baka" Mammins tayi maganan tana sulalewa saman gwiwarta gaban sultane.
SAFEENA dukkan rauninsa ce......safeena dukkan qwarin gwiwarsa ce a sanda yake raye. Sa'insarsu gaban should wani abune daya jima irin haka bata sake faruwa ba a gabansa. Kamar kowacce ta mance da wanzuwarsa a gurin,kamar kowacce ta mance da hukuncin aikata haka a gabansa?.
"Zan dauki alhakin komai......amma bazan iya jurar rasa biftu ba.......ta fara da shan guba.....dukkanmu gaba bamu da tabbacin abinda zai faru da rayuwarta".
Wani irin masifaffen tashin hankali ne morsa safiyya taji yana yanko mata. Idan ana lissafin ANNOBA tana ganin cewa mammina tafi gaban a kirata da sunan ko a sanyata a sahun......tafi qarfin sunan ANNOBA saidai wata halitta daban da tasha banban da yanayi da tunanin dan adam. Soke auren akhnan da hakeem hakan yana nufin dawowar kowanne lissafi baya?. Hakan yana nufin maida kowanne lissafi izuwa farkonsa?,tarin gwagwarmaya tarin dauki ba dadin da akayi dukka sun koma farkon lissafi?. Akwai wani tunani......akwai wani target akwai kuma wani ajiyayyen abu kuma boyayye a bayan kowanne faruwar al'amari.
"Soke auren hakeem da akhnan da zakayi shine babban kuskuren da zaka aikata sultane...." Morsa safiyya ta fadi tana girgiza kanta gami da qoqarin boye dukkan tsoron dake cin ransa.
Da wata irin fusata mammina ta waiwayo tana duban morsa safiyya.
"Wannan shine kalar maqaryaciyar soyayyar da kike iqirarin kina yi mata?......kar ya soke auren?.......yau tasha gube gobe tasha ruwan batir?......burinki kawai tayi aure?,tabar gabanki bayan ba saman kanki take rayuwa ba?,me ta tsare miki?.....tayi aure kowanne yanayi ma zata shiga ba damuwarki bane?,saboda BAKE KIKA HAIFETA BA?,SABODA BA FALAAK BACE?"
"ZAITUNA!......kul dinki.....kul bakinki ya sake....." Maganan da morsa safiyya ta fara da wani irin zafi daya sanyata miqewa tana nuna mammina da yatsa maganan ya katse saboda tsawar da sultane ya sakar musu.
Ba wadda bataji ta koma hayyacinta ba,don baquwar halayya ce ga sultane din. Yana da wani irin girma da yake bawa kowaccensu saboda kowacce akwai wani ajiyayyen dalili da yasa take da girma da daraja a idanunsa.
"Idan har wanzuwata a guri bata hanaku aibata kawunanku ba.....meye zai sanya ku fasa?" Yayi tambayar da harshen da yasa kowacce jinin daya fara tafarfasa a jikinta ya fara sanyaya.
Ganinta da jinta taji kaman ya makance na wucin gadi,yau ita ake duban cikin idanunta ake cewa jinin safeenarta BA ITA TA HAIFETA BA?. Wata bare can?,wata cikakkiyar abokiyar adawar da dukka tsahon rayuwarsu basu data biyunta?,tabbas.....idan tayi rantsuwa ko kaffara ba zatayi ba.....inda safeena tana raye a yau,zataji ciwo sama da ciwon da ita takeji yanzu cikin qirjinta,saidai wannan ciwon.....wannan radadin ta haramtawa mammina ganinsa.....ba zata taba bari ta fahimceshi ba.
"A shirye nake na dauki mummunan mataki akan kowaccenku......muddin kasancewata a guri ba zata zama sitiyarin control dinku ba!" Ya sake fadi wani fushi me kaifi yana gilmawa ta cikin idanunsa yana nuna yatsansa dan manuni.
"Kayi mana afuwa" Nannie ta furta ita kanta a yau tana jin banbanci tsakanin yanayin sultane na yau dana kullum.
Shuru ne ya ratsa dakin,tamkar ba ragowar wani abu me numfashi a cikin dakin.
Numfasawa sultane yayi,yana qoqarin daidaita kanshi da ragewa kansa damuwar da yakeji tana tasiri kadan kadan cikin zuciyarsa. Yana jin qwarin gwiwar hukunta akhnan.......yana jin takai lokacin da zata fuskanci fushinsa dama hukuncinsa,yana jin wani tasiri na maganganun morsa safiyya a ransa,yana ganin wasu daga cikin gaskiyarta,koda ta kasance me taurin kai,koda ta kasance me kafiya,koda ta kasance me tsaurarawa da yawa.
"Dole ne na janye auren akhnan da hakeem.......tunda wadanda keda alhakin karbar auren sun janye suma".
Tsahon rayuwarta zata iya cewa,ta jima bataji wani labari daya saukar da wata irin farinciki me girman gaske cikin zuciyarta ba.......ta jima bataji abinda yazo mata a bazata irin wannan a wadannan shekarun ba. Murmushi ko dariya take buqatar tayi a irin yanayin don furzar da yanayin da zuciyarta ke ciki,amma saita rikide da nuna alhini dama tsoro baro baro saman fuskarta.
Yadda morsa safiyya ke dubansa da wani irin dimaucewa,haka mammina ke kallon sultane da yanayin daya kebanta da zuciyarta kadai. Wani irin zafi zuciyarta ke mata,tana so ta riqe bakinta,tana so tayi shuru kada ta tanka,amma tana jin idan tayi haka,idan har sai ta jira sultane yace wani abu da kanshi zuciyarta zata fashe,zuciyarta ba zata iya dauka ba.
"Amma.......ba nadama?......ba kuskure cikin faruwar?......"
"Sun janye saboda labari yaje musu.......'yar da d'ansu ke burin kawowa cikin ahalinsu da ake zaton mace ta gari ce......yarinya nutsatsiya me biyayya ga maganar magabatanta abun ba haka bane..........a dazu na aika an maida musu da dukiyar aurensu da komai da komai nasu cikin mutuntawa kamar yadda suka kawo......" Shuru gurin ya sake dauka,kafin a hankali nannie ta magantu.
"Koda basu janye ba,koda basu fasa ba ni a nawa hasashen janyewar shi yafi alkhairi.......a duk sanda irin haka ta sake faruwa,ba wanda yake da tabbacin abinda zai ci gaba da faruwa,koma meye......ko yaya yanayin yakai ga hasala ko baci akhnan diyarmu ce,kuma lallai muna qaunar rayuwarta sama da yadda zamu qaunaci rayuwar kowa" .
"Ya isa safiyya" Sultane ya fada da sigar dakatar da momma safiyya,amma saita murmusa don har yanzu batakai gaci ba.
"Ka barni na gaya mata,zan gaya mata abinda yake shine.......illar bada tarbiyya ga macen da batasan ciwon haihuwa b........"
"Ya isheni haka safiyya!.....ya isheni!!!" Mammina ta magantu cikin wani irin fushi tana miqewa tsaye. Irin wannan fushin morsa safiyya ke fata da burin gani a tattare da ita......irin wannan fushin da take fata ya kaita ga yakice akhnan ta barta zuwa gareta......ta barta zuwa ga ainihin UWAr data cancanci rayuwarta........ta barta da AHALINTA na haqiqa........ta barta taju GARDIN soyayya da 'YAN UWANTAKA daga ahalinta na asali.......ahalinta na tsatso.
"Ki jima kina jifana da miyagun kalamai saboda haihuwa......kin dade kina fadamin dukka maganan da yazo bakinki akan akhnan......."
"Baki kyauta ba safiyya.......ba halinki bane,bai kuma kamata a yanzu ace kinyi ba,bai dace ki rama alkhairi da sharri ba" Muryar nanay dake bayyanar da zallar bacin rai ta iso gurin Nanay din tana takowa zuwa ciki gami da gaza jure ci gaba da tsaiwa daga bakin qofar don kada ta shigo ta yanke maganar da yakeyi da iyalin nasa. Amma ganin maganganu suna neman juyewa zuwa zafafan musayar yawu daka iya bada sakamako maras kyau taga ya dace ta qaraso ta kamawa d'an uwanta wannan rigimar da take hange cewa ta yau din ta dabance......ta yau din me girma ce.
Da sassarfa mammina ta taka tana cimma Nanay. Idanunta cike fal da hawaye ta kama hannunta.
"Don Allah ki gaya mata.......ki kuma tambayeta sai yaushe zata ga alkhairi na?.......sai yaushe zan zama MACEN ALKHAIRI a idanunta. Me takeso,me take buqata nayi bayan wanda nayi da zai gamsar da ita?" Mammina ta fada hawayen da ya tarar mata yana saukowa.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/2, 20:07] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 09*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________
"Tsahon shekaru ashirin da suka yita shudewa kawo yau.....ko meye ya kamata morsa safiyya ki fahimceshi......ko menene ya kamata ki yafeshi" Murmushi me dauke da wani nannuyan ciwo morsa safiyya ta saki. Tana hangen wani kwantaccen hali dabi'a zubi da tsari na musamman daga kowanne motsin mammina din. Abubuwan suna sake kwance mata kai,amma alqawari ne ta yiwa kanta,bakin rai bakin fama......ba zata taba sassautawa muradan mammina ba......ba zata taba rusuna musu ba......ba zata taba sauke mata kai ba......ba zata taba bari ta mulketa ba......ba kuma zata daina adawa da kowanne tsari da shiri nata ba muddin bata saki kurwa da rayuwar akhnan ba.
"Akwai wani lulluben duhu dake nannade cikin wasu irin yankuna masu tsananin duhun daya kusa fin duhun da suke boye dashi......ba zaku fahimci komai ba......wani yare ne da baya buqatar harshe ko motsi na labba ballantana akai ga fitar sauti.........abu daya data tambayeni kan me zatamin na yaba.....abu dayannan shine KI 'YANTA RAYUWAR AKHNAN.....KI RABU DA ITA DA DUK ABINDA YA SHAFETA".
Sosai kalmarta ta farko tayi duka me sauti a qirjin mammina.......bada hankali ga kalmar kuma na nufin d'arsuwar alamu masu tarin yawa ga zukata da kuma ayyuka,don haka ya zabi yin duk wani tattaki nata da fidda salon iya kauda hankalinta akan jimla ta biyu,don haka ta saki hannun Nanay a hankali,wani murmushi yana subuce mata maras armashi,tayi taku uku tana sake kusanta kanta da inda morsa safiyya ke zaune.
"Wannan shine cikar burinki......shine cikar burin da har ki mutu ba zaki sameshi ba muddin ba kyakkyawar niyya da nufi bane a zuciyarki......HAR ABADA bazan wulaqanta akhnan ta hanyar banzatar da ita da rayuwarta ba kaman yadda kike fata,jinin sultane yafi qarfin wulaqanci ko kuma tozarci na har abada a hannun zaituna.......idan baki da labarin soyayya KOMA KI TAMBAYA cikin hamshaqiyar qasar data tara isassun mata irin ZAITUNA.......Zan sadaukar da farincikina saboda farincikin akhnan.....zan iya yaqi da kowa don akhnan ta samu 'yancin da yayi daidai da rayuwarta........kamar yadda a yanzu nake tsugunnawa saman qafofina nake roqarka ka janye auren hakeem akan akhnan......ko don ka ceto rayuwar da qwaya daya tal da ita kadai SAFEENA ta iya baka" Mammins tayi maganan tana sulalewa saman gwiwarta gaban sultane.
SAFEENA dukkan rauninsa ce......safeena dukkan qwarin gwiwarsa ce a sanda yake raye. Sa'insarsu gaban should wani abune daya jima irin haka bata sake faruwa ba a gabansa. Kamar kowacce ta mance da wanzuwarsa a gurin,kamar kowacce ta mance da hukuncin aikata haka a gabansa?.
"Zan dauki alhakin komai......amma bazan iya jurar rasa biftu ba.......ta fara da shan guba.....dukkanmu gaba bamu da tabbacin abinda zai faru da rayuwarta".
Wani irin masifaffen tashin hankali ne morsa safiyya taji yana yanko mata. Idan ana lissafin ANNOBA tana ganin cewa mammina tafi gaban a kirata da sunan ko a sanyata a sahun......tafi qarfin sunan ANNOBA saidai wata halitta daban da tasha banban da yanayi da tunanin dan adam. Soke auren akhnan da hakeem hakan yana nufin dawowar kowanne lissafi baya?. Hakan yana nufin maida kowanne lissafi izuwa farkonsa?,tarin gwagwarmaya tarin dauki ba dadin da akayi dukka sun koma farkon lissafi?. Akwai wani tunani......akwai wani target akwai kuma wani ajiyayyen abu kuma boyayye a bayan kowanne faruwar al'amari.
"Soke auren hakeem da akhnan da zakayi shine babban kuskuren da zaka aikata sultane...." Morsa safiyya ta fadi tana girgiza kanta gami da qoqarin boye dukkan tsoron dake cin ransa.
Da wata irin fusata mammina ta waiwayo tana duban morsa safiyya.
"Wannan shine kalar maqaryaciyar soyayyar da kike iqirarin kina yi mata?......kar ya soke auren?.......yau tasha gube gobe tasha ruwan batir?......burinki kawai tayi aure?,tabar gabanki bayan ba saman kanki take rayuwa ba?,me ta tsare miki?.....tayi aure kowanne yanayi ma zata shiga ba damuwarki bane?,saboda BAKE KIKA HAIFETA BA?,SABODA BA FALAAK BACE?"
"ZAITUNA!......kul dinki.....kul bakinki ya sake....." Maganan da morsa safiyya ta fara da wani irin zafi daya sanyata miqewa tana nuna mammina da yatsa maganan ya katse saboda tsawar da sultane ya sakar musu.
Ba wadda bataji ta koma hayyacinta ba,don baquwar halayya ce ga sultane din. Yana da wani irin girma da yake bawa kowaccensu saboda kowacce akwai wani ajiyayyen dalili da yasa take da girma da daraja a idanunsa.
"Idan har wanzuwata a guri bata hanaku aibata kawunanku ba.....meye zai sanya ku fasa?" Yayi tambayar da harshen da yasa kowacce jinin daya fara tafarfasa a jikinta ya fara sanyaya.
Ganinta da jinta taji kaman ya makance na wucin gadi,yau ita ake duban cikin idanunta ake cewa jinin safeenarta BA ITA TA HAIFETA BA?. Wata bare can?,wata cikakkiyar abokiyar adawar da dukka tsahon rayuwarsu basu data biyunta?,tabbas.....idan tayi rantsuwa ko kaffara ba zatayi ba.....inda safeena tana raye a yau,zataji ciwo sama da ciwon da ita takeji yanzu cikin qirjinta,saidai wannan ciwon.....wannan radadin ta haramtawa mammina ganinsa.....ba zata taba bari ta fahimceshi ba.
"A shirye nake na dauki mummunan mataki akan kowaccenku......muddin kasancewata a guri ba zata zama sitiyarin control dinku ba!" Ya sake fadi wani fushi me kaifi yana gilmawa ta cikin idanunsa yana nuna yatsansa dan manuni.
"Kayi mana afuwa" Nannie ta furta ita kanta a yau tana jin banbanci tsakanin yanayin sultane na yau dana kullum.
Shuru ne ya ratsa dakin,tamkar ba ragowar wani abu me numfashi a cikin dakin.
Numfasawa sultane yayi,yana qoqarin daidaita kanshi da ragewa kansa damuwar da yakeji tana tasiri kadan kadan cikin zuciyarsa. Yana jin qwarin gwiwar hukunta akhnan.......yana jin takai lokacin da zata fuskanci fushinsa dama hukuncinsa,yana jin wani tasiri na maganganun morsa safiyya a ransa,yana ganin wasu daga cikin gaskiyarta,koda ta kasance me taurin kai,koda ta kasance me kafiya,koda ta kasance me tsaurarawa da yawa.
"Dole ne na janye auren akhnan da hakeem.......tunda wadanda keda alhakin karbar auren sun janye suma".
Tsahon rayuwarta zata iya cewa,ta jima bataji wani labari daya saukar da wata irin farinciki me girman gaske cikin zuciyarta ba.......ta jima bataji abinda yazo mata a bazata irin wannan a wadannan shekarun ba. Murmushi ko dariya take buqatar tayi a irin yanayin don furzar da yanayin da zuciyarta ke ciki,amma saita rikide da nuna alhini dama tsoro baro baro saman fuskarta.
Yadda morsa safiyya ke dubansa da wani irin dimaucewa,haka mammina ke kallon sultane da yanayin daya kebanta da zuciyarta kadai. Wani irin zafi zuciyarta ke mata,tana so ta riqe bakinta,tana so tayi shuru kada ta tanka,amma tana jin idan tayi haka,idan har sai ta jira sultane yace wani abu da kanshi zuciyarta zata fashe,zuciyarta ba zata iya dauka ba.
"Amma.......ba nadama?......ba kuskure cikin faruwar?......"
"Sun janye saboda labari yaje musu.......'yar da d'ansu ke burin kawowa cikin ahalinsu da ake zaton mace ta gari ce......yarinya nutsatsiya me biyayya ga maganar magabatanta abun ba haka bane..........a dazu na aika an maida musu da dukiyar aurensu da komai da komai nasu cikin mutuntawa kamar yadda suka kawo......" Shuru gurin ya sake dauka,kafin a hankali nannie ta magantu.
"Koda basu janye ba,koda basu fasa ba ni a nawa hasashen janyewar shi yafi alkhairi.......a duk sanda irin haka ta sake faruwa,ba wanda yake da tabbacin abinda zai ci gaba da faruwa,koma meye......ko yaya yanayin yakai ga hasala ko baci akhnan diyarmu ce,kuma lallai muna qaunar rayuwarta sama da yadda zamu qaunaci rayuwar kowa" .