← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 101

Sashe 82

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wata magana ce datazo masa a bazatar da baiyi tunani ba. Wata magana ce da bai taba tunanin jinta daga bakin morsa safiyya ba. Wata irin BA ZATA CE a tare dashi data sanyashi yin shuru na wani lokaci,kaman yadda ya saba bawai kai tsaye yake amsa maka magana ba har sai ya bawa qwaqwalwarsa damar numfasawa na wani lokaci. Ta yaya zai fara auren da bai shirya masa ba?......da yarinyar da yayi imanin komai nasu baizo daya ba?. Babu ta inda sukayi tarayya ita dashi......ba wani abu dake nuna daidaito a tsakaninsu......ta yaya ma?....wanne irin aure ne haka wanda ko da wasa bai taba hakaitoshi ba?. Idan kuma yace zaiyi auren CETO na wani lokaci ne.....ai ya sani cewa haramunne a qulla aure bisa wata yarjejeniya,yarjejeniyar ma ta rabuwa.....baisan daga inda zai samo halascin haka ba. Ta kowacce fuska baiga dacewa ko yuwuwar abun ba.......don ya sani.....aure ba abune ba wasa ba......sunna ce mafi qarfi da ba wasa a cikinta ko kadan,ta yaya zai fara abinda baiyi niyya ba?,bai shirya ba?.

Koda morsa safiyya bata nema ba.....koda bata buqata ba ya yankewa kansa yin revision a tarihin safeena.......ya azawa kansa wannan nauyin ba tare da shawarar kowa ko tunani na biyu tsakaninsa da zuciyarsa ba. Akwai abubuwa da yawa da yake buqatar saninsu......akwai abubuwa da yawa da bai kamata a barsu suci gaba da tabbata a haka ba. INA AHMAD ina jaririn dan yayansa?. Sun narke kenan?,sun shafe daga rayuwar safeena?,saboda tsoron salwantar rayukansu sai a tabbata a haka?. Jikinsa yana bashi tun daga farkon labarin cewa komai daya faru na farko dana qarshe a qulle suke da juna.....komai daya faru yana da alaqa da dana baya,ya zama dole GASKIYA tayi magana......ya zama dole wannan ZALUNCIN ya gushe hakanan.....ya zama dole a tabbatar da ZURI'AR SAFEENA suyi rayuwa me 'yanci kamar yadda kowacce zuri'a take rayuwa.....AMMA BANDA WANNAN AUREN.....wannan auren wani abune da bazai daukeshi a wuyansa ba sam.

Shuru itama morsa safiyya din kawai tayi,yayin da zuciyarta dake lullube a qirjinta take wani irin tsalle. Rawa kawai zuciyarta takeyi,tana cike da fata da sanya rai,tana cike da zullumin me zaya amsa mata dashi?.....tana tsaka da wannan zullumin e ya dubeta a hankali.

"Komai a hankali ake binsa da kuma nutsuwar da bazata kawo dana sani ba daga baya......."

"Kada ka bani amsa yanzu don Allah muhammad na roqeka.....kaje kayi tunani.....kayi tunani daga yau har zuwa kwana uku hudu biyar harma sati......amma ka sani,indai ka wuce haka komai zai iya faruwa da khadeeja" Ta qarasa maganar da wani irin rauni cikin idanunta. Zare idonsa yayi yana jin raunin nata yana tabashi,ya miqe a nutse,bayanansa dukka ya adana. Bawai zai iya gaya mata a halin daya ganta cewa kai tsaye bai karbi magananta ba.....don yasan aikata hakan zai sake jefata ne kawai cikin wani rudani na daban. Ta idanunta ya karanci dukkanin FATANTA yana kansa......ta sanya buri da fata me yawa a kansa.

"Na barki lafiya" Ya fada yana takawa a hankali.

"Na gode sosai muhammad da amsa kirana.....da jumurin zaman saurarona da kayi......na zabeka nayi kuma magana dakai a matsayin mutum me tsoron Allah.......Allah yana taimakon bawa muddin bawa bai gushe ba yana cikin taimakon dan uwansa" Magananta ta qarshe hadisi ne......hadisin da yaji yana kakkaryashi a hankali,don haka bai waiwaya ba bai kuma tsaya ba,yaci gaba da takawa yana fita a hankali daga sassan.

Ajiyar zuciya morsa safiyya ta sauke,ta gyada kanta a hankali tana daga hannuwanta zuwa sam. Wata sirrintacciyar addu'a ce tsakaninta da ubangijinta,ta shafa a nutse sannan ta waiwaya ta dauki wayarta tana laluben hairaan don ta turo mata armelle.

So yake ya koma personal residence dinsa.....so yake ya sake nisa da kowa da komai ko zai samu kwanyarsa tayi resettling na magangnun morsa safiyya da yakejin sun wani irin cika masa kwanya......amma kuma bai kamata daga shigowarsa gidan ace har ya sake fita ba. Saidai duk da haka hakan bai hanashi kebe kansa ba,yabar maleek da omar a qasa,ya haura zuwa samansa bayan ya sauya kayan jikinsa,sannan yayi zaune saman bedroom balcony ta bayan wasu flowers. Relaxing yayi sosai saman wani foldable bed dake a gurin,ya lumshe idanunsa yana sake bitar dukkanin labarin cikin kansa.

Ya jima cikin wannan yanayin,har zuwa sanda jikinsa ya bashi lokacin sallar magariba ya gabato,ya bude idanunsa a nutse ya jawo wayarsa dake gefansa,ya tarar da tarin miscal harda na omar da maleek,qarshe yaga gajeran saqon maleek dake gaya masa sun fita wani guri shida omar. Baibi kiran nasu ba tunda ya fahimci ma'anar kiran,sai kawai ya kira beeno ya fada masa ya duba email dinsa. Tashi yayi sosai ya zauna ya rubuta saqon da dukkan tsarin da yake buqatar ya aike masa.

Yana ji a jikinsa da ranshi akwai wani personal aiki da yahau kanshi......akwai xtra bincike daban da yahau kansa,ba kuma zai dakata ba har sai ya cimma gaci,har sai yakai inda jiki da zuciyarsa suke raya masa suke masa kuma tsammani.

Kamar kowanne lokaci da kansa ya dauki zafi irin wannan,sauraren karatun qur'ani da kuma karantashi ne kadai abinda yake zame masa nutsuwar zuciya da kuma hutu.

Yana zaune a farfajiyar da zata bashi daman ganin zirga zirgar kowa,da kuma sake karantar yadda dokarsa take aiki. Wani nazari yake sakeyi cikin gidan,motsin kowanne sashe,motsin kowanne hadimi da yanayin mu'amalarsa. Yana daga bangaren da ba lallai ka ankare dashi ba idan ba wucewa kazo yi ta gabansa ba,kuma koda kazo wucewar zaka dauka wani sha'ani daban ya keyi bawai nazarin yanayin gidan ba. Kunnensa manne da booth yana sauraren karatun qur'anin sheikh afif muhammad taj. Yawan lokuta yakan saurari qira'ar sheikh afif din,don yanason gani ko jin kamannin karatunsu da ake yawan fada. Tun yana da shekara sha takwas a duniya yake da nasa complete qur'an din audio,karatun da yawan manyan makarantun dake jimma dama Ethiopia gaba daya da wannan sound din suke amfani. Gidajen tv dana radio dinsu gaba daya.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Kiran daya shigo wayarsa ya sakashi tsaida karatun,ya maida hankalinsa akai a nutse sassanyar iskar dake tafe da hadari tana busashi da cikin Moroccan thobe din jikinsa data kasance olive color. Yanason abu me green qwarai,daga sanda yaji favourite colour na ma'aiki annabi muhammad s a w. Sai kuma kalar take bashi wani irin kwarjini gami da bayyanar da fatarsa me haske data d'ara ta al'ummar jimma oromia haske,wataqila hakan yana da nasaba da hutu da nutsuwa da yake ciki.

Nanay daya gani ya sanyashi katse karatun da yakeji,ya sanya hannu ya zare Bluetooth din ya ajiye,sannan ya katse kiran nanay yabi bayan kiran.

Ajiyar zuciya ta sauke sanda taji sallamarsa,hankalinta da tunaninta ya sake komawa kan saamee dake kwance saman gadon ROYAL CLINIC dake cikin masarautar jimma din. Tun ranar qarshe da sukayi waya da haisam din ta karanci damuwa ce fal zuciyar yarinyar,amma kawaici da alkunya irin na d'iya mace ya hanata nunawa. Tana tausayin dukkan wani maraya,saboda tasan me maraici yake nufi,maraicinma irin na UWA da ba'a maida makwafinsa.

"Ina fata ka yini lpy Muhammad?"

"Alhamdulillah nanay" Ya amsa mata safeena da safiyya suna dawo masa tar cikin idanu da zuciyarsa. Yana jin kamar ya shaidawa nanay din cewa yaga twin's dinta......amma yanaji a jikinsa lokaci baiyi ba,ba yanxu ba. Ba yanzu bane lokacin daya kamata ya fadi mata hakan ba,tabbas zata nema tako qafarta masarautar agadez ne......a yanzu kuma da komai ya sake warware masa ta labarin morsa safiyya bayajin ya kamata nanay din ta bayyana a yanzu.

"Ma sha Allah......magana zamuyi Muhammad" Ta furta a hankali tana tashi daga gaban gadon saamee gami da ficewa a hankali daga dakin.

"Yanzu kike buqata nanay?,ko zaki sanya wani lokaci da yayi miki saina kiraki?". Murmushi kadan ta saki,bata shakka ko kokwanton haisam.....biyayyarsa game da iyayensa ta dabance.....wata irin soyayya da jinqai yake gwada musu data jima bataga yaro irinsa ba.

"Idan nace zan bari zuwa wani lokaci muhammad sai na dinga ji kamar lokaci xai quremin......alfarma nake nema muhammad a gurinka" Kai ya girgiza da sauri kamar tana gabansa,ya zauna kuma sosai yana bata nutsuwarsa.

"Kinfi qarfin alfarma nanay,saidai umarni...." Murmushi me dan sauti kadan ta saki.

"Na sani muhammad.....amma wannan inaso a barshi a mazaunin alfarmar"

"Ina jinki nanay" Ya fadi cikin girmamawa.

"Ina tsoron wani abu muhammad......maraicin saamee yana tabani,don har yanzu bata saba da rayuwa ita kadai ba.....bata saba da rashin mahaifiyarta ba.....sai kuma na fahimci ta shiga wani yanayi da ita kanta nasan bata shirya masa ba". Shuru yayi yana saurarenta,kwanyarsa na qoqarin tattaro masa maganganun nanay guri daya ya aunasu a mizani.

"Muhammad.....ko kasan akwai alqawarin aure tsakaninka da saamee ta hannun mahaifiyarta kafin ta rasu?". Shuru ne ya gilma ta cikin kansa,kafin ya maida idanunsa a hankali ya lumshesu sannan ya budesu,zuciyarsa ta dauki

"Subhanallah" A hankali tana maimaitawa. Wani irin yanayi yana sake saukar masa,ya sake miqa hankalinsa akan nanay

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽

[2/9, 19:34] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 73*

"Ba wai hakan yana nufin lallai saika auri saame ba.....ba kuma hakan yana nufin zan tilastaka bane....aah,kamar ganin dacewar hadin mukayi dani da ita. Saidai tako ina ban hango ta yadda hakan zai kasance cikin lumana ba.....banga ta yadda zaka shaqu da saamee ba har ku fahimci juna ba saboda yanayin aikinka....a daidai lokacin na karanci kamar zuciyar yarinyar ta harbu da sonka...." Sosai maganan nanay ta shigeshi,ya fahimci hakan tunda dadewa,sannan omar ya jima yana maimaita masa.

"Na sani nanay" Ta fadi kansa tsaye. Ba wani abu daya kebance game dashi wai yana boyewa nanay,nanay dinsa itace aminiyarsa ta farko dake sanin komai daya danganceshi.
Chapter 82 · 0% Book details