← Book details Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 101

Sashe 43

Luu Luu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"An gama ranki ya dade......amma ki sani.....kallon kallo yana da hadari a wadansu lokutan,sai gwani shike iya satar kallo ya kuma fusgi abinda ganin ya bashi a sanda na kewayensa basu ankare da haka ba" Shuru ya ratsa tana fahimtar saqon da tamim ke aike mata da karkataccen harshe,saidai a yanzu zuciyarta bata aminta da shawarar tamim ba.

"Tafiyar hawainiyarmu bata kawomin alfanun komai ba bayaga MAFAKA,mafakar fa wani lokaci nake Allah wadai da ita...,hanzari nake buqatar gwadawa wannan karon,koda bayani ya motsa wasu sassa da zasu farka daga dogon baccin da suke......akwai wani taku na musamman.......dama ya kamaya susan KIFI NA GANINKA ME JAR KOMA!" Tayi maganan a wannan karon tana jin itama ta shirya ta kowanne bangare!!!.

_Uhmmmm.....me karatu,tafiyar fa zazzafa ce......abubuwa da yawa na shirin qulluwa agaba ba'a bigiren da aka shirya qulluwarsu ba,FADUWA DA NASARA......YIWUWAR FARA AFKUWAR SABON WASA TSAKANIN MAMMINA DA HAISAM......SHIN WASAN WAYE ZAIWA DADI?......WAZAI AFKA CIKI?.....KU BIYONI MUJE......._

zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

09166221261
KO
08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

09166221261

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261

*SHAIDAR BIYA*
09166221261

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽
[1/23, 20:08] +234 903 555 3736: 💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 02///PAGE 39*

*AKHNAN*

Idanu kawai takebin mammina dashi,wanda ta zauna tana bude kyautan da suka kusa cinye kaso daya cikin uku na dakin hutawar nata daya bayan daya kowanne tana ajiyeshi a gefe bayan ta bude.

"Ba zaki takura ba da rayuwa dashi.....nasanshi nasan mamanshi tsahon shekaru,bayason takura wannan shi ya hanashi aure tuntuni,yana neman matar da zatayi rayuwarta ne kawai ba tare data dameshi ba.....zaki samu dukkan wata izza daga sunan family dinsu kawai....zaki samu kalar sakakkiyar rayuwar da kikeso......kalli a iya yau kawai kyautukan alfarmar daya sauke miki" Mammina ta fadi tana ci gaba da bude kyautukan,wanda kusan kowanne box dake gurin tasan meye a ciki,amma yadda take nuna zumudinta zaka dauka karon farko data fara ganin kayan alatu na rayuwa irin haka.

Baki kadan akhnan din ta tabe,don sam bataji wata burgewa tattare da almaz ko daya a ranta ba. Eh ta karanci abinda mammina ta fada a kansa,da gaske bayason damuwa,ganinsa na farko ta tabbatar da hakan,ta sauke numfashi kadan tana sake tabe baki tare da tuna awannin baya da suka wuce.

Cikin qasaita dake cakude da fargaba ta yiwa kanta matsugunni saman daya daga cikin lafiyayyun kujerun da aka qawata gurin dasu. Wani irin ado da wani irin yanayi da tunda take ganawa da dukka mazajen da siltane yake mata ba'a taba tsara gurin irin haka ba.

Juyawa birra tayi da nufin fita daga gurin ta basu sarari,saidai a nutse da salon kalar umarnin data saba basu ta tsaida birran,sai birra din ta koma gefe daga bayanta ta tsaya tana sauke kanta a qasa.

Da dukka manyan kyawawan idanunta ta qure mutumin da kallo,wanda ke sanye da wata qawatacciyar alkyabba,bayan takalmin da aka yiwa wani irin qawataccen ado daya zame ya ajiyeshi a gefansa.

Kansa yana duqe a qasa,wanda bazai bata dama da ikon gane fuskarsa da kyau ba,saidai mamaki ya soma ratsata a hankali na rashin tantance bacci yake ko gyangadi?,don sam bataga alamun waya a hannunsa ba ballantana tayi tunanin waya yake dannawa.

Izzarta ta hanata magana,a haka suka shafe a qalla mintina biyar kafin ya motsa a hankali yana daga kansa gami da jinginar da bayansa a kujera.

Idanunsa ne ya soma sauka akan fuskarta,kaman yadda nata idanun suka sauka a kanshi,kallon kallo kuma ya sarqafe tsakaninsu na wasu sakanni kafin ta fara janye idanunta mamaki yana sauka a hankali saman zuciyarta.

"Shin me mammina ta gani tattare dashi data hangi dacewarsu?" Tambayar data soma yawo kenan saman kanta,wadda ta tilasta mata maida idanunta a karo na biyu kansa.

Still shima ita yake kallo,saidai a wannan karon yayi qoqarin sakin murmushin daya dan fidda kyansa ya kuma haska wani abu cikin idanunta. Sake zare dubanta tayi daga kansa tana rasa kowanne feelings a kansa. Soyayya dai dama tasan bata da lokacinta,bama kuma batunta akeyi ba,saidai wannan tarin baqincikin da bacin rai da tsananin tunzura da takeji a zuciyarta a duk sanda wani namiji ya tsaya a gabanta da sunan neman aure a yanzun bata jin ko guda daya.....

Me yasa dukka sharuddan data tsara gindaya masa?.....me yasa duk wani doka data tsara shimfida masa don yasan cewa bawai zai amsa sunan mijinta da gasken gaske ba suke sulalewa?.

"Na sani.....kada ki wani damu......zaki rayu yadda kikaga dama.....kaman yadda zan rayu yadda naga dama" Ya furta da wani izza ciki muryarsa da yadan ja hankalinta sosai ta sake daga kai tana dubansa.

Wannan karon tsakiyar idanunsa kawai ta kalla kai tsaye,sai takeji a ranta kamar ta taba ganinsa a wani guri kafin nan,kamar ta taba saninsa kafin yanzu,saidai dukka tunaninta ya gutsire a sanda yayi wani motsi nan take tarin hadiman data fahimci tare dashi suke suka fara shigowa gurin,shi kuma ya miqe tsam yana takawa da wani kamata irin yanayi data kasa tantance ne meye.....izza ce?.....ko nasa yanayinne a haka?.

Ko sanda zata dawo daga tunaninta tuni sun kammala jere takin kyaututukan data dinga binsu kawai da kallo ba tare da tasan ainihin meye da meye a ciki ba sun kuma juya suna take masa baya.

Bataji kalmar DACEWA ko BURGEWA tattare dashi ba.....saidai sam bata damu ba,don dama ba auren wadannan dukka zatayi ba.

"Gobe in sha Allahu zasu gabatar da sadakinsu" Mammina ta fadi tana tattara hankalinta akan akhnan bayan ta gaji da bude kyaututukan. Sanin dukka abinda ke ciki ne ya gajiyar da ita,tanaso kuma tayi saving lokacinta.

Sosai akhnan din ta tsuke idanunta tana duban mammina. Abu na farki daya fara zuwa mata kai shine SHIEKH HAISAM shine zai yanke adadin dukiyar da za'a bayar shi kuma ya basu ita?.

Idanunta ta dauke daga kan mammina,wani sabon bacin ran yana shimfida saman fuskarta. A hankali da wani irin coolness ta motsa labbanta.

"Me yasa saishi mammina?.....me yasa sultane zaiyimin haka?" Ta tambaya tana sake maido dubanta ga mammina.

"Wannan izzar.....wannan kimar,wannan dangantakar kwanann nan zata fara zama tarihi cikin agadez.....kwanan nan qyamata da ala wadai zata maye gurbin komai" Wannan shine abinda yake yawo saman zuciyar mammina din,saidai kuma a fili murmushi ta saki.

Har a ranta takejin matsalolin da take dasu guda biyu ne......tana kan hanyar kauda daya ta fuskanci dayar.......saboda haka dukkan wani uzuri da akhnan zata bayar tana daukarshi a matsayin wani bata lokaci ne kawai.

"Iya wannan lokaci,iya yanzu ne kawai yake da dama a kanki biftu,ki kwantar da hankalinki,daga wannan lokaci na miki alqawarin bazai sake shiga gonarki ba.....zan nesantashi da dukka iyakokinki,keda igiyar aure ma zata baki dukkan wata power?,kin manta wannan igiyar auren zata dawo da dukka wata kyakkyawar alaqa da dangantaka tsakaninki da sultane?,duk wani kusanci da kika rasa zaya dawo miki,meye abun damuwa?,ba abinda ya rage miki sai ki nutsu komai ya tafi daidai da hankulan masu nazari" Kai ta girgiza a hankali,hakan taketa qoqarin yi,amma sai takejin abun kamar yayi mata wahala.

"Niamy nakeso na koma mammina" Ta furta da wani irin sarewa,tana jin komai bayayi mata daidai.

Murmushin dake kwantar da zuciya ta saki tana maida hankalinta a kanta.

"Gaggawar me kike?,zaki zauna a shiryaki kaman kowacce amarya me gata,ko randa aka daura aure ne zaki iya wucewa niamy keda mijinki,wanda hakan shi zai sake bawa sultane nutsuwa da aminci a kanki......" Kai ta girgiza a hankali,a yanzu ba abinda take buqata irin ta samu 'yancinta,ta kuma koma rayuwarta kamar yadda take a baya,mara tarin matsaloli,rayuwa me cike da 'yanci da zartarswa akan dukkan abinda takeso.

"Sahel couture......ya miki nisan da bazai dawo hannunki kamar yadda yake a baya ba.....har gaban abada......zan tabbatar ya sake zamewa daga hannunki ta hannun amintacciyar taki" Ta furta qasan ranta tana sakin murmushi a bayyane,murmushin da akhnan ke kallonsa a matsayin wata hanya guda daya da mammina ke amfani da ita don samar mata da nutsuwa.

★A nutse suke takawa cikin farfajiyar kebantattun sassan haisam din da sultane ya mallaka masa,zuwa doguwar veranda da zata sadashi da qofar da zasu isa kai tsaye ga sassan nasa.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Yarima haisam tare da yarima maleek,wanda dukkaninsu suka narke cikin masarautar agadez da wani irin yanayi da bazai baka daman fahimtar sarautar dake jinin kowannensu ba. Saidai kuma kowannensun akwai wani irin kwantaccen kwarjini a tattare dashi,irin kwarjinin da jinin sarauta yake gaadarwa kowanne ahali nashi.

Dukkaninsu suna sanye ne da fararen tufafin da aka saqasu daga lallausar auduga me darajar gaske,saidai ba kowa bane zai fahimci hakan,saboda sassuqar sutura ce a jikin kowannensu. Maleek yana sanye da kurta pyjamas ne riga da wando,saman kansa kuwa Indonesian cap ce sassauqa data dace da suturar jikinsa,yayin da haisam ke sanye da jallabiyya fara sol me wani irin sulbi data dace da zatin tsahonsa da kyakkyawar fatarsa ta asalin qabilar oromia da suka sabawa ainihin kalarsu ta hanyar yin haske kadan daga ainihin skin color dinsu.

Komai na adon zaren jikin rigar fari ne qal,hakanan hiram din daya yiwa wani irin nadi na asalin samarin larabawa shima fari ne sol daya fidda kyan fuskarsa da dogon hancinsa dake zauna sosai saman fuskarsa ya sake bayyana tsananin kwarjinin idanunsa guda biyu. Half shoe ne a qafarsa shi dinma fari ne sol,lallausa kuma sassauqan da zai wahala ka fahimci yana yanayi da takalmin basarake.

Da azahar maleek ya sauka,ya kuma soma sanyawa an saukeshi a personal gidansa dake wajen masarautar,ya fara zuwa suka gana sannan suka tattauna akan yadda zai baqunceshi cikin masarautar,saboda tsarin shiga da fitar baqi daya sauya yanzu,dole ana buqatar bayanansa da kuma asalin yarensa wanda tuni haisam ya shirya kowanne bayani da zai bayar.
Chapter 43 · 0% Book details