Sashe 3
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Armelle?......me yake faruwa yau?....tun daga farkon gate nake ganin gidan ba kamar yadda na fita na barshi ba" . A nutse armelle ta saukar da kanta qasa,tana jin wani irin nauyi. Ta yaya matar data sadaukar da dukiyarta girma da matsayin da Allah ya bata domin inganta rayuwarsu da qoqarin sakasu farinciki?,ta yaya ita din zata zama mutum ta farko da zata zo mata da mummunan labarin da tayi imani ba wani labari mafi muni a gurinta da zai biyo bayansa.
Sautin murya da kukan falaak shine ya fanshi armelle,abinda ya sanya armelle janyewa baya a hankali,ya kuma saka morsa safiyya waiwaya zuwa ga inda takejin sautin kuka yana fita.
Falaak ce......cikin gudu gudu sauri sauri,abinda ya tsinka jinin morsa safiyya kena,ya sanyata mata tarin fargabar data hanata motsawa,har falaak ta qaraso ta kuma zube a jikinta tana rungume morsa safiyya da kyau tana sakin wani sabon kukan daya ratsa har tsakiyar tsokar zuciyar morsa safiyya din. Shafa gadon bayan falaak kawai takeyi,ta gaza tambayarta komai saboda tsoron abinda zataji. Kukan da falaak takeyi kuka ne me tsananin nauyi da ko wanda ke nesa ya jishi yasan yana fita ne direct ne daga ainihin cikin zuciyarta.
"Momma.......yaa biftu tasha guba......tasha guba momma.......tana can batasan inda hankalinta yake ba" Falaak ta qarasa fada tana fashewa da sabon kuka. Wani irin dokawa qirjin morsa safiyya yayi da wani kalar tashin hankali.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.......innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ta maimaita sau kusan hudu tana qoqarin tattara hankalinta da a yanzu tasan tafi buqatarsa sama da komai.
A hankali ta sanya hannu ta zare falaak daga jikinta,sai ta miqa hannun ta damqi tsintsiyar hannun falaak.
"Tana ina?".
"Sassanta......amma mammina tasa an hana kowa shiga.......daga ita sai bappi ne a ciki" Falaak din ta fadi cikin jin ciwon yadda taso shiga din,amma mammina ta leqo tana gaya mata kukanta zai tta'azzara yanayin da akhnan take ciki,so ta tsaya a baya ta mata addu'a.
Ko gane sauran bayanan falaak morsa batayi ba,tasan kawai tace dasu armelle
"Ku wuce bakin ayyukanku" Taci gaba da jan hannun falaak suna takawa zuwa shiyyar da zata sadata da sassan akhnan din.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[12/31, 19:36] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 05*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
________________________________
Shuru kawai parlor din ya dauka,kai kace babu wani sauran me rai dake raye a cikin sa. Cikin wani irin salubabben yanayi sultane ke tsaye gaban akhnan,cikin wani yanayi dashi kansa bazai iya fassarashi ba.
Tsahon mintuna kafin ya tsugunna gabanta a hankali,inda take kwance kawai,banbancinta da gawa qalilanne. Hannunsa ya sanya ta qasan duvet din da take lullube dashi ya kamo hannunta,wani irin sanyi tafukan hannun nata sukayi,a hankali ya furta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". A nutse haisam dake tsaye gefe daya ya daga idanunsa ya zube akan sultane din,dukkan jikinsa yana jin ya masa wani iri. Tun wanzuwarsu a gurin har zuwa kwantar da ita da akayi da bata taimakon farko da yayi gudun kada illar gubar tayi barnar da ba zata gyaru ba,bai sake daga idanunsa ya kalleta ba ko sau daya.
Kwata kwata tsaiwarsa a gurin ma ta zame masa kamar lalura ne kawai saboda shigowar me martaba a sanda yake qoqarin fita,shigowar da sultane din kuma yayi,wani yanayi yake ciki da yake buqatar wani a kusa,wanin da zai riqe koda hannunsa ne yaji sassautin abinda yakeji.
Yanayin sultane din kadai ya gama bayyanawa haisam rudun da yake ciki,saidai zallar jarumta irin ta basaraken mutum,irin jarumtar dake nasa jinin kenan shima,irin jarumtar kuma da aka sani cikin jinin dukka wanda yake da jibi da SARAUTA.
"Muhammad" Sultane ya kirashi muryarsa da tayi laushi can qasa,kansa kawai haisam ya daga yana duban sultane din,saidai kafin yace komai muryar mammina cikin wani irin yanayi ta tunkarosu,sai kuma gata ta iso.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.......ya Allah.......ya Allah ka taimakemu.....ka rufa mana asiri.....kar ka bari wani abu ya samu yarinyar nan" Tayi maganan sanda take wucewa kai tsaye zuwa ga inda akhnan ke kwance numfashinta yana fita da wani irin yanayi da ba haka ya saba fita ba.
Gaba daya ta rungumeta cikin jikinta,wani irin kuka me tafe da hawaye ya qwace mata.
"Me yasa zaki aikata haka?,me yasa zaki illata kanki akhnan?.....ashe dama baki haqura ba?,dama baki janye kalamanki ba?,dama da gaske kike sai kin sha din........Allah ka taimakamin.......d'iyata ya Allah" Ta qarashe fadi tana sakin wani sabon kukan.
A hankali ya lumshe idanunsa sai kuma ya budesu,ya motsa a hankali yana gyara hannun rigarsa. Yana da nufin fita ne daga sassan gaba daya,don dama dole ke tsaye dashi a gurin,shi ya gama nashi part din,ya gama iya abinda zai iya. Bayason kallon drama din matar nan,kanshi shuru yafi buqata,hayaniyarta kuma ya karanci me yawa ce,da gaske damunsa zatayi.
"Muhammad........ba wani qarin taimakon da zaka mata?,likita baya kusa........amma yana hanyan isowa" Sultane ya fada cikin wata muguwar karaya yana dauke idanunsa daga kan mammina,kalamanta kuma suna huda qirjinsa,karayar data sanya tausayin sultane din saukar masa lokaci guda.
Lallai koda ba'a gaya maka ba zaka fahimci tsantsar soyayyar da sultane yakewa akhnan......sosai haisam ya gama fahimtar irin girman wannan qauna da soyayyar....wadda a ransa yakejin indai har yana son yarinyar har haka,to lallai ba qaramin qoqari yayi ba gurin horata ta hanyar aura mata wanda babban muradinta shine ya janye aura mata shi din.
"Akwai........za'a iya bata injection na Atropine" Ya furta a hankali,duk da yana jin kamar bai dace ya buda sirrinsa ba ko yaya ne.
Ga duk wanda ya qware a aikin binciken sirri a qasarsu,suna da horo na musamman wajen irin wadannan abubuwa saboda shirin kota kwana da kuma yiwuwar faruwar irin wadannan abubuwa kan daya daga cikinsu ko su kansu,sirrinsu ne da ba wanda ya sani,amma a yanzun da yake kallon tsakiyar idanun sultane din dake jirkice da tarin rudani da abubuwa iri daban daban......yanajin kamar wajibinsa ne ya taimaka.......kwanyarsa kuma na bankado masa daya daga cikin ayoyin qur'ani dake fadin DUK WANDA YA RAYA RAI QWAYA DAYA TAMKAR YA RAYA MUTANE GABA DAYA NE kamar yadda farkon ayar ke fadin idan ka kashe rai daya kaman ka kashe al'umma gaba daya ne.
Cikin wani irin gaggawa da zafi sultane ya saki umarnin nemo ruwan allurar ko a ina yake cikin qasa da mintuna goma.
*MORSA*
Dukka hankalinta dama tunaninta baya tattare da ita sam sam. Kawai dai tana d'aga qafarta tana kuma saukewa ne bisa tabbacin ba zata fadi ba,saboda ko ina na cikin gidan wani shimfidadden terrazzo ne me matuqar kyau da daukan hankali.
Kukan falaak kawai ke yawo cikin qirjinta da kunnuwanta,yadda falaak ke kuka yana sake tabata gami da sake motsa wani tashin hankalin a tare da ita. Wai akhnan ta sha guba?......guba dai?,ko daya hankalinta da zuciyarta basu dauka ba basu kuma nutsu ba.
Tana tunkaro sassan akhnan din duk wani hadimi dake tsaron gurin wanda mammina ta sanya ya soma buda mata hanya ba tare da tace komai ba,taci gaba da kutsawa falaak na riqe a hannunta.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Shine abinda bakin mammina ke maimaitawa tana riqe da akhnan cikin jikinta. Ko ina ina jikin mammina rawa yake,wani irin tashin hakali yana bayyana kansa saman fuskarta,hatta da hailalan da take ambatawa bakinta rawa kawai yakeyi.
A nutse da irin nutsuwar da ba kasafai take barin gangar jikinsa ba ya taka zuwa ga box din da yasa aka shigo masa dashi yanzun na allurar daya buqata din.
Kunnuwansa suna kan sautukan mammina da bakinta ya kasa daina maimaita hailalan da takeyi duk da yadda yakeso ya raba kanshi da hayaniyar matar,a daidai lokacin da sultane ke tsaye saman kansu idanunsa akan akhnan din cikin wani irin yanayi me wuyar fassara,ya kasa matsawa,abinda ke yawo cikin kansa kawai shine zantukan mammaina data furta dazu
"Kenan dama ita ta shirya poisoning din kanta?" Tambayar da yaketa maimaitawa kansa ita kenan.
Tun dazun ya gaza sake cewa komai,yanayinsa wani yanayi me wahalar fassara da kai tsaye ba zaka iya karantar abinda yake ranshi ba.
Tas haisam ya zuqe ruwan allurar da nutsuwa,a daidai sanda gaba daya hankalin mammina ke kanshi. Qatotuwar ayar tambaya ta ajiye
"Me ya hada malami da iya allura?.....meye hadinsa duka duka da harkar lafiya?" Ta fadi tana nazartarshi da wani irin yanayi da ba lallai ka fahimta ba.
Yana fidda iskar data shiga cikin syringe din sallamar morsa safiyya da muryarta ke shaking ta wanzu a falon,abinda ya janye hankalinsu su duka kenan,banda haisam da yaci gaba da abinda yake a qoqarinsa na bata allurar ya kuma fice daga gurin don bawa iyalin daman ci gaba da abinda ya shafesu.
"Sheik muhammad" Falaak dake maqale a bayan morsa safiyya ta fadi da sautin da morsa dince kawai ta jishi,saita dan dubi sashen da falaak din ke kalla kafin ta zare idanunta daga kansa. A karon farko data kalleshi cikin yanayinta da ba na nutsuwa ba,ta hangi tarin kamala da kuma nutsuwa a tattare dashi.
Wani kallo mammina din ke bin morsa safiyya dashi,saidai kallo ne dake qudundune tsakanin duffan daba kowa zai masa fahimta ta kai tsaye ba.
Kai tsaye morsa safiyya ta isa gabansu idanunta akan akhnan dake jikin mammina. Idanunta suna bude,amma ba alamar tana iya gani ne ko gane kowa......ba kuma alamar tana tare dasu a duniyarsu,ba kuma alamar tana fahimtar abinda ke gudana a dakin.
Sautin murya da kukan falaak shine ya fanshi armelle,abinda ya sanya armelle janyewa baya a hankali,ya kuma saka morsa safiyya waiwaya zuwa ga inda takejin sautin kuka yana fita.
Falaak ce......cikin gudu gudu sauri sauri,abinda ya tsinka jinin morsa safiyya kena,ya sanyata mata tarin fargabar data hanata motsawa,har falaak ta qaraso ta kuma zube a jikinta tana rungume morsa safiyya da kyau tana sakin wani sabon kukan daya ratsa har tsakiyar tsokar zuciyar morsa safiyya din. Shafa gadon bayan falaak kawai takeyi,ta gaza tambayarta komai saboda tsoron abinda zataji. Kukan da falaak takeyi kuka ne me tsananin nauyi da ko wanda ke nesa ya jishi yasan yana fita ne direct ne daga ainihin cikin zuciyarta.
"Momma.......yaa biftu tasha guba......tasha guba momma.......tana can batasan inda hankalinta yake ba" Falaak ta qarasa fada tana fashewa da sabon kuka. Wani irin dokawa qirjin morsa safiyya yayi da wani kalar tashin hankali.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.......innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ta maimaita sau kusan hudu tana qoqarin tattara hankalinta da a yanzu tasan tafi buqatarsa sama da komai.
A hankali ta sanya hannu ta zare falaak daga jikinta,sai ta miqa hannun ta damqi tsintsiyar hannun falaak.
"Tana ina?".
"Sassanta......amma mammina tasa an hana kowa shiga.......daga ita sai bappi ne a ciki" Falaak din ta fadi cikin jin ciwon yadda taso shiga din,amma mammina ta leqo tana gaya mata kukanta zai tta'azzara yanayin da akhnan take ciki,so ta tsaya a baya ta mata addu'a.
Ko gane sauran bayanan falaak morsa batayi ba,tasan kawai tace dasu armelle
"Ku wuce bakin ayyukanku" Taci gaba da jan hannun falaak suna takawa zuwa shiyyar da zata sadata da sassan akhnan din.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
[12/31, 19:36] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 05*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
________________________________
Shuru kawai parlor din ya dauka,kai kace babu wani sauran me rai dake raye a cikin sa. Cikin wani irin salubabben yanayi sultane ke tsaye gaban akhnan,cikin wani yanayi dashi kansa bazai iya fassarashi ba.
Tsahon mintuna kafin ya tsugunna gabanta a hankali,inda take kwance kawai,banbancinta da gawa qalilanne. Hannunsa ya sanya ta qasan duvet din da take lullube dashi ya kamo hannunta,wani irin sanyi tafukan hannun nata sukayi,a hankali ya furta.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un". A nutse haisam dake tsaye gefe daya ya daga idanunsa ya zube akan sultane din,dukkan jikinsa yana jin ya masa wani iri. Tun wanzuwarsu a gurin har zuwa kwantar da ita da akayi da bata taimakon farko da yayi gudun kada illar gubar tayi barnar da ba zata gyaru ba,bai sake daga idanunsa ya kalleta ba ko sau daya.
Kwata kwata tsaiwarsa a gurin ma ta zame masa kamar lalura ne kawai saboda shigowar me martaba a sanda yake qoqarin fita,shigowar da sultane din kuma yayi,wani yanayi yake ciki da yake buqatar wani a kusa,wanin da zai riqe koda hannunsa ne yaji sassautin abinda yakeji.
Yanayin sultane din kadai ya gama bayyanawa haisam rudun da yake ciki,saidai zallar jarumta irin ta basaraken mutum,irin jarumtar dake nasa jinin kenan shima,irin jarumtar kuma da aka sani cikin jinin dukka wanda yake da jibi da SARAUTA.
"Muhammad" Sultane ya kirashi muryarsa da tayi laushi can qasa,kansa kawai haisam ya daga yana duban sultane din,saidai kafin yace komai muryar mammina cikin wani irin yanayi ta tunkarosu,sai kuma gata ta iso.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.......ya Allah.......ya Allah ka taimakemu.....ka rufa mana asiri.....kar ka bari wani abu ya samu yarinyar nan" Tayi maganan sanda take wucewa kai tsaye zuwa ga inda akhnan ke kwance numfashinta yana fita da wani irin yanayi da ba haka ya saba fita ba.
Gaba daya ta rungumeta cikin jikinta,wani irin kuka me tafe da hawaye ya qwace mata.
"Me yasa zaki aikata haka?,me yasa zaki illata kanki akhnan?.....ashe dama baki haqura ba?,dama baki janye kalamanki ba?,dama da gaske kike sai kin sha din........Allah ka taimakamin.......d'iyata ya Allah" Ta qarashe fadi tana sakin wani sabon kukan.
A hankali ya lumshe idanunsa sai kuma ya budesu,ya motsa a hankali yana gyara hannun rigarsa. Yana da nufin fita ne daga sassan gaba daya,don dama dole ke tsaye dashi a gurin,shi ya gama nashi part din,ya gama iya abinda zai iya. Bayason kallon drama din matar nan,kanshi shuru yafi buqata,hayaniyarta kuma ya karanci me yawa ce,da gaske damunsa zatayi.
"Muhammad........ba wani qarin taimakon da zaka mata?,likita baya kusa........amma yana hanyan isowa" Sultane ya fada cikin wata muguwar karaya yana dauke idanunsa daga kan mammina,kalamanta kuma suna huda qirjinsa,karayar data sanya tausayin sultane din saukar masa lokaci guda.
Lallai koda ba'a gaya maka ba zaka fahimci tsantsar soyayyar da sultane yakewa akhnan......sosai haisam ya gama fahimtar irin girman wannan qauna da soyayyar....wadda a ransa yakejin indai har yana son yarinyar har haka,to lallai ba qaramin qoqari yayi ba gurin horata ta hanyar aura mata wanda babban muradinta shine ya janye aura mata shi din.
"Akwai........za'a iya bata injection na Atropine" Ya furta a hankali,duk da yana jin kamar bai dace ya buda sirrinsa ba ko yaya ne.
Ga duk wanda ya qware a aikin binciken sirri a qasarsu,suna da horo na musamman wajen irin wadannan abubuwa saboda shirin kota kwana da kuma yiwuwar faruwar irin wadannan abubuwa kan daya daga cikinsu ko su kansu,sirrinsu ne da ba wanda ya sani,amma a yanzun da yake kallon tsakiyar idanun sultane din dake jirkice da tarin rudani da abubuwa iri daban daban......yanajin kamar wajibinsa ne ya taimaka.......kwanyarsa kuma na bankado masa daya daga cikin ayoyin qur'ani dake fadin DUK WANDA YA RAYA RAI QWAYA DAYA TAMKAR YA RAYA MUTANE GABA DAYA NE kamar yadda farkon ayar ke fadin idan ka kashe rai daya kaman ka kashe al'umma gaba daya ne.
Cikin wani irin gaggawa da zafi sultane ya saki umarnin nemo ruwan allurar ko a ina yake cikin qasa da mintuna goma.
*MORSA*
Dukka hankalinta dama tunaninta baya tattare da ita sam sam. Kawai dai tana d'aga qafarta tana kuma saukewa ne bisa tabbacin ba zata fadi ba,saboda ko ina na cikin gidan wani shimfidadden terrazzo ne me matuqar kyau da daukan hankali.
Kukan falaak kawai ke yawo cikin qirjinta da kunnuwanta,yadda falaak ke kuka yana sake tabata gami da sake motsa wani tashin hankalin a tare da ita. Wai akhnan ta sha guba?......guba dai?,ko daya hankalinta da zuciyarta basu dauka ba basu kuma nutsu ba.
Tana tunkaro sassan akhnan din duk wani hadimi dake tsaron gurin wanda mammina ta sanya ya soma buda mata hanya ba tare da tace komai ba,taci gaba da kutsawa falaak na riqe a hannunta.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Shine abinda bakin mammina ke maimaitawa tana riqe da akhnan cikin jikinta. Ko ina ina jikin mammina rawa yake,wani irin tashin hakali yana bayyana kansa saman fuskarta,hatta da hailalan da take ambatawa bakinta rawa kawai yakeyi.
A nutse da irin nutsuwar da ba kasafai take barin gangar jikinsa ba ya taka zuwa ga box din da yasa aka shigo masa dashi yanzun na allurar daya buqata din.
Kunnuwansa suna kan sautukan mammina da bakinta ya kasa daina maimaita hailalan da takeyi duk da yadda yakeso ya raba kanshi da hayaniyar matar,a daidai lokacin da sultane ke tsaye saman kansu idanunsa akan akhnan din cikin wani irin yanayi me wuyar fassara,ya kasa matsawa,abinda ke yawo cikin kansa kawai shine zantukan mammaina data furta dazu
"Kenan dama ita ta shirya poisoning din kanta?" Tambayar da yaketa maimaitawa kansa ita kenan.
Tun dazun ya gaza sake cewa komai,yanayinsa wani yanayi me wahalar fassara da kai tsaye ba zaka iya karantar abinda yake ranshi ba.
Tas haisam ya zuqe ruwan allurar da nutsuwa,a daidai sanda gaba daya hankalin mammina ke kanshi. Qatotuwar ayar tambaya ta ajiye
"Me ya hada malami da iya allura?.....meye hadinsa duka duka da harkar lafiya?" Ta fadi tana nazartarshi da wani irin yanayi da ba lallai ka fahimta ba.
Yana fidda iskar data shiga cikin syringe din sallamar morsa safiyya da muryarta ke shaking ta wanzu a falon,abinda ya janye hankalinsu su duka kenan,banda haisam da yaci gaba da abinda yake a qoqarinsa na bata allurar ya kuma fice daga gurin don bawa iyalin daman ci gaba da abinda ya shafesu.
"Sheik muhammad" Falaak dake maqale a bayan morsa safiyya ta fadi da sautin da morsa dince kawai ta jishi,saita dan dubi sashen da falaak din ke kalla kafin ta zare idanunta daga kansa. A karon farko data kalleshi cikin yanayinta da ba na nutsuwa ba,ta hangi tarin kamala da kuma nutsuwa a tattare dashi.
Wani kallo mammina din ke bin morsa safiyya dashi,saidai kallo ne dake qudundune tsakanin duffan daba kowa zai masa fahimta ta kai tsaye ba.
Kai tsaye morsa safiyya ta isa gabansu idanunta akan akhnan dake jikin mammina. Idanunta suna bude,amma ba alamar tana iya gani ne ko gane kowa......ba kuma alamar tana tare dasu a duniyarsu,ba kuma alamar tana fahimtar abinda ke gudana a dakin.