Sashe 61
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duban kansa yakeyi cikin madubin,yana jin wani izza tana shigarsa. Tsahon rayuwarsa bai taba ganin inda yayi kyau har haka ba,koda sau daya kuwa,duk da cewa yana rayuwa cikin sutura me kyau da kuma cima me kyau,amma ba sutura irin wannan ba....ba tufafi irin wannan ba me cike da nuna qarfin izzar wanda ya sanyasu. Sosai yakeji kansa yana sake shiga charge,abinda ya qara fadada nishadin da yakeji kenan,don tun daga daren jiya ya baje dukkan kayan mayensa da aka dakatar dashi daga sha,yasha me isarsa,ya kuma dora da wani da safen nan bayan wadancan sun sakeshi. Yana jin wani banbanci da wadannan kayan da wadanda ya saba sha. Wadannan din masu taada ne sosai data sanya aka tanadar masa kwali kwali kawai don jin dadinsa,ta kuma yi masa alqawari daman,ta kuma cika,abinda ya sake saka masa nutsuwa da bin dukkan sharudda da qa'idojinta. Basa sakashi yayi mankas ya manta da abinda yakeyi,amma suna fiddashi daga duniyarsa,suna kuma fitar dashi daga ainihin duniyar da yake rayuwa a cikin ta,suna sakashi ya jishi daidai yake da kowa,yana kuma daidai da tarar kowa da komai.
Waiwayowa yayi yana murmushi yana duba tamim,abinda ya sanya tamim dauke kansa daga mummunan kallon da yakewa almaz din,kallon dake cike da hassada qyashi kishi da baqinciki.
"Wai nine almaz a haka?.....nine na mallaki matar aure d'iya mafi girman daraja a yankin africa......gida irin wanda nake mafarki da rayuwa cikin izza mulki da qasaita.......amma kasan meye tamim?" Yayi tambayar yana duban fuskarsa yana kuma takowa zuwa gaban tamim din. Qoqarin gaske tamim yayi wajen maye murmushi saman fuskarsa.
"Na rasa wanne dalili ne ya sanya uwargijiyarka ta zaboni a cikin tarin matasan qasar Ethiopia.....a baya nayi tunanin don tana mahaifiyata ne,amma a yanzu tunanina ya gagara cafko komai" Almaz yayi maganar da tarin mamakin dake ransa daya bayyana cikin muryarsa.
Murmushi tamim ya saki,yana takawa a hankali gaban wani babban glass cup daya cikashi da tataccen lemon inibi wanda ya cakudashi da sinadarai daban daban.
"Kaidai ungo wannan kasha mu tafi.....yanzu ba lokaci bane na tunanin wannan.....tunda harka yadda ka shiga cikin masu sa'a ai shikenan,ba abinda ya rage maka saika zuba idanu kaci gaba da irgen lokutan sa'arka". Dan shuru almaz din yayi,kafin kuma ya saki murmushi yana miqa hannunsa ya karbi lemon hannun tamim din.
"Inason lemon nan sosai,inajin dadinsa" Ya furta a hankali sannna kuma yakai cup din bakinsa.
Tas ya shanye lemon a kurba daya,sannan ya miqawa tamim cup din yana cewa.
"Kamar zai bani freshness din da nakeso,na gode tamim" Ya damqa masa cup din yana juyawa. Da wani kalar shu'umin murmushi yabi almaz din,rabin aikinsa ya kammala saura rabi,yana duban takunsa da yakeyi cikin wani yanayi daya bayyanar da b'urbushin qasaita.
"Matsiyaci ya samu guri,wai har ya iya yanayi na masu mulki da saruta" Ya fada a fili can qasa yana jifan hanyar da almaz yabi da harara.
Jerin gwanon motocin alfarmar guda shida ne cass suka takewa motor din da almaz ke ciki baya. Ya saki wani irin murmushi sanda dukkan wani hadi dake cikin lemon ya fara zagaya sassan jikinsa,ya kuma soma jinsa a sama,uwa uba yadda yaga manyan motocin alfarma irin wannan na take masa baya sai ya sake sanya yanayin yabi jikinsa sosai
"Shege almaz,yau shine kamar gomna?" Ya tambayi kansa da kansa yana dariya. Sam a rayuwarsa ya rayu cikin wani madaukakin yanayi ba burinsa bane,damuwarsa daya shine ya rayu cikin 'YANCI. Bayason UMARNI,yafison ya rayu cikin sakewa da kuma zabawa kansa duk kalar rayuwar da yakeso,ba tare da an bashi umarni ba,ba tare da an sanyashi ko an hanashi ba. Ya sani......yanajin wata izza da girma a cikin jininsa da baisan wacce iri bace,wannan ya sanya sau tari yafi zabar kebance kansa tare da qin amincewa ya shiga taron jama'a.
Duba daya tamim yayi masa ya tabbatar ya fara fita daga hayyacinsa,ya fara buguwa,sai ya gyara zamansa sosai yana dubansa.
"Kasan meye almaz?" Kai ya girgiza yana duban tamim da idanun nan nasa da tamim din yake ganin suna masa kama da wasu idanu.
"Akhnan matarka.....tana da tsananin girman kai....bata girmamawa kowa saboda tana ganin mahaifinta shine sarki a wannan yankin....."
"Ashe?" Almaz ya fadi da wata irin murya yana bude idanunsa da kyau. Kai tamim ya jinjina cikin bashi tabbaci da son isar da saqonshi
"Qwarai da gaske.....kai baka lura ba?,a matsayinka na namiji kuma mijin dake aurenta.....ta taba gaidaka?,kota taba zuwa gurinka nemanka?,kota taba nemanka din koda a waya ne?" Shuru almaz yayi,wasu abubuwa suna cakudewa cikin kansa tsakanin maganganun tamim da kuma abinda tamim din ya bashi yasha. Gefe daya wata izza tana huruwa cikin ransa,yana jin kansa yana girma da fadi.
"Ba ko daya" Almaz ya fada muryarsa tana kaduwa da wani irin yanayi na wanda ya fara buguwa.
"Ahto....to kai kuma saika bari aci gaba da tafiya a haka?"
"Inaaaa......daga yau zan fara nuna mata ina da iko a kanta" Ya fada yana ji a ransa dole ya zama tsayayyen namiji.
A hankali tamim ke buda masa wasu abubuwa,yana kuma sake karanta masa abubuwan da ya tabbatar zasuyi tsananin tasiri a kansa game da akhnan din. So samu komai ya fada jagule musu a yau,shi yasa ya fara da horashi da kadan daga cikin kayan mayen dana tanada,wanda wannan shine zai bashi damar dorawa kan tsarinsa d'od'ar ba tare da sunansa ko alamar ayar tambaya ta hau kansa ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/2, 22:22] +234 903 768 6798: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 54*
Idanu mammina ta lumshe tana kuma budesu idon nata akan akhnan din. Duk da yanayin da take ciki ba abinda ya gusar da wannan sassanyan kyan......wannan kyan irin na safeena......wannan kyan da ya zamewa rayuwarta dukka qalubale da baqincikin da har kawo yau ba wani abu daya sassauta a ranta. Wannan kyan tana fatan lokacin gushewarsa ya zama a kurkusa.......a shafe tarihinsa cikin qasar agadez. Shi ta yaya ma wai zata bari AKHNAN ta fita daga tasarrufinta?. Ta yaya zata yarda tabar ruhin safeena ya kwanta lafiya cikin kusewarsa?. Yadda ta sanya darare da yawa na rayuwarta suka gagara zuwan mata da dadi,haka takeso tayita rasa nata dararen a qasan kushewa cikin baqinciki da takaici.
A zahiri hannuwan akhnan din ta kamo a tausashe,har yadda tayi din ya sanya akhnan duban idanunta,tashin farko kuma ta hangi wannan tsantsar qaunar da kulawar data saba gani a tare da mammina din.
"Ina cikin tsananin farinciki yau biftu,kinsan saboda me?" Kai ta girgixa a hankali.
"Yadda naji sultane yana jero miki addu'o'i na sanya albarka cikin masallacin haram. Yadda sultane ya nunamin duk wani fushi da yakeyi da ke ya kau,yadda sultane ya nunamin ya.yafe miki,kuma a yanzun kin koma akhnan dinsa ta tun tale tale" Wata nannauyar ajiyar zuciya ta saki tana jin wani nauyi dake kwance a qirjinta yana raguwa. Wani sanyi taji gami da sassauci yana sauka saman zuciyarta,sai takejin wani girma da qaunar mammina suna saukar mata. Duk wani kyakkyawan albishir na alkhairi daga bakin mammina take fara jinsa,ita daya ce take dauke da dukkan wani albishir me dadi da zai faranta rayuwarta da duniyarta.
"Amma kinsan wasu lokutan nakanji nadama tana saukarmin na hadaki da almaz?" Ta furta muryarta can qasa tana kuma sadda kanta qasa jikinta yana nuna wani irin mugun laushi da yayi.
"Mammina......nadama wacce iri?" Ta tambayeta tana jin wani fargaba kadan. Kai ta daga tana sake kallonta.
"Nayi wannan abunne don na samar miki da 'yancinki,ki sake cikin rayuwarki kamar yadda kikeso,amma abun mamaki shine.....sai walwalarki take raguwa,takura take maye gurbin sakewa,me yayi zafi biftu?,bayan a yanzunne kike da 'yancin yin kowacce rayuwa da kike so?" Kai ta girgixa a hankali,tana jin wannan raunin nata da bata bari kowa ya gani yana taso mata.
"Ban saba bane mammina.....a hankali zan saba zan saki jikina".
" Amma ko kinsan wannan rashin sabon naki yana aje ayar tambaya me yawa saman zuciyar mutane a kaina da kanki?......kinsan yau ne ranar da za'a rakaki kwanan gida?" Kai ta daga da sauri ta zubewa mammina wadannan blue eyes din. Karon farko da mammina taji kalar kallon akhnan din ya mata nauyi gami da haifar da wata jaririyar faduwar gaba.
"Mammina.....kwanan gida?.....ni da almaz?" Ta furta da sigar tambaya me wani irin nauyi.
Kai ta jinjina mata cikin bata tabbaci,sannan tace.
"Haka yake a al'adar buzaye......haka yake tun kaka da kakanni,indai baso kike ki fadawa duniya cewa almaz ba zabinki bane". Shuru akhnan tayi,wai tana qoqarin daidaita kanta tana kuma qoqarin daidaita abinda takeji a qirjinta. Wani kwana ne da amarya zatayi guda daya tal a gidanta da ango,sannan washegari ya rakota ta dawo gidansu,sannan a sake shiryata a maidata.
Kai ta shiga girgzawa don ta kasa tausar zuciyarta ta karbi maganar. Sam ba zata iya ba......ba zata iya bin kowacce al'ada da akazo da ita ba wai akan aure,to a wanne dalili ma?,auren da dole ce ta kaita ga yinsa,dolen amintar da sultane da maido kyakkyawan alaqansu ta baya.
"Bazan iya ba mammina.....ba,bazanje ba,ko sama da qasa zata hadu bazanje kwana da almaz gida daya ba a yanzun,qarshen satinnan zan wuce Niamey,bana buqatar wani tsari da zai sanya yace zai bini,ko ke kice saimun tafi tare". Numfashi mammina ta sauke a hankali,dama ta sani,tasan za'a rina,kuma dama itama bata shirya tilastata kwana gida tare da almaz ba,to amma kuma tafiya Niamey bata hangen wani abu da zai sanya ta rushe tsarin tafiyarsu a tare.
Waiwayowa yayi yana murmushi yana duba tamim,abinda ya sanya tamim dauke kansa daga mummunan kallon da yakewa almaz din,kallon dake cike da hassada qyashi kishi da baqinciki.
"Wai nine almaz a haka?.....nine na mallaki matar aure d'iya mafi girman daraja a yankin africa......gida irin wanda nake mafarki da rayuwa cikin izza mulki da qasaita.......amma kasan meye tamim?" Yayi tambayar yana duban fuskarsa yana kuma takowa zuwa gaban tamim din. Qoqarin gaske tamim yayi wajen maye murmushi saman fuskarsa.
"Na rasa wanne dalili ne ya sanya uwargijiyarka ta zaboni a cikin tarin matasan qasar Ethiopia.....a baya nayi tunanin don tana mahaifiyata ne,amma a yanzu tunanina ya gagara cafko komai" Almaz yayi maganar da tarin mamakin dake ransa daya bayyana cikin muryarsa.
Murmushi tamim ya saki,yana takawa a hankali gaban wani babban glass cup daya cikashi da tataccen lemon inibi wanda ya cakudashi da sinadarai daban daban.
"Kaidai ungo wannan kasha mu tafi.....yanzu ba lokaci bane na tunanin wannan.....tunda harka yadda ka shiga cikin masu sa'a ai shikenan,ba abinda ya rage maka saika zuba idanu kaci gaba da irgen lokutan sa'arka". Dan shuru almaz din yayi,kafin kuma ya saki murmushi yana miqa hannunsa ya karbi lemon hannun tamim din.
"Inason lemon nan sosai,inajin dadinsa" Ya furta a hankali sannna kuma yakai cup din bakinsa.
Tas ya shanye lemon a kurba daya,sannan ya miqawa tamim cup din yana cewa.
"Kamar zai bani freshness din da nakeso,na gode tamim" Ya damqa masa cup din yana juyawa. Da wani kalar shu'umin murmushi yabi almaz din,rabin aikinsa ya kammala saura rabi,yana duban takunsa da yakeyi cikin wani yanayi daya bayyanar da b'urbushin qasaita.
"Matsiyaci ya samu guri,wai har ya iya yanayi na masu mulki da saruta" Ya fada a fili can qasa yana jifan hanyar da almaz yabi da harara.
Jerin gwanon motocin alfarmar guda shida ne cass suka takewa motor din da almaz ke ciki baya. Ya saki wani irin murmushi sanda dukkan wani hadi dake cikin lemon ya fara zagaya sassan jikinsa,ya kuma soma jinsa a sama,uwa uba yadda yaga manyan motocin alfarma irin wannan na take masa baya sai ya sake sanya yanayin yabi jikinsa sosai
"Shege almaz,yau shine kamar gomna?" Ya tambayi kansa da kansa yana dariya. Sam a rayuwarsa ya rayu cikin wani madaukakin yanayi ba burinsa bane,damuwarsa daya shine ya rayu cikin 'YANCI. Bayason UMARNI,yafison ya rayu cikin sakewa da kuma zabawa kansa duk kalar rayuwar da yakeso,ba tare da an bashi umarni ba,ba tare da an sanyashi ko an hanashi ba. Ya sani......yanajin wata izza da girma a cikin jininsa da baisan wacce iri bace,wannan ya sanya sau tari yafi zabar kebance kansa tare da qin amincewa ya shiga taron jama'a.
Duba daya tamim yayi masa ya tabbatar ya fara fita daga hayyacinsa,ya fara buguwa,sai ya gyara zamansa sosai yana dubansa.
"Kasan meye almaz?" Kai ya girgiza yana duban tamim da idanun nan nasa da tamim din yake ganin suna masa kama da wasu idanu.
"Akhnan matarka.....tana da tsananin girman kai....bata girmamawa kowa saboda tana ganin mahaifinta shine sarki a wannan yankin....."
"Ashe?" Almaz ya fadi da wata irin murya yana bude idanunsa da kyau. Kai tamim ya jinjina cikin bashi tabbaci da son isar da saqonshi
"Qwarai da gaske.....kai baka lura ba?,a matsayinka na namiji kuma mijin dake aurenta.....ta taba gaidaka?,kota taba zuwa gurinka nemanka?,kota taba nemanka din koda a waya ne?" Shuru almaz yayi,wasu abubuwa suna cakudewa cikin kansa tsakanin maganganun tamim da kuma abinda tamim din ya bashi yasha. Gefe daya wata izza tana huruwa cikin ransa,yana jin kansa yana girma da fadi.
"Ba ko daya" Almaz ya fada muryarsa tana kaduwa da wani irin yanayi na wanda ya fara buguwa.
"Ahto....to kai kuma saika bari aci gaba da tafiya a haka?"
"Inaaaa......daga yau zan fara nuna mata ina da iko a kanta" Ya fada yana ji a ransa dole ya zama tsayayyen namiji.
A hankali tamim ke buda masa wasu abubuwa,yana kuma sake karanta masa abubuwan da ya tabbatar zasuyi tsananin tasiri a kansa game da akhnan din. So samu komai ya fada jagule musu a yau,shi yasa ya fara da horashi da kadan daga cikin kayan mayen dana tanada,wanda wannan shine zai bashi damar dorawa kan tsarinsa d'od'ar ba tare da sunansa ko alamar ayar tambaya ta hau kansa ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/2, 22:22] +234 903 768 6798: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 54*
Idanu mammina ta lumshe tana kuma budesu idon nata akan akhnan din. Duk da yanayin da take ciki ba abinda ya gusar da wannan sassanyan kyan......wannan kyan irin na safeena......wannan kyan da ya zamewa rayuwarta dukka qalubale da baqincikin da har kawo yau ba wani abu daya sassauta a ranta. Wannan kyan tana fatan lokacin gushewarsa ya zama a kurkusa.......a shafe tarihinsa cikin qasar agadez. Shi ta yaya ma wai zata bari AKHNAN ta fita daga tasarrufinta?. Ta yaya zata yarda tabar ruhin safeena ya kwanta lafiya cikin kusewarsa?. Yadda ta sanya darare da yawa na rayuwarta suka gagara zuwan mata da dadi,haka takeso tayita rasa nata dararen a qasan kushewa cikin baqinciki da takaici.
A zahiri hannuwan akhnan din ta kamo a tausashe,har yadda tayi din ya sanya akhnan duban idanunta,tashin farko kuma ta hangi wannan tsantsar qaunar da kulawar data saba gani a tare da mammina din.
"Ina cikin tsananin farinciki yau biftu,kinsan saboda me?" Kai ta girgixa a hankali.
"Yadda naji sultane yana jero miki addu'o'i na sanya albarka cikin masallacin haram. Yadda sultane ya nunamin duk wani fushi da yakeyi da ke ya kau,yadda sultane ya nunamin ya.yafe miki,kuma a yanzun kin koma akhnan dinsa ta tun tale tale" Wata nannauyar ajiyar zuciya ta saki tana jin wani nauyi dake kwance a qirjinta yana raguwa. Wani sanyi taji gami da sassauci yana sauka saman zuciyarta,sai takejin wani girma da qaunar mammina suna saukar mata. Duk wani kyakkyawan albishir na alkhairi daga bakin mammina take fara jinsa,ita daya ce take dauke da dukkan wani albishir me dadi da zai faranta rayuwarta da duniyarta.
"Amma kinsan wasu lokutan nakanji nadama tana saukarmin na hadaki da almaz?" Ta furta muryarta can qasa tana kuma sadda kanta qasa jikinta yana nuna wani irin mugun laushi da yayi.
"Mammina......nadama wacce iri?" Ta tambayeta tana jin wani fargaba kadan. Kai ta daga tana sake kallonta.
"Nayi wannan abunne don na samar miki da 'yancinki,ki sake cikin rayuwarki kamar yadda kikeso,amma abun mamaki shine.....sai walwalarki take raguwa,takura take maye gurbin sakewa,me yayi zafi biftu?,bayan a yanzunne kike da 'yancin yin kowacce rayuwa da kike so?" Kai ta girgixa a hankali,tana jin wannan raunin nata da bata bari kowa ya gani yana taso mata.
"Ban saba bane mammina.....a hankali zan saba zan saki jikina".
" Amma ko kinsan wannan rashin sabon naki yana aje ayar tambaya me yawa saman zuciyar mutane a kaina da kanki?......kinsan yau ne ranar da za'a rakaki kwanan gida?" Kai ta daga da sauri ta zubewa mammina wadannan blue eyes din. Karon farko da mammina taji kalar kallon akhnan din ya mata nauyi gami da haifar da wata jaririyar faduwar gaba.
"Mammina.....kwanan gida?.....ni da almaz?" Ta furta da sigar tambaya me wani irin nauyi.
Kai ta jinjina mata cikin bata tabbaci,sannan tace.
"Haka yake a al'adar buzaye......haka yake tun kaka da kakanni,indai baso kike ki fadawa duniya cewa almaz ba zabinki bane". Shuru akhnan tayi,wai tana qoqarin daidaita kanta tana kuma qoqarin daidaita abinda takeji a qirjinta. Wani kwana ne da amarya zatayi guda daya tal a gidanta da ango,sannan washegari ya rakota ta dawo gidansu,sannan a sake shiryata a maidata.
Kai ta shiga girgzawa don ta kasa tausar zuciyarta ta karbi maganar. Sam ba zata iya ba......ba zata iya bin kowacce al'ada da akazo da ita ba wai akan aure,to a wanne dalili ma?,auren da dole ce ta kaita ga yinsa,dolen amintar da sultane da maido kyakkyawan alaqansu ta baya.
"Bazan iya ba mammina.....ba,bazanje ba,ko sama da qasa zata hadu bazanje kwana da almaz gida daya ba a yanzun,qarshen satinnan zan wuce Niamey,bana buqatar wani tsari da zai sanya yace zai bini,ko ke kice saimun tafi tare". Numfashi mammina ta sauke a hankali,dama ta sani,tasan za'a rina,kuma dama itama bata shirya tilastata kwana gida tare da almaz ba,to amma kuma tafiya Niamey bata hangen wani abu da zai sanya ta rushe tsarin tafiyarsu a tare.