Sashe 15
Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba wani naqasu ko kasawa da saamee ke dashi......ta cika macen da za'a sota da dukkan quality dinta,to amma hakanan baisan me yasa yakejin a ransa bata hau mizani ba. Ya jima yana bincikar kansa me yasa yakejin kamar saamee ta rasa wani abu?.....me yasa yakejin kamar akwai wani hali dabi'a da yake nema da saamee ta rasa?. Ya dade yana tambayar kansa indai har saamee nada wani dabi'a ko halayya data rasa.....wacece?.....wacece zatayi?,wacece kuma zata cika?. Amsar daya ce har yau BAI SANI BA.....BAISAN ME TA RASA BA.....BESAN KUMA ME TAKE NEMA BA.
Abu daya daya sani wanda baisan ko yana da alaqa da ganin gazawar saamee ba bawai don ta gaza din ba?..... Mutum ne da komai yafison ya mallakeshi da JARUMTARSA......komai yafison yayi YAQI kansa bawai ya sameshi daga kwance ba. Jininsa na GWAGWARMAYA NE......yana ganin komai akayi yaqi a kansa yafi zama da kima da daraja.....anfi kuma riqeshi da dukkan qarfi.......har abada kuma idan zaka kalli wannan abun zakafi tuna kanka da sunan JARUMI bawai LUSARIN NAMIJI BA.
Idanunsa da suka shanye ya daga a hankali,daidai sanda yaga gilmawar inuwa ta bayan labulen dake tsakanin parlor din Bedroom din nasa. Kamar gilmawar walqiya komai ya bace,ya zubawa gurin idanu a hankali kafin kuma wani miskilin murmushi ya subuce masa.
"Wannan shine iya zurfinka?......wannan shine iya qwarewar taka?" Ya furta can qasan ransa yana gyada kansa da cikakkiyar nutsuwa sannan ya miqe yana takawa a nutse yana nufar parlor din.
Baiyi zaton komai zaizo da sauqi har haka ba.....bai dauka kuma zatayi zaben lusarin me binkice irin wannan ba. Amma ta wani gefen sai ya mata uzuri,tabbas ya sani,inda tasan girman had'arin da yake dashi......dan sanya idanu na gaske zata nemo ta hadashi dashi ba wannan qaramin halittar ba........amma ko meye shi ya masa daidai......zaiyi wasa da hankalinta yadda ya kamata.
*AKHNAN*
Komai batace musu ba,illa kunnuwanta kawai data basu tana sauraren mitarsu a kanta sanda birra ke miqa mata kayanta tana shiryawa da kanta.
Tanaso komai zasuyi cikin daren nan da mammina suyishi a qare.......mafita take nema,ba kuma mafita irin wannan da sultane ya bata ba. Mafitar da zata fita gaba daya daga cikin sharuddan sultane,taci gaba da rayuwarta kamar yadda take a baya.
Duk kusan mita da qorafinsu akan ta koma sahel couture ne. Jinsu kawai takeyi.....yadda takeji da kamfanin.....yadda kamfanin yake qunshe da wani irin tasiri a rayuwar qasar niger gaba daya,da yadda aikinta tuquru yakai kamfanin wani tudu da bata taba tsammani ba ko a mafarki abun ya bata tsoro. Daidai da sultane abun ya daure masa kai.......ya kuma sake daga darajar akhnan a zuciyarsa da idanunsa. Wasu irin tarin nasara da ninkuwa da komai na kamfanin yayi wanda ba wanda a cikinsu ya taba hango masa nasara irin haka a kurkusa.
Sahel couture wata kyauta ce ta ba zata da sultane ya taba mata a rayuwa. Ruhin dukiyarsa gaba daya,kuma sirrin dukiyarsa,ba zatan data girgiza mutane da yawan gaske,ta sake kuma haska girman matsayinta a zuciyar sultane din,wanda hakan ya sanyata alfahari me yawan gaske. A wannan lokutan bata taba tunani ko kawowa ba akwai wani abu me suna DAMUWA da yake da tasirin nesanta da Niamey ma gaba daya bare sahel couture din kansa ba.
A nutse ta karbi bakin mayafin da birra ke riqe dashi,ta kuma soma Rolling saman sumarnan tata me sulbi da data kwanta luf saboda yadda birra ta gyarata sosai ta matse mata ita cikin siririn band da bazai takurawa darenta ba.
"Ba wani tunani nawa da yake daidai a yanzu.....ba wani sauran qwarin gwiwar data ragemin da zata ban damar jagorantar sahel couture yanzu.....mammina tasan da hakan,ta kuma gaya miki ke kikafi cancanta kici gaba da jagorantarsa......bansan me kike jira ba" Tayi maganar a nutse da tasirin izzarta cikin fitar kowanne lafazi daga labbanta.
"Kinsan wani abu?" Shehnaz ta fada tana qarewa akhnan kallo,wadda tayi wani irin sassanyan kyau,kai ba zakace nan da wanni zata kwanta ba,saika dauka ta shirya ne don fita wani guri daban a wajen gidan.
Akhnan bata amsa ba,sai aisa data dubi shehnaz alamun ita suke saurare.
"Ke kika maida komai me zafi akhnan.......amma inda zaki sassauta zuciyarki......wallahi na hango miki wani kyakkyawan zabi....zabin da nake da yaqinin zaki samu nutsuwar da baki taba hange ko tunani ba......sheikh haisam akhnan......."
Wata irin wawiyar juyowa akhnan din tayi......sannan ta zubewa shehnaz idanun nan nata dake da surkin kwarjini irin na d'iyoyin da sarauta ta game jininsu.
"Koma meye kikeson fada abu mafi alkhairi ki barshi a bakinki.......idan kuma har shaye shaye kika fara shehnaz daga yau ba zaki sake marmarin kusantar irin abinda kika sha ba ballantana ya suranta miki qazamin tunani irin wannan har abada.........ba wani namiji daidai dani a yanzu a duniyar nan......bansan ko gaba ba,koda qaddara ta sanya na amsa sunan MATAR AURE.....to koma waye wannan mijin....." Sai bata qarasa ba ta girgiza kai da wani irin yanayi daya tabbatar musu da tarin abubuwan dake binne cikin zuciyarta,take ganin baki yayi kadan ya furtasu daidai.
"Zanje naga mammina" Iya abinda ta fada musu kenan ta soma takawa tana fita a dakin.
Cikin qasaita da jinta cikin cikakken tsaro take takawa a filin da zai kaita kai tsaye zuwa sassan mammina din. Wata irin iska ce me ratsa jiki take kadawa gami da kai kawo daga kowanne kusurwoyin duniya.......idanunta ta zare daga duban qasaitattun katangun dake zagaye dasu,wadanda iya kallonsu kawai na sake sanya mata jin izza da qasaita. Tabbas.....lallai inda za'a tasheta a wata rayuwa ta daban,a kuma bata zabi,babu shakka zata yita zabar kasancewarta cikin ahalin SARAUTA.
Iya ginin da masarautar agadez ta mallaka da wani irin tsari da aka zamanantar dashi tayi imanin zai wahala a samu tsarin masarauta tasu kaf Africa.
Sararin samaniya ta maida dubanta,duk da cewa duhun dare mamaye saman gaba daya,hakana bai hana hasken farin wata nuna hadarin dake lullube a saman ba,hadarin da ya jima yana haduwa,kuma a yau kamar yana nuna ya tumbatsa da yawa,nan da wasu mintuna ko awanni yana iya hade jikinsa dukka tsaf,ya kuma jirayi umarnin sarkin sarakuna wajen shayar da al'ummar agadez dama na nijer gaba daya ruwan farko.
Iskar ta mata dadi qwarai.....kamar yadda yanayin ya mata dadi.......saidai hakan bai hana kalaman shehnaz yin suya sosai a qirjinta ba.
Iya fitar furucin daga bakin shehnaz sai takejin kamar ta qasqanta......kamar neman kai ake da ita......yanzun har araharta takai haka?......me yasa sultane yakeson lallai sai ya zabtare dukkan wani girma nata da darajarta ya watsar?,har wadanda kimarsu da martabarsu batakai ba suyi tsammanin sunkai tsaikon da zasu kusanci iyakokinta?. Ba wani taku da zatayi ba'a zube a qasa bisa saman gwiwoyi ba cikjn gaisuwar ban girma,wanda ko daya bata amsa ba sai birra dake amsa mata.
Wannan din dabi'arta ce......kaman yadda yake girmanta ne......baka isa tana takawa a farfajiyar guri ba kaima naka qafafun suci gaba da takawa ba,zaka jira har sai sanda ta bada baya ko tabar gurin. Girman da dukkan al'ummar masarautar ke bata banbancinsa kadanne dana sultane,kowa fata yake......qoqari yake ya kyautata mata da dukkan girmamawa saboda farincikin sultane.
Tun daga qofar mammina ta farko masu tsaron qofar ke janyewa gami da sauke idanunsu qasa tare da kaucewa kallon akhnan din da yake kasancewa zunubi ne ga kowanne d'a namiji cikin masarautar muddin ba ita ta lamunce maka hakan ba.
*MAMMINA*
Zare wayar dake kunnenta tayi a nutse tana duban bakin qofar inda yalwa ke durqushe ta yadda bata iya hangota.
"Ina neman izinin yin bayani idan an lamuncemin haka" Ta fada da wani yanayi da ya gayawa mammina akwai labari a bakin yalwa din.
"An baki" Ta fada tana gintse wayar gami da ajiyeta.
"Gimbiya akhnan na dab da shigowa sassannan". Shiru mammina tayi......kafin wani shu'umin murmushi ya subuce mata.
Tun kwanaki data diba mata a ranta basu cika ba sai gashi akhnan din ta gaza jurewa ta nemota?. Lallai ba shakka ta wannan fannin tayi tinjimin aiki da ya kamata ta yabawa kanta da kanta. Tayi aikin daya zame mata makami mafi muni a idanu da zuciyar morsa safiyya......ta yadda bata yadda za'ayi morsa safiyya ta iya karbe akhnan daga hannunta......har gaban abada,koda itace tace akhnan din ta koma hannun morsa safiyya din,ta juya akalar girma da biyayya shawari da matsayin uwa data bata.
"Banaso kai tsaye a barta ta iskeni......banaso ta samu ganina kai tsaye cikin sauqi kaman yadda yake a baya". Ta fada fuskarta na sake fadada da fara'a.
"An gama" Yalwa ta fada tana miqewa da hanzari da kuma sassarfa tana sauka qasa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Sanda tazo matakalar qarshe akhnan na shigowa. Ita daya ce,ta baro birra a baya,don birra din tazo iyakacin shingen da ba wanda ya isa ya d'arashi cikin bayi ko hadimai.
Qasa yalwa tayi da kanta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku amma idar da abinda ran uwar gijiyarta keso ta kuma tsara tamkar bauta yake a wajenta.
"Allah ya taimaki hasken agadez......Allah ya baki yawan rai da nisan kwana......kamar giwa ta samu kwanciya nake zato......ko za'ayi haquri a koma zuwa gobe?". Cak akhnan ta tsaya daga daga qafarta da tayi zuwa stairs na farko sannan ta waiwayo ta zubewa yalwa idanunta.
"Kinsan dawa kike magana?" Ta furta cikin izzar data kada hantar yalwa.
"Kinsan me kike cewa?......."
"Tuba nake ranki ya dade,ayimin aikin rai" Ta fada muryarta da labbanta dukka suna rawa saboda tsananin tsoron akhnan din daya shigeta. Kamar ba zata sake cewa komai ba......amma saita jinjina kai ta juya taci gaba da takawa.
"Koda wasa karki sha'awar xaki sake maimaitawa"
"Na tuba in sha Allahu" Ta amsa mata tana jin gwiwoyinta kamar ba zasu dauketa ba.
Duk taku daya da takeyi ranta yan sake suya,yaushe tayi arahar da kamar yalwa wai itace zata mata iso?,iso fa akan mammina......mamminarta na da bau irinta kaf rayuwarta.
Kaman yadda batayi sallama ba bayan ta canko dakin da mammina din zaune,sai kawai ta jingina da qofar dakin tana harde hannuwanta a qirjinta,fuskarta shimfide d wani nannuyan yanayi.
Abu daya daya sani wanda baisan ko yana da alaqa da ganin gazawar saamee ba bawai don ta gaza din ba?..... Mutum ne da komai yafison ya mallakeshi da JARUMTARSA......komai yafison yayi YAQI kansa bawai ya sameshi daga kwance ba. Jininsa na GWAGWARMAYA NE......yana ganin komai akayi yaqi a kansa yafi zama da kima da daraja.....anfi kuma riqeshi da dukkan qarfi.......har abada kuma idan zaka kalli wannan abun zakafi tuna kanka da sunan JARUMI bawai LUSARIN NAMIJI BA.
Idanunsa da suka shanye ya daga a hankali,daidai sanda yaga gilmawar inuwa ta bayan labulen dake tsakanin parlor din Bedroom din nasa. Kamar gilmawar walqiya komai ya bace,ya zubawa gurin idanu a hankali kafin kuma wani miskilin murmushi ya subuce masa.
"Wannan shine iya zurfinka?......wannan shine iya qwarewar taka?" Ya furta can qasan ransa yana gyada kansa da cikakkiyar nutsuwa sannan ya miqe yana takawa a nutse yana nufar parlor din.
Baiyi zaton komai zaizo da sauqi har haka ba.....bai dauka kuma zatayi zaben lusarin me binkice irin wannan ba. Amma ta wani gefen sai ya mata uzuri,tabbas ya sani,inda tasan girman had'arin da yake dashi......dan sanya idanu na gaske zata nemo ta hadashi dashi ba wannan qaramin halittar ba........amma ko meye shi ya masa daidai......zaiyi wasa da hankalinta yadda ya kamata.
*AKHNAN*
Komai batace musu ba,illa kunnuwanta kawai data basu tana sauraren mitarsu a kanta sanda birra ke miqa mata kayanta tana shiryawa da kanta.
Tanaso komai zasuyi cikin daren nan da mammina suyishi a qare.......mafita take nema,ba kuma mafita irin wannan da sultane ya bata ba. Mafitar da zata fita gaba daya daga cikin sharuddan sultane,taci gaba da rayuwarta kamar yadda take a baya.
Duk kusan mita da qorafinsu akan ta koma sahel couture ne. Jinsu kawai takeyi.....yadda takeji da kamfanin.....yadda kamfanin yake qunshe da wani irin tasiri a rayuwar qasar niger gaba daya,da yadda aikinta tuquru yakai kamfanin wani tudu da bata taba tsammani ba ko a mafarki abun ya bata tsoro. Daidai da sultane abun ya daure masa kai.......ya kuma sake daga darajar akhnan a zuciyarsa da idanunsa. Wasu irin tarin nasara da ninkuwa da komai na kamfanin yayi wanda ba wanda a cikinsu ya taba hango masa nasara irin haka a kurkusa.
Sahel couture wata kyauta ce ta ba zata da sultane ya taba mata a rayuwa. Ruhin dukiyarsa gaba daya,kuma sirrin dukiyarsa,ba zatan data girgiza mutane da yawan gaske,ta sake kuma haska girman matsayinta a zuciyar sultane din,wanda hakan ya sanyata alfahari me yawan gaske. A wannan lokutan bata taba tunani ko kawowa ba akwai wani abu me suna DAMUWA da yake da tasirin nesanta da Niamey ma gaba daya bare sahel couture din kansa ba.
A nutse ta karbi bakin mayafin da birra ke riqe dashi,ta kuma soma Rolling saman sumarnan tata me sulbi da data kwanta luf saboda yadda birra ta gyarata sosai ta matse mata ita cikin siririn band da bazai takurawa darenta ba.
"Ba wani tunani nawa da yake daidai a yanzu.....ba wani sauran qwarin gwiwar data ragemin da zata ban damar jagorantar sahel couture yanzu.....mammina tasan da hakan,ta kuma gaya miki ke kikafi cancanta kici gaba da jagorantarsa......bansan me kike jira ba" Tayi maganar a nutse da tasirin izzarta cikin fitar kowanne lafazi daga labbanta.
"Kinsan wani abu?" Shehnaz ta fada tana qarewa akhnan kallo,wadda tayi wani irin sassanyan kyau,kai ba zakace nan da wanni zata kwanta ba,saika dauka ta shirya ne don fita wani guri daban a wajen gidan.
Akhnan bata amsa ba,sai aisa data dubi shehnaz alamun ita suke saurare.
"Ke kika maida komai me zafi akhnan.......amma inda zaki sassauta zuciyarki......wallahi na hango miki wani kyakkyawan zabi....zabin da nake da yaqinin zaki samu nutsuwar da baki taba hange ko tunani ba......sheikh haisam akhnan......."
Wata irin wawiyar juyowa akhnan din tayi......sannan ta zubewa shehnaz idanun nan nata dake da surkin kwarjini irin na d'iyoyin da sarauta ta game jininsu.
"Koma meye kikeson fada abu mafi alkhairi ki barshi a bakinki.......idan kuma har shaye shaye kika fara shehnaz daga yau ba zaki sake marmarin kusantar irin abinda kika sha ba ballantana ya suranta miki qazamin tunani irin wannan har abada.........ba wani namiji daidai dani a yanzu a duniyar nan......bansan ko gaba ba,koda qaddara ta sanya na amsa sunan MATAR AURE.....to koma waye wannan mijin....." Sai bata qarasa ba ta girgiza kai da wani irin yanayi daya tabbatar musu da tarin abubuwan dake binne cikin zuciyarta,take ganin baki yayi kadan ya furtasu daidai.
"Zanje naga mammina" Iya abinda ta fada musu kenan ta soma takawa tana fita a dakin.
Cikin qasaita da jinta cikin cikakken tsaro take takawa a filin da zai kaita kai tsaye zuwa sassan mammina din. Wata irin iska ce me ratsa jiki take kadawa gami da kai kawo daga kowanne kusurwoyin duniya.......idanunta ta zare daga duban qasaitattun katangun dake zagaye dasu,wadanda iya kallonsu kawai na sake sanya mata jin izza da qasaita. Tabbas.....lallai inda za'a tasheta a wata rayuwa ta daban,a kuma bata zabi,babu shakka zata yita zabar kasancewarta cikin ahalin SARAUTA.
Iya ginin da masarautar agadez ta mallaka da wani irin tsari da aka zamanantar dashi tayi imanin zai wahala a samu tsarin masarauta tasu kaf Africa.
Sararin samaniya ta maida dubanta,duk da cewa duhun dare mamaye saman gaba daya,hakana bai hana hasken farin wata nuna hadarin dake lullube a saman ba,hadarin da ya jima yana haduwa,kuma a yau kamar yana nuna ya tumbatsa da yawa,nan da wasu mintuna ko awanni yana iya hade jikinsa dukka tsaf,ya kuma jirayi umarnin sarkin sarakuna wajen shayar da al'ummar agadez dama na nijer gaba daya ruwan farko.
Iskar ta mata dadi qwarai.....kamar yadda yanayin ya mata dadi.......saidai hakan bai hana kalaman shehnaz yin suya sosai a qirjinta ba.
Iya fitar furucin daga bakin shehnaz sai takejin kamar ta qasqanta......kamar neman kai ake da ita......yanzun har araharta takai haka?......me yasa sultane yakeson lallai sai ya zabtare dukkan wani girma nata da darajarta ya watsar?,har wadanda kimarsu da martabarsu batakai ba suyi tsammanin sunkai tsaikon da zasu kusanci iyakokinta?. Ba wani taku da zatayi ba'a zube a qasa bisa saman gwiwoyi ba cikjn gaisuwar ban girma,wanda ko daya bata amsa ba sai birra dake amsa mata.
Wannan din dabi'arta ce......kaman yadda yake girmanta ne......baka isa tana takawa a farfajiyar guri ba kaima naka qafafun suci gaba da takawa ba,zaka jira har sai sanda ta bada baya ko tabar gurin. Girman da dukkan al'ummar masarautar ke bata banbancinsa kadanne dana sultane,kowa fata yake......qoqari yake ya kyautata mata da dukkan girmamawa saboda farincikin sultane.
Tun daga qofar mammina ta farko masu tsaron qofar ke janyewa gami da sauke idanunsu qasa tare da kaucewa kallon akhnan din da yake kasancewa zunubi ne ga kowanne d'a namiji cikin masarautar muddin ba ita ta lamunce maka hakan ba.
*MAMMINA*
Zare wayar dake kunnenta tayi a nutse tana duban bakin qofar inda yalwa ke durqushe ta yadda bata iya hangota.
"Ina neman izinin yin bayani idan an lamuncemin haka" Ta fada da wani yanayi da ya gayawa mammina akwai labari a bakin yalwa din.
"An baki" Ta fada tana gintse wayar gami da ajiyeta.
"Gimbiya akhnan na dab da shigowa sassannan". Shiru mammina tayi......kafin wani shu'umin murmushi ya subuce mata.
Tun kwanaki data diba mata a ranta basu cika ba sai gashi akhnan din ta gaza jurewa ta nemota?. Lallai ba shakka ta wannan fannin tayi tinjimin aiki da ya kamata ta yabawa kanta da kanta. Tayi aikin daya zame mata makami mafi muni a idanu da zuciyar morsa safiyya......ta yadda bata yadda za'ayi morsa safiyya ta iya karbe akhnan daga hannunta......har gaban abada,koda itace tace akhnan din ta koma hannun morsa safiyya din,ta juya akalar girma da biyayya shawari da matsayin uwa data bata.
"Banaso kai tsaye a barta ta iskeni......banaso ta samu ganina kai tsaye cikin sauqi kaman yadda yake a baya". Ta fada fuskarta na sake fadada da fara'a.
"An gama" Yalwa ta fada tana miqewa da hanzari da kuma sassarfa tana sauka qasa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Sanda tazo matakalar qarshe akhnan na shigowa. Ita daya ce,ta baro birra a baya,don birra din tazo iyakacin shingen da ba wanda ya isa ya d'arashi cikin bayi ko hadimai.
Qasa yalwa tayi da kanta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku amma idar da abinda ran uwar gijiyarta keso ta kuma tsara tamkar bauta yake a wajenta.
"Allah ya taimaki hasken agadez......Allah ya baki yawan rai da nisan kwana......kamar giwa ta samu kwanciya nake zato......ko za'ayi haquri a koma zuwa gobe?". Cak akhnan ta tsaya daga daga qafarta da tayi zuwa stairs na farko sannan ta waiwayo ta zubewa yalwa idanunta.
"Kinsan dawa kike magana?" Ta furta cikin izzar data kada hantar yalwa.
"Kinsan me kike cewa?......."
"Tuba nake ranki ya dade,ayimin aikin rai" Ta fada muryarta da labbanta dukka suna rawa saboda tsananin tsoron akhnan din daya shigeta. Kamar ba zata sake cewa komai ba......amma saita jinjina kai ta juya taci gaba da takawa.
"Koda wasa karki sha'awar xaki sake maimaitawa"
"Na tuba in sha Allahu" Ta amsa mata tana jin gwiwoyinta kamar ba zasu dauketa ba.
Duk taku daya da takeyi ranta yan sake suya,yaushe tayi arahar da kamar yalwa wai itace zata mata iso?,iso fa akan mammina......mamminarta na da bau irinta kaf rayuwarta.
Kaman yadda batayi sallama ba bayan ta canko dakin da mammina din zaune,sai kawai ta jingina da qofar dakin tana harde hannuwanta a qirjinta,fuskarta shimfide d wani nannuyan yanayi.