← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 101

Sashe 76

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka kawai ta zabi yin shawagi a yau cikin masarautar kamar yadda ta saba a lokuta masu yawa. Irin hakan yana zama wani salo ne a gareta na fahimtar kowa da komai ba tare da yanayinta ya nuna ba. Takanyi noticing yawan adadin baqin dake masarautar ba tare da tayi magana da kowa ba,saidai a yanzun ta sani ba wata baquwar fuska cikin masarautar,don wancan malamin yayi limiting na komai.

Tafisu na biye da ita a hankali sunayin nazarinsu a tare ba tare da wata hira a tsakaninsu. Wannan yanayinne ya sanya kowa ke zaton ba shaquwa ba kuma kyakkyawar mu'amala tsakaninta da tafisu din.

"Ina yaiwata mafarkin Ethiopia......ina yawan afkawa cikin tunaninta koda banso hakan ba,bana jin akwai sauran aminci a nan gurin tafisu,haka zuciyata da jikina suke bani" Murmushi kadan tafisu ta saki tana girgiza kai.

"Nafi zaton kwadayin cikar burinki ne yake sakaki a irin wannan yanayin. A nan din uwargijiyata......babu wani abu daya isa ya karya amincin da kike dashi,ba wanda ya isa ya tsallake iyakokin da kika shata......ba wani abu komai girmansa da ya isa ya girgizaki ko ya girgiza darajarki da martabarki. Anya kina da masaniyar irin girma kima da amincin da kike dashi kuwa a zukatan talakawa?". Maganganun tafisu sun shigeta sosai.

"Kin manta cewa ke a yanzun ba halak malak din qasar Ethiopia bace ke?,ke din ba'abzina ce haifaffiya uwa uba da dangi gaba daya?,kin samu wannan shaidar ta hannun mutum mafi girma daraja da kuma aminci irin sultane,kin manta ne?" Tafisu ta sake tuna mata da wani abu daya sake bata relief.

"Kamar isowar tamim nake gani" Tafisu ta furta qasa qasa tana duban gabansu.

"Shine.....gwara daya iso,dama yau ne rana ta qarshe cikin yarjejeniyarmu......mu qarasa can" Mammina ta fadi yana sauya akalarta zuwa wani amintaccen gurin zama daya zama kebantacce garesu kadai da kuma sultane.

Idanunta akan tamim sanda yake takowa da wannan qaqqarfan jikin nasa,tana karantar wani yanayi a tattare dashi da bata saba gani ba.

Cikin girmamawa ya qaraso,ya kuma zube a gabanta kamar yadda ya saba din da tarin girmamawa.

"Bani labarin dukkanin abinda yake tafe dakai.....ba saura jira ko doguwar shimfida" Ta buqata cikin zaquwa da ganin yanayinsa.

Qasa yayi da kansa,yana jin wata fargaba tsakiyar qirjinsa da baisan dalilinta ba.

"Akwai alamun kwancewar wani noti guda daya cikin notikan da muka daure" Kai tsaye ta fahimci inda maganan ta dosa,wani irin abu taji yayi yarrrrr cikin jikinta,tsigar jikinta tayi wani irin zubawa,ta ritsashi da ido sosai.

"Bani bayanin a bude". Zama yayi sosai a qasa yana sake yin qasa da kansa.

"Akwai mutum daya da gilmawarsa ta qaranta cikin hukumar......akwai mutumin da aka dauki wasu satittika da kwanaki ba'a ganshi ba......bacewar motsin daya daga cikin ma'aikata kuwa a wajen yana alamta tafiyarsu izuwa wani muhimmin aiki,bacewar kowa a cikinsu bazai iya zama barazana ba.......amma BACEWARSA shi din babban barazana ne da zai iya tarwatsa KOWA!......An tabbatar min indai shidinne.....to ba shakka SHI KADAI GAYYA NE!!!"

"Dakata!!!!" Mammina ta fada cikin tsawa.

"Daina kurantamin kowanne mutum a gabana,ka manta a gaban wa kake?". Qasa yayi da kansa,haka kawai yana jin wani rashin nutsuwa yana shigarsa.

" A bani tabbacin gurbin da ake tunanin ba kowa da gaske ba kowa din?.....muddin ya sanya qafarsa cikin agadez ne.....muddin ya sanya qafarsa cikin masarautata ne.......saina sanyashi yayi nadamar binciko laifin daya daga cikin mutanena ma ballantana ni da kaina......tabbaci nake buqatar samu da farko tukunna!!.....ka riqe wannan da kyau.....sati daya tak na baku,duk kuwa wahalar da aikin ke dashi,bazan iya jira sama da kwanaki bakwai ba".

"An gama" Tamim ya furta yana miqewa da cikakken karsashin nan nasa yana barin gurin.

Kasa motsawa tayi kwata kwata daga gurin,saita dinga jin wani abu yana shigarta gaba daya me kama da fargaba da razani.

"Bai kamata kiji komai ba,bai kamata ki dinga mantawa da cewa ke ba jinin Ethiopia bace.....bai kamata ki dinga mantawa da al'adar agadez ba game da gwiwar sarki,ke din kina cikin kariyar sultane da alfarmar masarauta HAR ABADA!" . Wadannan kalaman na tafisu su suka suka shiga jikinta da kyau,wadannan kalaman su suka binne tsoron da yaso yayi tasiri a zuciyarta.

*MORSA SAFIYYA*

A nutse take gyara lullubin lafayar dake saman kanta,tana kuma sake duban fuskarta a madubi. Fuskar da wasu lokuta suke tuna mata mutum biyu da har yanzu bata maye gurbinsu ba a rayuwarta duk da tsahon shekarun. SAFEENA DA KHADEEJA.

Motsa qofar da akayi shi ya sanyata waiwayawa. Armelle ce cikin kamalar nan tata.

"Allah ya baki yawan rai,an kammala shirya komai,kuma sunce sheikh yana hanya,amma kuna falaak da hairaan suna buqatar ganinki".

"Ki fadi musu su shigo" Kai armelle ta jinjina ta koma da baya.

A nutse ta koma saman ottoman ta zauna tana fuskantar qofa. Daidai sanda hairaan ke shigowa a gaba falaak na biye da ita a baya,hairaan din riqe da hannun falaak.

Cikin kwanaki qananu falaak din tayi wani fayau da ita,daga jiki har fuska sun nuna ramarta. Sau daya tak momma ta qara ganinta tun wancan ranar,duk da zuciyarta cike take da tausayin autar tata amma ta danne,saboda bata son komai da zai kawo mata cikas a tsarinta da qudurinta har sai ta cimmasa. Ta shirya fuskantar kowa......ta shirya qalubalantar kowa,koda kuwa sultane ne,shi yasa koda nanny batayi maganan komai ba,duk da awannin da suka shafe ita da nanny din suna tattaunawa game da sakin.

"Ina fata ba zuwa kukayi ku batamin lokaci ba" Morsa ta fada tana wani hade rai. Murmurshi kawa hairaan ta saki.

"Inamu ina batawa morsa kuma momma guda rai?....neman afuwa da yafiya kawai mukazo yi" Hairaan ta fadi tana sakin falaak,wadda bata zame ko ina ba sai gaban morsa safiyya.

Sulalewa tayi ta zauna a gabanta tamkar me zaman sallah,muryarta can qasa da wani irin rauni ta soma magana kanta a qasa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Momma ki yafemin.....kiyi haquri momma,na gaza ganowa da fahimtar nufinki,duk da cewa nice na miki alqawarin tallafa miki da bada gudunmawata wajen gyara rayuwar yaa biftu,kiyi haquri bisa musun da nayi miki,kiyi haquri kan bata miki ran da nayi.....gaskiya ne da kikace yaa biftu ta fini buqatat sheikh haisam.....da gaske ne momma na yarda da hakan,ni ina iya ganinki,ina iya rabarki naji duminki.....ita kuwa ta rasa hakan,ni ban rasa gatan wanda zai dorani akan hanyar da rayuwata zata inganta ba ta kuma kubuta,amma ita ta rasa wannan.....na SADAUKARWA da yaa biftu sheikh da dukka soyayyar da nake masa,na sadaukar mata momma.....zan kuma goya miki baya ganin komai ya daidaita" Wasu hawaye ne suka taru sosai a idanun morsa safiyya,duk kuma yadda takai ga taresu amma sai hakan ya gagara,don haka ta barsu suka zubo da duminsu gaba daya,suka kuma sauka kan hannuwan falaak dake saman cinyarta,abinda ya sanya falaak din kama hannun morsa din ta saka cikin nata ta runtseshi sosai.

Hannunta ta aza kan falaak a hankali tana dauke hawayen da gefan lafayar jikinta.

"Ba abinda kikayimin falaak,Allah yayi miki albarka.....Allah yayi miki albarka....Allah yayi miki albarka,tabbas ina me yaqini da tabbacin ba zaki tozarta ba,ba shakka Allah sai ya maida miki madadin sheikh haisam,ina miki fatan ya zama a kurkusa ta yadda zuciyarki ba zata cika da kadaici ba,ba kuma zata tagayyara ba,soyayyar da baki hasashen samunta gurin sheik ba alfarmar manzan Allah S A W zaki sameta gurin makwafinsa har sai kinji kamar tayi miki yawa ma,Allah ya cireshi daga zuciyarki kaman yadda yake fidda gashi daga nono,ya mantar dake soyayyarsa ya cikata da qaunar Allah da manzansa dama dukkan wanda zai zama madadinsa" . Qanqame morsa safiyya tayi da kyau,tun daga nan tasan cewa addu'ar UWA ba wasa bace,wani sanyi taji yana ratsa zuciyarta,wata nutsuwa ce taji tana saukar mata,sabanin kwanakin data dauka cikin qunci da jin cewa ba zata iya barwa kowa haisam din ba. Sai hairaan ta matso itama tana cuso kanta a tsakaninsu hawaye fal nata idanun. Morsa safiyya tasan me take nufi,qarin sanya albarka itama take nema,don haka ta saki murmurshi tana shafa kanta itama gami da kwararo mata addu'a. Koda ta kammala bataji ta nutsu ba,hannuwanta ta daga tana yiwa akhnan tata daban,duk da batasan me akeyi bama,amma bata taba daga qafa ba akan mata addu'a,ko ta yiwa yaranta ko batayi musu ba.

(Duk runtsi duk wuya a nemi addu'a da albarkar iyaye,karku yadda kuyi wasa da ita,wata dama ce da idan ta wuce bata dawowa kowa,idan sun rasu ka kyautatawa 'yan uwansu da qawaye da abokansu,hakan zai zama tamkar su ka kyautatawa,haka addini ya koya mana,haka yake a addininance,Wanda suka rasa nasu Allah ya jiqansu da rahama,wadanda kuma suke raye ubangiji ya qara musu lafiya da nisan kwana me amfani).

*HAISAM*

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/6, 19:28] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 68*

*HAISAM*

Qasan ransa yakejin dadi da sassauci na yadda ya samu gidan komai yana tafiya daidai da umarnin da yake bayarwa daga can ainihin gidansa. Wannan girman.....wannan martabar da kowa ke bashi ba abinda ya sauya sai sake qaruwa ma da yayi. Cikin girmamawa da martaba dan adam daya gada daga ainihin jinin OROMIA na asali yake amsa kowa gami da duba matsayar kowa a aiki da yadda kowa ke tsaye akan aikinsa.

Baiyi hanzarin wucewa kai tsaye zuwa sassansa ba,sai ya zabi ya qarasa mintunan da suka rage wajen duban tsaron gidan da sauransu.
Chapter 76 · 0% Book details