← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 84 OF 101

Sashe 84

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun a dararen da suka shude ta yiwa kanta wadannan alqawuran,zata maida rayuwarta yadda take a baya a cikin satin. Zata maida kanta PRINCESS KHADEEJA MUHAMMAD HAMMUD dinta kamar yadda take a baya,zata rayu yadda takeso,ba shawarar kowa....ba sanya hannun kowa.....ba gudanarwa ko yankewar hukuncin kowa. Wannan ya sanya ba tare data shaidawa mammina ko tayi shawara da ita ba ta fara shirye shiryen komawa Niamey. Tun a daren jiya ta gayawa hannatu a gyaran gidan a maidashi kaman yadda yake a baya,a fadawa babban driver dinta na garin Niamey wato HARISU ya duba motocinta gaba daya da take fita office dasu a fita dasu a siyo wasu. Koda ta koma Niamey tana jin zatayi hutun sati daya cikin gidan kafin ta fara fita office. Zata zauna na sati daya ta maida wannan tunanin na CEO a kanta,ta sake kintsa nutsuwarta da yadda zata karbi ayyukanta.

A yanzun da take zaune cikin daya daga cikin falukanta da takan huta. Baida kujera ko daya,sai wasu irin lausasan Turkish carpet da tuntum manya masu dauke da tambari na sarauta da sunanta a jikin kowanne. ABIDA me mata gyaran gashinta ce,wadda ta iya nau'ikan manyan kitso na qasashe da qabilu daban daban,da kuma kalba manya da takan yiwa akhnan din a sanda duk zata koma Niamey idan ta gama hutun qarshen mako da takeyi a baya.

Tana mata kalbar data zama manya kuma tana hade jelarsu guri daya yadda ba zasu damu uwar gijiyartata ba,yayin da akhnan din ta maida hankalinta sosai ga ameesha tana sauraren bayanai akan kamfanin na watannin da tayi bata tare dasu.

Kowanne bayani na ameesha sake bata mamaki kawai yakeyi,amma bata dakatar da ita ba,taci gaba da sauraronta duk da ba ganewa takeyi ba,amma ta aza hakan akan cakudewar bayanan ameesha dinne guri daya ya kawo haka,don bada wannan salon da kuma wannan yanayin suka gabatar mata da bayani ba.

Kanta taji abida ta saki,abinda ya sanyata dauke kai daha system din da suke video call da ameesha ta maida ga abida,sai idanun nata suka sauka akan mammina dake takowa cikin izza,da alama kuma ita ta saka hadimanta su bawa dukkan hadiman dake dakin umarnin fita.

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[2/10, 19:48] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 74*

Bata motsa ba,bata kuma ce da ita komai ba,sai kawai ta maida idanunta ga Ameesha sukaci gaba da tattaunawarsu cikin salon miskilancin nan nata da ya motsa.

Idanun mammina akan ameesha bayan ta daukeshi daga kan akhnan da rabi akayi masa kalbar ta kuma sauka lambas a gadon bayanta,sai rabin gashin da yabi gefan kuncinta ya kwanta.

A jikinta taji abubuwa biyu,bata kuma buqatar qarin bayani. Hankalinta ya kwanta da har take shirye shiryen komawa Niamey kenan?,sannan ya akayi ta samu access da ameesha?....me take gaya mata?.

Tana buqatar fahimtar komai kafin tayi magana daukan mataki na gaba ko kuma yin wani motsin,don haka ta samu tuntum daya ta zauna akai tana harde qafarta.

Still akhnan bata waiwayo ba,saidai yanayin ameesha da taga kaman yana sauyawa,kamar bayanin tana yinsa ne kawai ba tare da ita kanta tasan gundarin abinda take magana akai ba. A nutse ta lumshe idanunta sannan ta budesu a kanta.

"Ameesha" Ta kirata da muryarnan tata dake cike da aji gayu da sarauta.

"Ranki ya dade"

"Ki tattara komai ta yadda idan na iso zanji dadin dubawa,bazan wuce gata ba in sha Allah"

"To Allah ya kawoki lafiya,godiya nake" Ameesha ta fadi wani sanyi yana tsargawa qasan ranta. Tana fatan ta iso da wuri,ta kuma jima tana addu'ar dawowarta a lokaci irin wannan kafin komai ya qarasa kwabewa.

"Gata?" Mammina ta furta a nutse da salon tambayar da ba iya fili kadai ba.....hatta da zuciyarta ta aikewa tambayar. A nutse ta waiwayo ta dubi mammina tana kuma dakatawa da kashe system din.

"Eh gata" Ta amsa mata kai tsaye da wani irin yanayi da tasan sauran mutane kadai akhnan me magana dasu a haka ba ita giwa ba.

"Gata in sha Allah......ko akwai sauran abinda ya rage da zan zauna nayi?.....kowa burinsa ya cika,an daurawa akhnan aure,ta taba aure a tarihin rayuwarta dai ko?" Ta fada da dukkanin alamun dake nuna abun yana mata ciwo.....da dukkanin alamun dake nuna cewa abun yana mata radadi tare da jefata a danasanin amincewa da wannan yarjejeniyar tunda farko.

"Akhnan d'iyata" Mammina ta kirata bayan ya sake matsowa dab da ita,idanunta da jikinta dukka sunayin wani irin laushi.

"Ban taba zato ko tunanin wani lokaci yana zuwa da zaki zargeni koki tuhumeni da cutar dake ba" Ta furta hawaye yana saukowa daga idanunta. Har tsakiyar zuciyarta akhnan taji hakan,a karon farko taga abinda bata taba ganina idanun mammina ba tsahon rayuwarta,kuka ko hawaye

"Na rantse miki harda girman Allah......almaz shine kalar mijin da yafi dacewa dake.....kinsan a yanzu haka halin daya shiga saboda abinda ya aikata din?". Tayi mata tambayar tana tsareta da idanu tanason karantar yanayinta.

Kai tsaye akhnan din take duban mammina. Haka kawai tayi loosing interest aka komai daya shafeta......tana jin tana rasa dukkan wani confidence da qwarin gwiwa akan mammina din. Batasan me yasa ba,tana jin kawai komai ma ya fita a ranta,amma wani sashe na zuciyarta yana gaya mata,bai kamata KUSKURE D'AYA TAK da aka samu daga bangaren mammina din ya zama wani abu ba.....ya zama wani dalili da zai sanya ta juya bayanta daga dukkan wani alkhairan mammina din a tare da ita ba.

Wata irin mutum ce ita da bata manta alkhairi komai qanqantarsa.

"Wallahi akhnan ya fiki shiga baqinciki bacin rai da kuma damuwa.......a yanzun ina me baki tabbacin baisan inda kanshi da hankalinsa yake ba,kuma dukka a kanki,dukka ta sanadinki" Mammina din ta fadi yanayinta yana nuna narkewar zuciyarta.

"Ta yaya zanyi saken da wani mummunan abu zai rabi diyata?.....ta yaya zanyi saken da halitta mafi soyuwa a zuciyata da rayuwata zata fuskanci wata barazana?,bayan bani da kamar wannan halittar duk duniya?. Ina jin wani irin mamaki kaman zai kasheni a duk sanda na kalli fuskarki,naga kuma ba abinda ya cikata sai tuhuma da ganin baqina" Mammina ta furta tana share qwallarta data sake gangaro mata.

"Amma duk da haka ni zaituna.....nayi alqawarin saita lamuranki,koda kuwa hakan shine abu na qarshe da zan aiwatar a rayuwata.......abu daya zan gaya miki.....ko mene zai biyo baya kada ki tuhumeni.....idanunki da hankalinki kawai nake buqata......amma karki manta da wannan ko sau daya a zuciyarki......ni mammina UWA nake a gareki.....bazan kuma taba canzawa daga wannan sunan ba har abada.....kamar yadda babu wani abu da zai sauya qaunar da nake miki har gaban abada". Daga haka ta miqe da wani irin yanayi dake nuna mutuwar jiki da damuwa me yawa.

Samun kanta tayi dabin mammina din da kallo,tana jin jikinta itama gaba daya yanayin wani irin sanyi. Tana jin kamar ya kamata tabi bayanta.....amma wani sashe na zuciyarta dake daqare da wannan izzar dake gauraye da jinin sarauta na gaya mata ta qyaleta.

Wani irin kewa takeji a yau......wani irin kadaici takeji duk da cewa tana zagaye ne da mutane. Samun kanta tayi da miqewa tsam,ta taka a hankali tana isa bakin qofar dakin,ya maidata ta murza mata key ta kulleta. Dawowa tayi a nutse zuwa bedside drawer dinta da ba wanda yake da alhakin taba gurin,ta murzata ta budeta,ta kuma fiddo wani dan zagayayyen akwaiti me matsakaicin girma ruwan gold. Budeshi tayi a nutse,ta saka hannu tana fiddo wasu hotuna qananu guda biyu.

Idanu sosai ta xubawa fuskar dake jikin hoton,fuskar dake dauke da wani lallausan murmushi. SAFEENA ce,idanunta a cikin hoton suna kallon camera ne kai tsaye,wasu irin kyawawan idanu da suke kama sosai da nata,banbamcinsa da natan ita fari da blue ne......yayin da na safeena ya kasance fari da baqi sidik......

Hannu ta sanya a hankali ta shafi hoton,a ranta tana raya abubuwa masu yawa.......a ranta tana raya inda tana raye yaya zasu fuskanci wadannan kwanakin masu tsanani da taurari a tattare da ita?,saita lumshe idanunta tana damqe hoton sosai a tafin hannunta.

Haka kawai takejin akwai wani abu da ba daidai ba......haka kawai takejin akwai wani KUSKURE da yake tare da ayyukanta da zartarwata......ko kuma yake tattare da tunani da hukuncin mammina?. Amsar da bata da ita batasan kuma yadda zata fassara abun ba.

*SULTANE*

Cikin kamala da nutsuwa irin tasa,wadda bata taba sauyawa ba ko a wanne bigire kuma ko awanne yanayi ya samu kansa ba ya qarasa qofar dakin bobbo muhammad dawud,wanda ya kasance daura dashi cikin daya daga cikin manyan hotels dake kusa da haramin madeena.

Sau daya ya nema izinin shiga,bobbo da kansa ya taso ya budewa sultane din bayan ya ajiye dan qaramin alqur'anin dake hannunsa.

"Ina fata kaima qira'arka irin ta yaronka ce ko?" Sultane ya fadi yana duban bobbo muhammad wanda ya ajiye masa ruwan daya ciro masa mara sanyi sosai a fridge. Bawai don daga wani guri sultane ya taso ba,ba kuma wai don yana jin ishirwa ba.....aah,kawai don tarin girmamawa ga tsohuwar abota.

Murmushi sosai bobbo muhammad dawud yayi. Zuwa yanzu har ya saba da yanda duk fitowar rana da kuma faduwarta sai sultane din ya ambaci hasaim. A irin ambaton da ko motii aba jifar baya tunanin yana ambatonsa haka.

"Duk wanda ya zauna da muhammad saiya dosani wani haske na alqur'ani daga gareshi" Obbo ya fadi yana zama gefan gadonsa yana fuskantar sultane. Kai sultane ya gyada a hankali,yana sake jin nutsuwa gami da gamsuwa me yawan gaske a tare dashi game da haisam din.
Chapter 84 · 0% Book details