Sashe 46
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani bacin rai me nauyin gaske ya soma narke mata yana ratsa kowanne lungu da sashe na zuciyarta. Ta tabbatar tayi imanin yaji takun tafiyarta,kamar yadda ta fahimci akwai wani a gefansa dake tsaye tare dashi da yaji alamun tahowarta,amma yanayin tsaiwarsa bai canza ba ballanta yakai ga waiwayo inda take. Me ya dauki kansa?,me yakejin kansa?,wannan kadai yana sake tabbatar mata ya shirya yin hakanne don ya wulaqanta ya toxartata ya qasqanta matsayinta a duniya,a yau kuma taci alwashin saita maida wannan martanin a kansa,saita sanya yaji fiye da zafin da ita taji.
Tazara kadan ta rage a tsakaninsu,ta tsaya cak tana goye hannayenta a qirji gami da sake zuba masa idanu ta baya tana sake zurfafa kallonta a kansa. Taku hudu omari yayi yana basu space,space din dabai nesantashi da ji da ganin abinda ke faruwa ba.
Yaji tsaiwarta a bayansa,saidai yanajin kamar kusancin dake tsakaninsu yayi yawa,amma duk da hakan bai juya ba sai bayan wasu sakanni da suke sake tabbatarwa da akhnan shi din MA'ABOCIN GIRMAN KAI NE.
Bataga alamun zai juyo ba....bataga alamun yasan da wanzuwarta a gurin ba,haqurinta kuma ragagge ne da ba zata iya jiran reaction dinsa ba,duk da tarin izzar da take cinta sai ta sake goye hannunta sosai a qirjinta,cike da izza,cike da jin isa ta motsa labbanta,tattausar muyar nan da bacin rai ya yiwa murfi ta soma yawo cikin iskar dake kadawa tana isar da saqonta ga kunnuwansa.
"Wannan itace hanyar da malamai suke bi don qasqantar da daraja kima da martabar 'ya mace.......da bautar da ita cikin aure da sunan addini da kuma musulunci da irin son zuciya da qarairayinsu!" Sosai sautin maganarta ya zauna masa cikin kai da zuciya da wani irin dumi da yaji yana mamayar zuciyar tasa.
Numfashi yaja ya aika har cikin hunhunsa yana kiran sunan Allah can qasan zuciyarsa da neman taimako kada shaidan ya rinjayeshi,sai ya saki qarfen da yake dafe dashi ya waiwayo a nutse idanunsa suna sauka a kanta.
Guri daya idanunsu suka sarqe,ya sake zare dubansa daga kan fuskarta data bayyana tarwai ta siririyar walqiyar dake haskawa kadan kadan wadda bata dauke da sautin komai,wannan shi zai baka damar ganin yadda iska ke wasa da mayafin saman kanta,da sassalkan wani siririn gashinta me santsi daya ratso ta gefan kunnenta ya fito.
Yadda ya zare dubansa a kanta kamar kullum kamar yadda ta kula al'adarsa ce ya sake tunzurata. A koda yaushe yana nuna shi din wani tsarkakke ne wanda ita ta jima da sanin son zuciya da son rai da kuma fakewa bayan addini suna aiwatar da son rai da son zuciyarsu babu wanda yakai malami yin hakan. Wanna fusatar ta sanya ta qara taku biyu zuwa gabansa,tana son ta bambance me yakeji dashi da yake mata wani kallo sannan ya watsar ta hanyar janye idanunsa a duk sanda zasu hadu irin haka.
"Kana tunanin bada aurena wani abu ne me sauqi da wasu qananun sulalla marasa darajar da ko takalmin sakawa a qafar hadimaina darajarsa tafi ta wadannan sulallan?" Ta sake fadi cike da tsiwa numfashinta yana dagawa sosai ta saman qirjinta. Numfashi ya sake ja yana aikewa cikin gangar jikinsa yana jin wataqila wannan zai taimaka wajen controlling kansa da zuciyarsa.
"Wannan itace hanyar daka zaba wajen qasqantar da darajata?wajen gayawa duniya abace ni me sassauqar daraja?......darajar da baka isa ka samu kwatankwacinta ba?!" Ta sake tambayarsa tana sane takawa zuwa inda yake tsaye kamar ta manta da tana qara kawo kusanci ne a tsakaninsu.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Labarina.......sunana.....daukakata da darajata wani abun tattaunawa ne tsakanin manyan masarautu,ba na iya agadez kawai ba......dole sadakina da aurena ya bambanta dana kowacce d'iya dake jin asali da gata!.....bakasan hakan ba?" Ta sake tambayarsa,idanunsa na sake hange mata wani irin calmness a tattare dashi. Kaman ba ihu take masa ba.....kaman ba fada take masa ba,tunzura take so yayi.......tanaso yayi wani abu guda daya da zai sanyata ta yaga wannan rigar maluntar.....rigar mutuncin da yakejin yana sanye da ita.
Tarin rufewa da idanunta sukayi ya sanya ya gaza ganin yadda adams apple dinsa ke sama da qasa yana qoqarin tura duk wani yunqurin bayyana fusata da fushi da zuciyarsa ke qoqarin turawa saman fuskarsa. Zuciyarsa na wani irin motsawa da mugun qarfi,yayin daya sanya kalar nashu qarfin yana danneta da dukka iyawarsa. Amanar da sultane ya damqa a hannunsa ke gilmawa cikin idanunsa........yardar sultane a kansa yake tunawa.......da rauninta na kasancewarta D'IYA MACE......d'iya macen ma da rayuwarta cikin wani yanayi na tagayyara da girman kanta son ranta da son zuciyarta ya hanata ta gane ramin da take shirin shiga ta binne kanta.
Hannunsa kawai omari yake dunqulewa yana qoqarin bin umarnin haisam ta hanyar danne na'aurar warning dake tsakiyar tafin hannun haisam din. Mafi girman qarar da na'urar keyi yake gayawa omari qaqqarfan warning haisam ke masa na kada ya soma matsowa ko sanya baki kome girman abinda zai faru.
"Ka qwace komai na matsayina daga hannun sultane......a zakutana mutane ma kanason qwace wannan martabar tawa?......ka gayamin......nauyin kudin da zai siya dukka ilimin da kake taqama dashi kana tunanin yayi daidai da abinda zai iya biyan sadaki na?!!".
Wani abu me tsini yaji ya caki tsakiyar zuciyarsa......wani abu daya sanyashi daga dukkan manyan idanunsa ya zubesu saman fuskarta,idanun da suka nutse cikin nata ba tare data shirya ba,suka kuma soma sakin wadannan magnet din masu wani iri kaifi da girma da suka sanyata yin taku biyu baya da kanta don rage tazarar da ita ta tsuke nisan dake tsakaninsu.
"Sadaki ba shine ke daga darajar mace ba ko ya sauketa......sadaki ba gasa bane.......haqqi ne da Allah yace a bawa mace.....sai kuma addininmu ya gaya mana mafi qarancin sadaki shi yafi albarka a aure......nayi abinda shari'a tafi so......idan har alfaharinki da girman kanki yana da nauyi sama MUTUNCI da KARAMCI ......wannan ba matsalata bane" Ya qarasa maganan yana zube hannayensa a aljihun jubah dinsa gami da dage dukka kafadunsa,manyan fararen idanunsa na zagayawa tsakanin blue eyes dinta,daga bayanta kuma yana hange masa kusantowar motsin da yakejin bai aminta dashi ba,saidai motsin bai janye hankalinsa daga duban kai tsaye da yake mata na ido cikin ido ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/26, 19:09] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE PAGE 42*
Batasan ya akayi ta samu idanunta da zame kansu da kuma qwace dubansu daga cikin nasa ba bayan ba abinda ta tsara yi kenan ba.......tana jin idan ta bari ya gayamata ko ya maida mata magana ko qwaya daya ce yayi jayayya da girmanta,don haka cikin rashin yarda da izzarta takai qasa ta sake motsa labbanta fushinta na bayyana sosai.
"Me ka dauki kanka?......a tunaninka kai din waye?" Wani miskilin murmushi dake cakude da izza ya saki,wanda ya kusan tafiya da numfashinta na wucin gadi,cikin nuna halin ko in kula yana kuma sake raba hankalinsa da yadda yakejin hucin giftasu daga hagu zuwa dama ya maida mata amsa.
"Muhammad haisam wani ne.....wanda ya zame miki tilas ki dakata da qidddige iya adadin ikonsa......don zaki gaza a sanda hasashenki bazai taba iya cafko adadin qarfin ikonsa ba". A karon farko iya tsaho shekarun da tayi a duniya da aka taba challenge nata......da ta taba fadin magana aka maida mata......da aka tsaya a gabanta ana dubanta da duba na kai tsaye......irin duban da mammina ko sultane kadai keda iko da lasisin yi mata shi. Koda ya samu daman tsaiwa a inda ta tsaya.....koda ya samu daman maida mata magana ba zata bari ta kwana da ciwon rai ba.
"Idan kana jin dadin tozarta matan da kasan sunfi qarfin matakinka a rayuwa?,daga kaina ba zaka qara kusantar aikata hakan ba" A karo na biyu wani qasaitaccen murmushi ya subuce masa,yayi qas da kansa yana hangen tazarar inuwar boyayyen mutum daga bayanta wanda yake da tabbacin batasan da tsaiwarsa ba,sai ya daga kansa a nutse yana mata nuni da hanya cikin kamala.
"Idan kin gama fadin duk abinda yake ranki kina iya tafiya" Idanunta ta qanqance sosai,reshe yana neman juyewa da mujiya. Gurbi da muhallin fushi takeson gani saman fuskarsa akan maganganun data gaya masa.......amma sai yake maye gurbin haka da wani murmushi da iya tsahon zamanta cikin da'irar sarauta,gidan mulki da iko bata taba ganin murmushin dake cakude da zallar izza irinsa ba. Yabar mata ciwon fadin maganar a ranta?,kuma yana umartarta da tafiya daga muhallin daya kasance mallakin mahaifinta?......saman QASAR data kasance cikakken ikonta..
"Ki tafi nace" Yayi maganar wannan karon yanayin fuskarsa yana juyewa da wani matsanancin tsare gida yana kuma ajiye mata wani nannauyan kallo da taji ya mata wani mahaukacin kwarjini.
Wannan dabi'artata ta taurin kai da kafiya ita ta motsa.....izzarta ta taso ta lullubeta,ita dake bada umarni yau ita wani yake bawa umarni?......ita dake da iko na fada aji ita ake fadawa abinda zatayi?.
Sake tsareta yayi shima da kakkaifan kallonsa,yana sake irga motsi da takun bulama. Kaucewarta a gurin yafi buqata a sannan,don yanason nunawa bulama qarshen rashin qwarewa cikin aikinsa. Saidai kuma baya qaunar wanzuwarta a gurin,saboda ba gaban idanunta yake buqatar yin kowanne motsi nasa ba.....amma yana karantar kafiyarta da taurin kanta na shirin zame masa cikas,kaman yadda ya karanci bulama yana daf da kubcewa tsarinsa,don haka dole yayi wani irin taku da bai kai biyar ba,ya miqa hannu tsakanin shukokin dake daura dasu,ya damqi wuyan bulama cikin wani irin zafin nama,sannan ya fincikoshi daga duhu zuwa cikin haske,ya kuma watsar dashi a gurin.
Tazara kadan ta rage a tsakaninsu,ta tsaya cak tana goye hannayenta a qirji gami da sake zuba masa idanu ta baya tana sake zurfafa kallonta a kansa. Taku hudu omari yayi yana basu space,space din dabai nesantashi da ji da ganin abinda ke faruwa ba.
Yaji tsaiwarta a bayansa,saidai yanajin kamar kusancin dake tsakaninsu yayi yawa,amma duk da hakan bai juya ba sai bayan wasu sakanni da suke sake tabbatarwa da akhnan shi din MA'ABOCIN GIRMAN KAI NE.
Bataga alamun zai juyo ba....bataga alamun yasan da wanzuwarta a gurin ba,haqurinta kuma ragagge ne da ba zata iya jiran reaction dinsa ba,duk da tarin izzar da take cinta sai ta sake goye hannunta sosai a qirjinta,cike da izza,cike da jin isa ta motsa labbanta,tattausar muyar nan da bacin rai ya yiwa murfi ta soma yawo cikin iskar dake kadawa tana isar da saqonta ga kunnuwansa.
"Wannan itace hanyar da malamai suke bi don qasqantar da daraja kima da martabar 'ya mace.......da bautar da ita cikin aure da sunan addini da kuma musulunci da irin son zuciya da qarairayinsu!" Sosai sautin maganarta ya zauna masa cikin kai da zuciya da wani irin dumi da yaji yana mamayar zuciyar tasa.
Numfashi yaja ya aika har cikin hunhunsa yana kiran sunan Allah can qasan zuciyarsa da neman taimako kada shaidan ya rinjayeshi,sai ya saki qarfen da yake dafe dashi ya waiwayo a nutse idanunsa suna sauka a kanta.
Guri daya idanunsu suka sarqe,ya sake zare dubansa daga kan fuskarta data bayyana tarwai ta siririyar walqiyar dake haskawa kadan kadan wadda bata dauke da sautin komai,wannan shi zai baka damar ganin yadda iska ke wasa da mayafin saman kanta,da sassalkan wani siririn gashinta me santsi daya ratso ta gefan kunnenta ya fito.
Yadda ya zare dubansa a kanta kamar kullum kamar yadda ta kula al'adarsa ce ya sake tunzurata. A koda yaushe yana nuna shi din wani tsarkakke ne wanda ita ta jima da sanin son zuciya da son rai da kuma fakewa bayan addini suna aiwatar da son rai da son zuciyarsu babu wanda yakai malami yin hakan. Wanna fusatar ta sanya ta qara taku biyu zuwa gabansa,tana son ta bambance me yakeji dashi da yake mata wani kallo sannan ya watsar ta hanyar janye idanunsa a duk sanda zasu hadu irin haka.
"Kana tunanin bada aurena wani abu ne me sauqi da wasu qananun sulalla marasa darajar da ko takalmin sakawa a qafar hadimaina darajarsa tafi ta wadannan sulallan?" Ta sake fadi cike da tsiwa numfashinta yana dagawa sosai ta saman qirjinta. Numfashi ya sake ja yana aikewa cikin gangar jikinsa yana jin wataqila wannan zai taimaka wajen controlling kansa da zuciyarsa.
"Wannan itace hanyar daka zaba wajen qasqantar da darajata?wajen gayawa duniya abace ni me sassauqar daraja?......darajar da baka isa ka samu kwatankwacinta ba?!" Ta sake tambayarsa tana sane takawa zuwa inda yake tsaye kamar ta manta da tana qara kawo kusanci ne a tsakaninsu.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Labarina.......sunana.....daukakata da darajata wani abun tattaunawa ne tsakanin manyan masarautu,ba na iya agadez kawai ba......dole sadakina da aurena ya bambanta dana kowacce d'iya dake jin asali da gata!.....bakasan hakan ba?" Ta sake tambayarsa,idanunsa na sake hange mata wani irin calmness a tattare dashi. Kaman ba ihu take masa ba.....kaman ba fada take masa ba,tunzura take so yayi.......tanaso yayi wani abu guda daya da zai sanyata ta yaga wannan rigar maluntar.....rigar mutuncin da yakejin yana sanye da ita.
Tarin rufewa da idanunta sukayi ya sanya ya gaza ganin yadda adams apple dinsa ke sama da qasa yana qoqarin tura duk wani yunqurin bayyana fusata da fushi da zuciyarsa ke qoqarin turawa saman fuskarsa. Zuciyarsa na wani irin motsawa da mugun qarfi,yayin daya sanya kalar nashu qarfin yana danneta da dukka iyawarsa. Amanar da sultane ya damqa a hannunsa ke gilmawa cikin idanunsa........yardar sultane a kansa yake tunawa.......da rauninta na kasancewarta D'IYA MACE......d'iya macen ma da rayuwarta cikin wani yanayi na tagayyara da girman kanta son ranta da son zuciyarta ya hanata ta gane ramin da take shirin shiga ta binne kanta.
Hannunsa kawai omari yake dunqulewa yana qoqarin bin umarnin haisam ta hanyar danne na'aurar warning dake tsakiyar tafin hannun haisam din. Mafi girman qarar da na'urar keyi yake gayawa omari qaqqarfan warning haisam ke masa na kada ya soma matsowa ko sanya baki kome girman abinda zai faru.
"Ka qwace komai na matsayina daga hannun sultane......a zakutana mutane ma kanason qwace wannan martabar tawa?......ka gayamin......nauyin kudin da zai siya dukka ilimin da kake taqama dashi kana tunanin yayi daidai da abinda zai iya biyan sadaki na?!!".
Wani abu me tsini yaji ya caki tsakiyar zuciyarsa......wani abu daya sanyashi daga dukkan manyan idanunsa ya zubesu saman fuskarta,idanun da suka nutse cikin nata ba tare data shirya ba,suka kuma soma sakin wadannan magnet din masu wani iri kaifi da girma da suka sanyata yin taku biyu baya da kanta don rage tazarar da ita ta tsuke nisan dake tsakaninsu.
"Sadaki ba shine ke daga darajar mace ba ko ya sauketa......sadaki ba gasa bane.......haqqi ne da Allah yace a bawa mace.....sai kuma addininmu ya gaya mana mafi qarancin sadaki shi yafi albarka a aure......nayi abinda shari'a tafi so......idan har alfaharinki da girman kanki yana da nauyi sama MUTUNCI da KARAMCI ......wannan ba matsalata bane" Ya qarasa maganan yana zube hannayensa a aljihun jubah dinsa gami da dage dukka kafadunsa,manyan fararen idanunsa na zagayawa tsakanin blue eyes dinta,daga bayanta kuma yana hange masa kusantowar motsin da yakejin bai aminta dashi ba,saidai motsin bai janye hankalinsa daga duban kai tsaye da yake mata na ido cikin ido ba.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/26, 19:09] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE PAGE 42*
Batasan ya akayi ta samu idanunta da zame kansu da kuma qwace dubansu daga cikin nasa ba bayan ba abinda ta tsara yi kenan ba.......tana jin idan ta bari ya gayamata ko ya maida mata magana ko qwaya daya ce yayi jayayya da girmanta,don haka cikin rashin yarda da izzarta takai qasa ta sake motsa labbanta fushinta na bayyana sosai.
"Me ka dauki kanka?......a tunaninka kai din waye?" Wani miskilin murmushi dake cakude da izza ya saki,wanda ya kusan tafiya da numfashinta na wucin gadi,cikin nuna halin ko in kula yana kuma sake raba hankalinsa da yadda yakejin hucin giftasu daga hagu zuwa dama ya maida mata amsa.
"Muhammad haisam wani ne.....wanda ya zame miki tilas ki dakata da qidddige iya adadin ikonsa......don zaki gaza a sanda hasashenki bazai taba iya cafko adadin qarfin ikonsa ba". A karon farko iya tsaho shekarun da tayi a duniya da aka taba challenge nata......da ta taba fadin magana aka maida mata......da aka tsaya a gabanta ana dubanta da duba na kai tsaye......irin duban da mammina ko sultane kadai keda iko da lasisin yi mata shi. Koda ya samu daman tsaiwa a inda ta tsaya.....koda ya samu daman maida mata magana ba zata bari ta kwana da ciwon rai ba.
"Idan kana jin dadin tozarta matan da kasan sunfi qarfin matakinka a rayuwa?,daga kaina ba zaka qara kusantar aikata hakan ba" A karo na biyu wani qasaitaccen murmushi ya subuce masa,yayi qas da kansa yana hangen tazarar inuwar boyayyen mutum daga bayanta wanda yake da tabbacin batasan da tsaiwarsa ba,sai ya daga kansa a nutse yana mata nuni da hanya cikin kamala.
"Idan kin gama fadin duk abinda yake ranki kina iya tafiya" Idanunta ta qanqance sosai,reshe yana neman juyewa da mujiya. Gurbi da muhallin fushi takeson gani saman fuskarsa akan maganganun data gaya masa.......amma sai yake maye gurbin haka da wani murmushi da iya tsahon zamanta cikin da'irar sarauta,gidan mulki da iko bata taba ganin murmushin dake cakude da zallar izza irinsa ba. Yabar mata ciwon fadin maganar a ranta?,kuma yana umartarta da tafiya daga muhallin daya kasance mallakin mahaifinta?......saman QASAR data kasance cikakken ikonta..
"Ki tafi nace" Yayi maganar wannan karon yanayin fuskarsa yana juyewa da wani matsanancin tsare gida yana kuma ajiye mata wani nannauyan kallo da taji ya mata wani mahaukacin kwarjini.
Wannan dabi'artata ta taurin kai da kafiya ita ta motsa.....izzarta ta taso ta lullubeta,ita dake bada umarni yau ita wani yake bawa umarni?......ita dake da iko na fada aji ita ake fadawa abinda zatayi?.
Sake tsareta yayi shima da kakkaifan kallonsa,yana sake irga motsi da takun bulama. Kaucewarta a gurin yafi buqata a sannan,don yanason nunawa bulama qarshen rashin qwarewa cikin aikinsa. Saidai kuma baya qaunar wanzuwarta a gurin,saboda ba gaban idanunta yake buqatar yin kowanne motsi nasa ba.....amma yana karantar kafiyarta da taurin kanta na shirin zame masa cikas,kaman yadda ya karanci bulama yana daf da kubcewa tsarinsa,don haka dole yayi wani irin taku da bai kai biyar ba,ya miqa hannu tsakanin shukokin dake daura dasu,ya damqi wuyan bulama cikin wani irin zafin nama,sannan ya fincikoshi daga duhu zuwa cikin haske,ya kuma watsar dashi a gurin.