Sashe 76
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Soli Center suka nufa, "oya fito" ya umurceta, cikin sanyinta ta fita tana tafia a hankali, duk ta raina kanta ganin irin mutanen da ke wurin, bata tunanin a garin Katsina akwai irin wuraren nan, ko don bata fita ne oho, tana bin ko ina da kallo, wurin ya hadu, tana ganin yanmata da samarin su, Har suka iso Shawarma&Pizza Spot, yayi ordering, Pizza da Shawarma, tace "Hamma ba yunwa kakeji ba, kwadayi kakeji" murmushin gefen baki kawai ya mata, yace "Muci Anan?" ta marairaice tace "No please" don ta raina kanta da kallon da 'yan gurin ke binta dashi, ya lura yace "Oya rik'e, i am not your Boy" ta amsa ledojin hannunshi, Rafeeq be da tausayi, suna tafia yace "do you need anything? Tace "No Thanks" suna tafia zasu koma cikin mota Sukaji ance "R-Lema" a tare suka juya, wata hadaddiyar budurwa suka gani Rafeeq ya zaro ido yace "Nanjeee? Omg" ai ko wacce aka kira da Nanjee ta rugo da gudu ta rungume Rafeeq shima rungume ta yayi suna jin dadin ganin juna,
Gaban Nasiba ya yanke ya fadi, meye wannan? Wacece wannan rungume da Hamma Rafeeq? Zuciyarta na bugu da sauri, duk ta dabarce ta shiga yanayi ganin Rafeeq da wata, hankalinta yayi matuk'a gun tashi, da sauri ta dauke ido ta matsa gefe don kirjinta na barazanar fitowa " OMG R-freaking Lema, What are you doing here?" murmushi kawai yakeyi ya kasa cewa komai don be san me zai cemata ba, mamaki ya cika ta, don ta san ba haka yake ba, ya cika surutu a da, amma yanzu sai basarwa yakeyi, tace "lookat you, what happened to you kamar ba R-leman da na sani ba" share maganan yayi yace "Yaushe kika dawo daga States? tace "wallahi last week nagama Masters na and all, ina Maalesh? Maalesh na Kano Wallahi, "I've missed you guys wallahi" "same here" "who is she R-Lema, your girl? Ya tsina fuska yayi Shaf ya mance da Seebi da ke tsaye kamar gunki, ba tare da ya kalleta ba yace "She's so not my type ke kin sani, shes my cousin" Seebi na jin haka, No reason taji hawaye na sauka daga fuskarta, Nan aka kira wayar Rafeeq ya matsa gefe yana receiving wayar, Nanjee ta matso kusa da Seebi, ta sa hannu tana share hawayen Fuskar Seebi, tace "Haba k'anwata why are you crying?" Seebi ta wayance tace "Aa ba kuka nakeyi ba" dont lie to me, i caught you crying, tell me you have feelings for R-lema huh? Tell me" daburcewa Seebi tayi tana girgiza kai, tace "No No is not what you are thinking, wani abu ya shigar min ido ne" Nanji tayi murmushi tace "bansan ya kuke da R-lema ba, but i can say you have feelings for him, You got Jealous when you saw us together, dont worry, i am not a threat, R-lema was my Bestfriend, and Maalesh was my crush lokacin muna Secondary School, so you dont have to worry about me, Kina sonsa, i can say that for sure" Nasiba ta rasa bakin magana, bata taba zaton wani ko wata zai fuskanci abunda takeji game da Rafeeq ba, tayi Alkawarin barin abun a ranta har mutuwarta, tace "Sorry Aunty is not what you are thinking" Nanji tayi murmushi tace "kanwata think about it, Rafeeq ya min yaro da na miki snatching" ta fada tana daria ita kuwa Seebi ta rasa yanda zatayi, Feeeq ya dawo yace "Oya lets get going Mami ta kira tana tambayarki" Nanji Babe bari mu tafi, sukayi shaking hands tareda exchanging Numbers, Seebi ta kallesu ta gefen Ido, Allah ya sauwake kuna diyan musulmai kuna taba juna kamar muharamai" ta murguda baki, fuu ta wuce gun mota don wani abu da takeji me kama da Kishi, Nanji na kallonta tayi daria ta wuce gun Saurayinta dama tare suke.
**********
Tun a mota ya ga yanayinta ya chanza, ba kamar da sukazo ba, amma yanzu ta hade rai sai fushi takeyi, ko me aka mata oho, yaso ya mata magana amma ya shareta har suka zo Gida, yana parking ta bude k'ofa zata fita yayi saurin rik'o hannun ta yace "Whats your Problem?" a dan masife tace "i dont have any" baki bude ya kalleta, ashe ta iya fushi, to me yayi zafi haka? Tab" ta wuce ta bar mai ledojinshi, ya daga kafada yace "matsalarki" ya wuce Dakinshi.
Da fushi ta shiga gidan tana ta mita cikin zuciyyarta, ba kowa a Parlorn K'asa ta hau sama daidai Dakin Saude taji ana magana k'asa k'asa, ta so wucewa don lab'e haramun ne, amma zuciyarta ya haneta, ta kasa kunne sosai ta gane Aunty Meema ce da Saude ke magana amma bata jin me suke cewa, a tsorace ta dan tura k'ofar a hankali, ta kutsa kai ciki ta labe tsaf takejin Su, jikinta ya fara rawa sakamakon abubuwan da kunnuwanta suke jiye mata:
"Wallahi Sis cikin kwanaki Shidda gidajen Boka shabiyar naje garuruwa daban daban, duk magana daya suke gaya min, wai ba abunda zasu iya miki" da Sauri Nasiba ta ciro wayarta ta danna record.
"Yanzu shikenan tawa ta sameni, yanzu ya zanyi da Alhaji? Gashi Aishatu ta dawo na san sai yanda tayi dashi, Matsalata Aneesa, ya zanyi da ita? Yanzu idan Alhaji ya fadi ya mutu bata da gadonsa, ya zanyi in sa ya bata k'addarorinsa, da ace ta hanyar Sunna muka haifi Aneesa da nasan tana da gadon Hafiz, gashi Hafiz be bar mata komai ba, kai ni tau na shiga uku" da sauri Nasiba ta toshe bakinta, tana fadin inalillahi wa ina ilaihir rajiun, yanda ta shigo haka ta fito a tsorace, jikinta na rawa ta ci karo sa Nene, Nene tace "meye haka jikin ki ke rawa kamar Mazari? Ya akayi? Ko gamo kikayi? Seebi ta ja hannuj Nene zuwa daki, ta rasa me zatace, Nene tace "wai meye? Zaki gaya min ko sai na je dakin Sauden naga me kike ma rawar jiki don naga da ga chan kike" da sauri tace "Aa nene, kar kije bari kiji" ta mata Playing abunda tayi recording, "tohhhh maganar kenan? Shi Hafiz din waye? Seebi tace " Yayan Uncle Zaid ne, ya rasu" toh Shine Uban Aneesar kenan, kuma Shegia ce, to ko sun sani? Anya bana tunanin sun sani, bari dai muga" Nene ta mik'e Seebi tayi saurin kamota, ina zaki? Haba Nene tada fitina zakiyi tsakaninsu? DonAllah kar kije, Nene ta lailayo ashar ta watsa ma Seebi, tace "Uban meyasa kikayi rakodin din, ni ban guri dalla" ta fita da wayar Seebi a hannu" Seebi ta daura hannu a kai "La i'llahailallah lahu take maimaitawa Hafiz Lema ne Baban Aneesa? Kuma ba ta hanyar Aure suka haifeta ba? Gashi Nene ta je fallasa asirinsu, anya tayi daidai kuwa da ba Nene wayar? Da sauri ta bi bayan Nene.
Nene bata tsaya ko ina ba sai dakin Aneesa,
Aneesa ta kalleta galala tace " Meye? Zaki shigo min daki? Nene tace "yi hakuri, DanAllah zuwa nayi ki latsa min inji wannan rakodin din" kamar ba zata karbi wayar ba ta karba, ta yi playing recoding din da tagani" K'arara muryar Mamarta taji tana wannan furucin ta zaro ido tace da Nene meye wannan? Ko Kinsan Babanki Shine Hafiz Lema? Ko kinsan ke Shegiya ce? Ihu Aneesa ta rusa, Na shiga Uku, ni Shegia? Ai ko a sittin ta diro daga kan gadin ta fita waje tana bige Seebi da ke kokarin riketa, wucewa tayi dakin Saude, Saude da Meema na kan Gadi, Aneesa ta danne kan Saude, duk ta chanza kamar wacce Aljannu suka shiga, tace "Saude Aminu ki gaya min da babanki, Ni diyar Hafiz Lema ce? Hafiz Lema ne Baba na? Dama ni shegia ce?"
_Bibilicious Biebee_
(donAllah kuyi hakuri, kunji ni shiru kwana biyu, hakan ya faru ne sakamakon Makaranta da muka koma, Karatu ya tasoni gaba wallahi ga matsalar wuta da muke fama da ita, kuyi min uzuri, nima so nake nagama wallahi, kunsan halin Karatu. DonAllah ku cigaba da Hakuri nagode..)
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg5⃣7⃣
Cikin k'ak'ari Saude tace "Aneesa ki dagani, You are hurting me, ki cika min Wuya" Meema tayi tayi ta k'waci Saude daga hannun Aneesa amma ta kasa, Nene a ranta tace "ku k'arata chan" Mami da Daddy suka shigo da sauri, Daddy yace "Meke faruwa nan ne?" ai Nene ta mik'a ma Daddy wayar Nasiba yayi Playing recording din nan, idan shi ya kada yayi jazir, ya Kalli Saude da Aneesa cike da Tsana, Daddy ya juya ya bar Dakin, Mami ce ta k'arasa gunsu tana ririk'e Aneesa, Aneesa Calm down, let your Mom go, please" a hankali Aneesa ta zame k'asa tana gurshek'en kuka me tsumma rai, Sauden ma Kukan takeyi, tace "Aneesa my child, ki saurareni" Aneesa tace "Saude ki daina min magana, ni ba diyarki bace, ashe ni shegia ce? Ba ta hanyar aure aka sameni ba? Kikayi min k'arya Babana ya rasu, Allah ya isa, Allah ya isa, na tsaneki Saude, i wish i have a different Mother" Mami tayi saurin taran Aneesa tace "Haba Aneesa, ki daina magana haka, Musulmi na kwarai shine wanda yake rungumar k'addarar sa da hannu bibiyu, me kyau ko mara kyau, DonAllah muje ki sha ruwa ki huta, kar ki sa abun a ranki". Fuu ta fita kamar zata tashi sama, Mami ta kalli Saude ta dan yi mata alamun tayi hakuri kafin ta wuce, Saude ta daura hannu a kai ta rusa ihu, Shikenan Asiri na Ya tonu, banda sauran Mutunci a idon kowa, Meema tawa ta k'are ya zanyi?" Meema ta hau lallashinta.
Gaban Nasiba ya yanke ya fadi, meye wannan? Wacece wannan rungume da Hamma Rafeeq? Zuciyarta na bugu da sauri, duk ta dabarce ta shiga yanayi ganin Rafeeq da wata, hankalinta yayi matuk'a gun tashi, da sauri ta dauke ido ta matsa gefe don kirjinta na barazanar fitowa " OMG R-freaking Lema, What are you doing here?" murmushi kawai yakeyi ya kasa cewa komai don be san me zai cemata ba, mamaki ya cika ta, don ta san ba haka yake ba, ya cika surutu a da, amma yanzu sai basarwa yakeyi, tace "lookat you, what happened to you kamar ba R-leman da na sani ba" share maganan yayi yace "Yaushe kika dawo daga States? tace "wallahi last week nagama Masters na and all, ina Maalesh? Maalesh na Kano Wallahi, "I've missed you guys wallahi" "same here" "who is she R-Lema, your girl? Ya tsina fuska yayi Shaf ya mance da Seebi da ke tsaye kamar gunki, ba tare da ya kalleta ba yace "She's so not my type ke kin sani, shes my cousin" Seebi na jin haka, No reason taji hawaye na sauka daga fuskarta, Nan aka kira wayar Rafeeq ya matsa gefe yana receiving wayar, Nanjee ta matso kusa da Seebi, ta sa hannu tana share hawayen Fuskar Seebi, tace "Haba k'anwata why are you crying?" Seebi ta wayance tace "Aa ba kuka nakeyi ba" dont lie to me, i caught you crying, tell me you have feelings for R-lema huh? Tell me" daburcewa Seebi tayi tana girgiza kai, tace "No No is not what you are thinking, wani abu ya shigar min ido ne" Nanji tayi murmushi tace "bansan ya kuke da R-lema ba, but i can say you have feelings for him, You got Jealous when you saw us together, dont worry, i am not a threat, R-lema was my Bestfriend, and Maalesh was my crush lokacin muna Secondary School, so you dont have to worry about me, Kina sonsa, i can say that for sure" Nasiba ta rasa bakin magana, bata taba zaton wani ko wata zai fuskanci abunda takeji game da Rafeeq ba, tayi Alkawarin barin abun a ranta har mutuwarta, tace "Sorry Aunty is not what you are thinking" Nanji tayi murmushi tace "kanwata think about it, Rafeeq ya min yaro da na miki snatching" ta fada tana daria ita kuwa Seebi ta rasa yanda zatayi, Feeeq ya dawo yace "Oya lets get going Mami ta kira tana tambayarki" Nanji Babe bari mu tafi, sukayi shaking hands tareda exchanging Numbers, Seebi ta kallesu ta gefen Ido, Allah ya sauwake kuna diyan musulmai kuna taba juna kamar muharamai" ta murguda baki, fuu ta wuce gun mota don wani abu da takeji me kama da Kishi, Nanji na kallonta tayi daria ta wuce gun Saurayinta dama tare suke.
**********
Tun a mota ya ga yanayinta ya chanza, ba kamar da sukazo ba, amma yanzu ta hade rai sai fushi takeyi, ko me aka mata oho, yaso ya mata magana amma ya shareta har suka zo Gida, yana parking ta bude k'ofa zata fita yayi saurin rik'o hannun ta yace "Whats your Problem?" a dan masife tace "i dont have any" baki bude ya kalleta, ashe ta iya fushi, to me yayi zafi haka? Tab" ta wuce ta bar mai ledojinshi, ya daga kafada yace "matsalarki" ya wuce Dakinshi.
Da fushi ta shiga gidan tana ta mita cikin zuciyyarta, ba kowa a Parlorn K'asa ta hau sama daidai Dakin Saude taji ana magana k'asa k'asa, ta so wucewa don lab'e haramun ne, amma zuciyarta ya haneta, ta kasa kunne sosai ta gane Aunty Meema ce da Saude ke magana amma bata jin me suke cewa, a tsorace ta dan tura k'ofar a hankali, ta kutsa kai ciki ta labe tsaf takejin Su, jikinta ya fara rawa sakamakon abubuwan da kunnuwanta suke jiye mata:
"Wallahi Sis cikin kwanaki Shidda gidajen Boka shabiyar naje garuruwa daban daban, duk magana daya suke gaya min, wai ba abunda zasu iya miki" da Sauri Nasiba ta ciro wayarta ta danna record.
"Yanzu shikenan tawa ta sameni, yanzu ya zanyi da Alhaji? Gashi Aishatu ta dawo na san sai yanda tayi dashi, Matsalata Aneesa, ya zanyi da ita? Yanzu idan Alhaji ya fadi ya mutu bata da gadonsa, ya zanyi in sa ya bata k'addarorinsa, da ace ta hanyar Sunna muka haifi Aneesa da nasan tana da gadon Hafiz, gashi Hafiz be bar mata komai ba, kai ni tau na shiga uku" da sauri Nasiba ta toshe bakinta, tana fadin inalillahi wa ina ilaihir rajiun, yanda ta shigo haka ta fito a tsorace, jikinta na rawa ta ci karo sa Nene, Nene tace "meye haka jikin ki ke rawa kamar Mazari? Ya akayi? Ko gamo kikayi? Seebi ta ja hannuj Nene zuwa daki, ta rasa me zatace, Nene tace "wai meye? Zaki gaya min ko sai na je dakin Sauden naga me kike ma rawar jiki don naga da ga chan kike" da sauri tace "Aa nene, kar kije bari kiji" ta mata Playing abunda tayi recording, "tohhhh maganar kenan? Shi Hafiz din waye? Seebi tace " Yayan Uncle Zaid ne, ya rasu" toh Shine Uban Aneesar kenan, kuma Shegia ce, to ko sun sani? Anya bana tunanin sun sani, bari dai muga" Nene ta mik'e Seebi tayi saurin kamota, ina zaki? Haba Nene tada fitina zakiyi tsakaninsu? DonAllah kar kije, Nene ta lailayo ashar ta watsa ma Seebi, tace "Uban meyasa kikayi rakodin din, ni ban guri dalla" ta fita da wayar Seebi a hannu" Seebi ta daura hannu a kai "La i'llahailallah lahu take maimaitawa Hafiz Lema ne Baban Aneesa? Kuma ba ta hanyar Aure suka haifeta ba? Gashi Nene ta je fallasa asirinsu, anya tayi daidai kuwa da ba Nene wayar? Da sauri ta bi bayan Nene.
Nene bata tsaya ko ina ba sai dakin Aneesa,
Aneesa ta kalleta galala tace " Meye? Zaki shigo min daki? Nene tace "yi hakuri, DanAllah zuwa nayi ki latsa min inji wannan rakodin din" kamar ba zata karbi wayar ba ta karba, ta yi playing recoding din da tagani" K'arara muryar Mamarta taji tana wannan furucin ta zaro ido tace da Nene meye wannan? Ko Kinsan Babanki Shine Hafiz Lema? Ko kinsan ke Shegiya ce? Ihu Aneesa ta rusa, Na shiga Uku, ni Shegia? Ai ko a sittin ta diro daga kan gadin ta fita waje tana bige Seebi da ke kokarin riketa, wucewa tayi dakin Saude, Saude da Meema na kan Gadi, Aneesa ta danne kan Saude, duk ta chanza kamar wacce Aljannu suka shiga, tace "Saude Aminu ki gaya min da babanki, Ni diyar Hafiz Lema ce? Hafiz Lema ne Baba na? Dama ni shegia ce?"
_Bibilicious Biebee_
(donAllah kuyi hakuri, kunji ni shiru kwana biyu, hakan ya faru ne sakamakon Makaranta da muka koma, Karatu ya tasoni gaba wallahi ga matsalar wuta da muke fama da ita, kuyi min uzuri, nima so nake nagama wallahi, kunsan halin Karatu. DonAllah ku cigaba da Hakuri nagode..)
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg5⃣7⃣
Cikin k'ak'ari Saude tace "Aneesa ki dagani, You are hurting me, ki cika min Wuya" Meema tayi tayi ta k'waci Saude daga hannun Aneesa amma ta kasa, Nene a ranta tace "ku k'arata chan" Mami da Daddy suka shigo da sauri, Daddy yace "Meke faruwa nan ne?" ai Nene ta mik'a ma Daddy wayar Nasiba yayi Playing recording din nan, idan shi ya kada yayi jazir, ya Kalli Saude da Aneesa cike da Tsana, Daddy ya juya ya bar Dakin, Mami ce ta k'arasa gunsu tana ririk'e Aneesa, Aneesa Calm down, let your Mom go, please" a hankali Aneesa ta zame k'asa tana gurshek'en kuka me tsumma rai, Sauden ma Kukan takeyi, tace "Aneesa my child, ki saurareni" Aneesa tace "Saude ki daina min magana, ni ba diyarki bace, ashe ni shegia ce? Ba ta hanyar aure aka sameni ba? Kikayi min k'arya Babana ya rasu, Allah ya isa, Allah ya isa, na tsaneki Saude, i wish i have a different Mother" Mami tayi saurin taran Aneesa tace "Haba Aneesa, ki daina magana haka, Musulmi na kwarai shine wanda yake rungumar k'addarar sa da hannu bibiyu, me kyau ko mara kyau, DonAllah muje ki sha ruwa ki huta, kar ki sa abun a ranki". Fuu ta fita kamar zata tashi sama, Mami ta kalli Saude ta dan yi mata alamun tayi hakuri kafin ta wuce, Saude ta daura hannu a kai ta rusa ihu, Shikenan Asiri na Ya tonu, banda sauran Mutunci a idon kowa, Meema tawa ta k'are ya zanyi?" Meema ta hau lallashinta.