Sashe 48
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hmmmm" Akhnan din ta fadi d wani abu me nauyi da taji yana sauka cikin qirjinta,sannan ta maida dubanta ga qofar,wasu abubuwa suns yawo gami da kutsa kai cikin tunanikanta.
"Biftu.......shin bake kika zabi almaz ba?.....auren almaz zakiyi fa?,zabinki" Shehnaz ta fada tana dora hannunta saman cinyar akhnan din.
Akwai alamun shakka da kokwanto cikin muryar shehnaz,abinda ta tabbatar yana cikin sharadinsu da mammina,don haka ta sake juyowa tana duban shehnaz din
"Don ni na zabi almaz......ba hakan yana nufin ra'ayina zai sauya ba......ba abinda zabin ya zamemim face zallar qasqanci.....kamarni zaya karbi sadakina da wasu tsirarun sulalla?" Tayi maganan tana nuna kanta da yatsarta,da alamun bacin ranta ya sake motsuwa.
"Kuka zaki masa biftu?" Shehnaz ta furta a hankali bayan ta gama qarewa qwayar idanun akhnan kallo wadda ta hada ruwan hawaye daya sanya qwayar idanun nata qara qyalli.
"Jamais de la vie(Allah ya sawwaqe)" Ta fadi tana jifan shehnaz da harara kamar wadda ta yiwa fatan mutuwa. Yadda tayin ya sanya shehnaz sakin wani qaramin murmushi. Batasan me yasa ba,batasan kuma me ya faru ba.....izzarta bata barinta nuna jin zafin abubuwa,ba'a mata ma abinda zataji zafin ballantana ta nuna,amma yanzun.....tashi daya.....lokaci daya gaba daya sheikh haisam din ya birkita tunaninta,ya dagula lissafinta,ya sanyata tanajin zafi dama haushin komai.......ME YASA?. Tambayar da shehnaz ta yiwa kanta kenan sanda akhnan take tattara ya nata ya nata. Ta tabbatar daki zata canza,wannan din kuma salonta ne,dabi'arta ne idan suka bata mata rai ita da aisa,ko sukayi mata zancan da bata so. Sai batace mata komai ba,bata kuma hanata fitan ba,don tasan zai wahala ta iya kwana ita daya yadda ake tsula ruwannan,duk kuwa da cewa wani irin kurman gini ne da bakajin qara ko sautin saukan ruwan,saidai kuma baya hana walqiya ratsowa har inda kake,mafi girman abinda akhnan din tafi tsoro kenan.
"Kiyi qoqari ki tashi da wuri,don gobe ne naji nanay tana maganan za'a fara gyaran jiki" Ta gayawa akhnan din cikin daga murya kadan tana boye dariyarta can qasan ranta. Ita abun su
Inda ace tana da sauran energy a tattare da ita,a yau din zata tsaya ne suyi abinda ta jima bata yishi ba,tabbas da sai an shiga tsakaninsu da shehnaz,to amma ba wannan ba......kowacce gaba ta jikinta ba abinda take buqata sai KADAICI da KEBEWA.
*HAISAM*
A tsaye kawai maleek din yake rungume da hannayensa daya riqe lallausan towel a tsakiyarsu yana kallon yadda haisam ke zare jiqaqqun kayan jikinsa yana zubesu saman sofa bed.
Dukkan wani motsi na haisam din maleek yana biye dashi,har zuwa sanda ya rage fara qal din vest din jikinsa,ya juya a nutse yana laluben towel sai maleek ya daga masa na hannunsa yana duban qwayar idanunsa da bai kalli kowa dake tsaye carko carko ba tun a parlor.
Fararen manyan idanunsa da suka sauya launi kadan ya daga ya kalli maleek din,sannan ya miqa hannu ya karbi towel din,sai maleek ya sakar masa ba tare da yace masa komai na,shima ya karba yana juyawa a nutse ya nufi toilet.
Ajiyar zuciya me nauyin gaske maleek ya saki,ya jinjina kai a nutse ya tsugunna ya kwashe kayan haisam din. Yaga abinda yakeson gani din,wani irin fushi ne kwance cikin idanun haisam,irin fushin da akan samu jikin jinin SARAUTA saboda wata dabi'a ta rashin son raini dake tattare da wannan jinin wanda irinsa ne a jikinsa shi da haisam. Wannan ya sanya sau tari yafi kowa saurin fahimtar haisam.....saboda wasu irin dabi'u da jini kusan irin daya ke zagayawa a jikinsu.
Abinda yake gani a idanun haisam a yanzun me zurfi da girma ne,irin abinda bai taba gani ba a idonsa akan kowa. Ya tabbatar dukka shurun da yayi da qoqarin kaucewa hada ido da kowa yana yine cikin yunqurin controlling kansa fushinsa da kuma bacin ransa. Yayi imanin inda ba tasiri na ilimin zamantakewa da addini a tattare dashi......akhnan din zata gane girman kuskuren data tafka Kai tsaye. Yana YAKANA yana da DAUKE KAI......amma a duk sanda qura takai bango yana da wahalar sarrafuwa yana kuma da wuyar sha'ani. A mganganunta yasan ta tabo abu mafi girman da yafi tsanar a taba masa ADDININSA,dole yasan fushinsa yana iya fin haka ma. Yana kammale masa kayan ya taka a nutse yana ficewa a dakin don ya bashi daman shiryawa da daukan adadin lokutan da yaga sunyi masa.
Bai jima ba sosai ya fito ya fara shiryawa,yana shiryawan yana ambaton sunan Allah don neman agaji da samun sassaucin dacin da yakeji tun daga harshensa zuwa cikin maqogoronsa. Yanata qoqarin manta maganganunta,amma koda ya cillasu baya saisun dawo masa cikin kansa.
"Subhanallah" Ya fadi a hankali lokacin daya kammala fesa wannan mayen turaren nasa ya ajiye bottle din saman madubi. Tafin hannunsa ya sanya ya shafa qirjinsa har sau uku yana furta addu'ar sassauta fushi da bacin rai. Baisan me yake samunsa ba a kwanakin nan.....baisan me yasa a kanta fushinsa yake yawa ba.....baisan me yasa kome tayi yake bata ransa fiye da yadda ya kamata yaji ba.
Yayi iyakacin bakin qoqarinsa na kaucewa kowanne shirgi nata,don ba dominta ya shigo AGADEZ ba,ba zamanta yakeyi ba.....bata kuma cikin lissafin mutanen da yake hangen bincikensa zai iya wucewa ta kansu,amma kuma baisan me ya sanya lamuranta ke sake shiga cikin rayuwarsa ba.
Duk yadda yakai ga yakicewa da dojewa amma sultane yana sake jawoshi da sakashi cikin al'amuranta......banda girmamawa ga sultane sam baiga hadinsa da karbar sadakinta da kuma zamowa waliyyinta har ya daura mata aure ba.
Komawa yayi ya zauna a hankali gefan sofa bed din yana sake maimaita addu'ar. A hankali a hankali yaji yanayinsa yana daidaituwa,fushin kuma yana raguwa,sai ya miqe a hankali ya soma takawa bayan ya sanya flip flops dinsa masu tashin gaske,don kawai fitowar ta zama dole saboda maleek da omar da yasan ba gidan zasu kwana ba.
"Nifa na kasa jurewa......batasan gonar da take shiga bane?......inda a Jimma ne tana zaton shekara daya ma ta isheta ta samu daman tsaiwa kawai a gabansa......iya tsaiwa kawai obbo maleek,bare harta samu daman fadin maganganu masu zafi?" Abdii dake balbalin fada ya fadi yana nuna yatsarsa ga maleek dake zaune hankali kwance yana shan coffee dinsa,da alama kuma ya tattara dukka hankalinsa akan abdii din daketa zirya yana fada.
Murmushi omar ya saki yana ajiye remote din hannunsa daya dauka don kashe Ac din parlor din
"Ina hakaitota ni kaina cikin masarautar jimma........rashin sani yafi dare duhu,inda cikin jimma ta fadi wadannan maganganun data zama nama".
"Da ba zata sake rashin kunya a duniya ba.....da tasan ba'a tabawa oromian prinsii dinsu.....amma nan gaba sai......". Cikin tarin nutsuwarnan tashi ya saki gyaran murya sannna ya zagayo yana zaban kujerar zama.
Tuni abdii ya kama kanshi,kai kace ba shine yaketa surfa bala'in nan ba. A hankali ya zauna saman kujerar a lokaci guda kuma yana aikewa abdii wani kallo daya sanya abdii din diriricewa,lokaci guda kuma ya miqe yahau hadowa haisam coffee ba kuma don ya buqaci hakan ba,sai don nauyin da idanu da kuma kallon da haisam din ya jefeshi dashi ya sanyashi qaramar rudewa.
Parlor din ya dauki shuru,cikinsu ba wanda ya sake cewa komai,har zuwa abdii ya kammala hada coffee din ya kawo gaban haisam din yana cewa.
"Obbo....."
"Zauna nan" Haisam ya fadi kai tsaye cikin salon umarni. Bai musa ba ya zauna din,saidai ya kasa hada idanu da Haisam din kai tsaye.
"Morning flight evening flight or night flight......wanne ka zaba don komawa Ethiopia kuma jimma?". Idanu abdii ya zaro yana qoqarin duban haisam da yakai cup din coffee bakinsa a nutse
"Obbo......ni bance zan koma gida ba,idan nabar niger obbo tare dakai ne".
"Kace mana abdii?"
"Lakki(a'ah)" Abdii ya fada yana girgiza kai.
"Meye alaqarka da dabbar da ba ita ka shigo farauta ba daji?,koda zata yita bibiyarka a baya?" Ya jefa masa tambayar yana ajiye mug din hannunsa.
"Babu obbo"
"Ergamni keenya maali?(meye mission dinmu?)"
"Obbo......zaqulo mutumin daya kashe ajani,sannan mu kaishi gaban hukumar binciken sirri qasar Ethiopia kuma ta hukuntashi" Kai ya jinjina a nutse yana lumshe idanunsa gami da budesu.
"Daga sanda kaji a ranka ka fara sauka daga wannan ra'ayin,to daga ranar ka siyi tikeetii(ticket)na komawa Ethiopia....banzo AGADEZ don susan waye ni ba......na yarda na zama mutum mafi qasqanci a idanun kowa muddin hakan zai zama tsani zuwa ga cikar burinmu......"
"Kamar ba komai zaka iya dauka ba kaima daga gurin yarinyar ba.....kamar tana jin kanta tana da Kyau......maza suna layin mutuwar sonta tana wahalar dasu....."
"Omari,Dhaabadhaa(stop it)" Yatsunsa ya saka yayi zipping bakinsa alamun yayi shuru,sai ya kalli maleek yana daukan nasa mug din ya zauna gaba kadan dasu yana fadin.
"buna keessan xumurree,nuti ni deemna(idan ka gama shan coffee din sai mu tafi)".
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kamar kowacce magana ta qare,amma can qasa maleek ya zare mug dinsa daga bakinsa yana duban haisam.
"Rayuwarta na kewaye da hatsari haisam.....daidai ne ka kauda kai?" Maleek din bai zaci samun amsa daga gurinsa da wuri ba,amma kafin ya maida cup dinsa bakinsa sai yaji yana fadin.
"Ani lubbuu namoota koo fi warra koo baraaruuf qofa dhufe(nazo nan ne kawai don ceton rayuwar jama'ata data iyayena)......haqqin kareta ko daukar nauyinta ba'a wuyana yake ba" Ya qarasa fada yana dire mug din gami da daukar remote ya fara canza tasha.
"But she's so strong fa.... Omari ka kula kuwa?" Ya kira sunan omar din yana kanne masa ido daya.
"Indeed......" Omar ya fada yana qoqarin qara wani abu,saidai haisam.ya kira sunansa da sound dinnan da dukkaninsu sunsan idan yayi irin wannan kiran me yake nufi. Hannayensa zube a aljihun trouser din jikinsa,still idanunsa kan TV da suke program kai tsaye da sheikh Dr zaakir naikh.
*MAMMINA*
"Biftu.......shin bake kika zabi almaz ba?.....auren almaz zakiyi fa?,zabinki" Shehnaz ta fada tana dora hannunta saman cinyar akhnan din.
Akwai alamun shakka da kokwanto cikin muryar shehnaz,abinda ta tabbatar yana cikin sharadinsu da mammina,don haka ta sake juyowa tana duban shehnaz din
"Don ni na zabi almaz......ba hakan yana nufin ra'ayina zai sauya ba......ba abinda zabin ya zamemim face zallar qasqanci.....kamarni zaya karbi sadakina da wasu tsirarun sulalla?" Tayi maganan tana nuna kanta da yatsarta,da alamun bacin ranta ya sake motsuwa.
"Kuka zaki masa biftu?" Shehnaz ta furta a hankali bayan ta gama qarewa qwayar idanun akhnan kallo wadda ta hada ruwan hawaye daya sanya qwayar idanun nata qara qyalli.
"Jamais de la vie(Allah ya sawwaqe)" Ta fadi tana jifan shehnaz da harara kamar wadda ta yiwa fatan mutuwa. Yadda tayin ya sanya shehnaz sakin wani qaramin murmushi. Batasan me yasa ba,batasan kuma me ya faru ba.....izzarta bata barinta nuna jin zafin abubuwa,ba'a mata ma abinda zataji zafin ballantana ta nuna,amma yanzun.....tashi daya.....lokaci daya gaba daya sheikh haisam din ya birkita tunaninta,ya dagula lissafinta,ya sanyata tanajin zafi dama haushin komai.......ME YASA?. Tambayar da shehnaz ta yiwa kanta kenan sanda akhnan take tattara ya nata ya nata. Ta tabbatar daki zata canza,wannan din kuma salonta ne,dabi'arta ne idan suka bata mata rai ita da aisa,ko sukayi mata zancan da bata so. Sai batace mata komai ba,bata kuma hanata fitan ba,don tasan zai wahala ta iya kwana ita daya yadda ake tsula ruwannan,duk kuwa da cewa wani irin kurman gini ne da bakajin qara ko sautin saukan ruwan,saidai kuma baya hana walqiya ratsowa har inda kake,mafi girman abinda akhnan din tafi tsoro kenan.
"Kiyi qoqari ki tashi da wuri,don gobe ne naji nanay tana maganan za'a fara gyaran jiki" Ta gayawa akhnan din cikin daga murya kadan tana boye dariyarta can qasan ranta. Ita abun su
Inda ace tana da sauran energy a tattare da ita,a yau din zata tsaya ne suyi abinda ta jima bata yishi ba,tabbas da sai an shiga tsakaninsu da shehnaz,to amma ba wannan ba......kowacce gaba ta jikinta ba abinda take buqata sai KADAICI da KEBEWA.
*HAISAM*
A tsaye kawai maleek din yake rungume da hannayensa daya riqe lallausan towel a tsakiyarsu yana kallon yadda haisam ke zare jiqaqqun kayan jikinsa yana zubesu saman sofa bed.
Dukkan wani motsi na haisam din maleek yana biye dashi,har zuwa sanda ya rage fara qal din vest din jikinsa,ya juya a nutse yana laluben towel sai maleek ya daga masa na hannunsa yana duban qwayar idanunsa da bai kalli kowa dake tsaye carko carko ba tun a parlor.
Fararen manyan idanunsa da suka sauya launi kadan ya daga ya kalli maleek din,sannan ya miqa hannu ya karbi towel din,sai maleek ya sakar masa ba tare da yace masa komai na,shima ya karba yana juyawa a nutse ya nufi toilet.
Ajiyar zuciya me nauyin gaske maleek ya saki,ya jinjina kai a nutse ya tsugunna ya kwashe kayan haisam din. Yaga abinda yakeson gani din,wani irin fushi ne kwance cikin idanun haisam,irin fushin da akan samu jikin jinin SARAUTA saboda wata dabi'a ta rashin son raini dake tattare da wannan jinin wanda irinsa ne a jikinsa shi da haisam. Wannan ya sanya sau tari yafi kowa saurin fahimtar haisam.....saboda wasu irin dabi'u da jini kusan irin daya ke zagayawa a jikinsu.
Abinda yake gani a idanun haisam a yanzun me zurfi da girma ne,irin abinda bai taba gani ba a idonsa akan kowa. Ya tabbatar dukka shurun da yayi da qoqarin kaucewa hada ido da kowa yana yine cikin yunqurin controlling kansa fushinsa da kuma bacin ransa. Yayi imanin inda ba tasiri na ilimin zamantakewa da addini a tattare dashi......akhnan din zata gane girman kuskuren data tafka Kai tsaye. Yana YAKANA yana da DAUKE KAI......amma a duk sanda qura takai bango yana da wahalar sarrafuwa yana kuma da wuyar sha'ani. A mganganunta yasan ta tabo abu mafi girman da yafi tsanar a taba masa ADDININSA,dole yasan fushinsa yana iya fin haka ma. Yana kammale masa kayan ya taka a nutse yana ficewa a dakin don ya bashi daman shiryawa da daukan adadin lokutan da yaga sunyi masa.
Bai jima ba sosai ya fito ya fara shiryawa,yana shiryawan yana ambaton sunan Allah don neman agaji da samun sassaucin dacin da yakeji tun daga harshensa zuwa cikin maqogoronsa. Yanata qoqarin manta maganganunta,amma koda ya cillasu baya saisun dawo masa cikin kansa.
"Subhanallah" Ya fadi a hankali lokacin daya kammala fesa wannan mayen turaren nasa ya ajiye bottle din saman madubi. Tafin hannunsa ya sanya ya shafa qirjinsa har sau uku yana furta addu'ar sassauta fushi da bacin rai. Baisan me yake samunsa ba a kwanakin nan.....baisan me yasa a kanta fushinsa yake yawa ba.....baisan me yasa kome tayi yake bata ransa fiye da yadda ya kamata yaji ba.
Yayi iyakacin bakin qoqarinsa na kaucewa kowanne shirgi nata,don ba dominta ya shigo AGADEZ ba,ba zamanta yakeyi ba.....bata kuma cikin lissafin mutanen da yake hangen bincikensa zai iya wucewa ta kansu,amma kuma baisan me ya sanya lamuranta ke sake shiga cikin rayuwarsa ba.
Duk yadda yakai ga yakicewa da dojewa amma sultane yana sake jawoshi da sakashi cikin al'amuranta......banda girmamawa ga sultane sam baiga hadinsa da karbar sadakinta da kuma zamowa waliyyinta har ya daura mata aure ba.
Komawa yayi ya zauna a hankali gefan sofa bed din yana sake maimaita addu'ar. A hankali a hankali yaji yanayinsa yana daidaituwa,fushin kuma yana raguwa,sai ya miqe a hankali ya soma takawa bayan ya sanya flip flops dinsa masu tashin gaske,don kawai fitowar ta zama dole saboda maleek da omar da yasan ba gidan zasu kwana ba.
"Nifa na kasa jurewa......batasan gonar da take shiga bane?......inda a Jimma ne tana zaton shekara daya ma ta isheta ta samu daman tsaiwa kawai a gabansa......iya tsaiwa kawai obbo maleek,bare harta samu daman fadin maganganu masu zafi?" Abdii dake balbalin fada ya fadi yana nuna yatsarsa ga maleek dake zaune hankali kwance yana shan coffee dinsa,da alama kuma ya tattara dukka hankalinsa akan abdii din daketa zirya yana fada.
Murmushi omar ya saki yana ajiye remote din hannunsa daya dauka don kashe Ac din parlor din
"Ina hakaitota ni kaina cikin masarautar jimma........rashin sani yafi dare duhu,inda cikin jimma ta fadi wadannan maganganun data zama nama".
"Da ba zata sake rashin kunya a duniya ba.....da tasan ba'a tabawa oromian prinsii dinsu.....amma nan gaba sai......". Cikin tarin nutsuwarnan tashi ya saki gyaran murya sannna ya zagayo yana zaban kujerar zama.
Tuni abdii ya kama kanshi,kai kace ba shine yaketa surfa bala'in nan ba. A hankali ya zauna saman kujerar a lokaci guda kuma yana aikewa abdii wani kallo daya sanya abdii din diriricewa,lokaci guda kuma ya miqe yahau hadowa haisam coffee ba kuma don ya buqaci hakan ba,sai don nauyin da idanu da kuma kallon da haisam din ya jefeshi dashi ya sanyashi qaramar rudewa.
Parlor din ya dauki shuru,cikinsu ba wanda ya sake cewa komai,har zuwa abdii ya kammala hada coffee din ya kawo gaban haisam din yana cewa.
"Obbo....."
"Zauna nan" Haisam ya fadi kai tsaye cikin salon umarni. Bai musa ba ya zauna din,saidai ya kasa hada idanu da Haisam din kai tsaye.
"Morning flight evening flight or night flight......wanne ka zaba don komawa Ethiopia kuma jimma?". Idanu abdii ya zaro yana qoqarin duban haisam da yakai cup din coffee bakinsa a nutse
"Obbo......ni bance zan koma gida ba,idan nabar niger obbo tare dakai ne".
"Kace mana abdii?"
"Lakki(a'ah)" Abdii ya fada yana girgiza kai.
"Meye alaqarka da dabbar da ba ita ka shigo farauta ba daji?,koda zata yita bibiyarka a baya?" Ya jefa masa tambayar yana ajiye mug din hannunsa.
"Babu obbo"
"Ergamni keenya maali?(meye mission dinmu?)"
"Obbo......zaqulo mutumin daya kashe ajani,sannan mu kaishi gaban hukumar binciken sirri qasar Ethiopia kuma ta hukuntashi" Kai ya jinjina a nutse yana lumshe idanunsa gami da budesu.
"Daga sanda kaji a ranka ka fara sauka daga wannan ra'ayin,to daga ranar ka siyi tikeetii(ticket)na komawa Ethiopia....banzo AGADEZ don susan waye ni ba......na yarda na zama mutum mafi qasqanci a idanun kowa muddin hakan zai zama tsani zuwa ga cikar burinmu......"
"Kamar ba komai zaka iya dauka ba kaima daga gurin yarinyar ba.....kamar tana jin kanta tana da Kyau......maza suna layin mutuwar sonta tana wahalar dasu....."
"Omari,Dhaabadhaa(stop it)" Yatsunsa ya saka yayi zipping bakinsa alamun yayi shuru,sai ya kalli maleek yana daukan nasa mug din ya zauna gaba kadan dasu yana fadin.
"buna keessan xumurree,nuti ni deemna(idan ka gama shan coffee din sai mu tafi)".
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Kamar kowacce magana ta qare,amma can qasa maleek ya zare mug dinsa daga bakinsa yana duban haisam.
"Rayuwarta na kewaye da hatsari haisam.....daidai ne ka kauda kai?" Maleek din bai zaci samun amsa daga gurinsa da wuri ba,amma kafin ya maida cup dinsa bakinsa sai yaji yana fadin.
"Ani lubbuu namoota koo fi warra koo baraaruuf qofa dhufe(nazo nan ne kawai don ceton rayuwar jama'ata data iyayena)......haqqin kareta ko daukar nauyinta ba'a wuyana yake ba" Ya qarasa fada yana dire mug din gami da daukar remote ya fara canza tasha.
"But she's so strong fa.... Omari ka kula kuwa?" Ya kira sunan omar din yana kanne masa ido daya.
"Indeed......" Omar ya fada yana qoqarin qara wani abu,saidai haisam.ya kira sunansa da sound dinnan da dukkaninsu sunsan idan yayi irin wannan kiran me yake nufi. Hannayensa zube a aljihun trouser din jikinsa,still idanunsa kan TV da suke program kai tsaye da sheikh Dr zaakir naikh.
*MAMMINA*