Sashe 45
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bakin Zauren Gidan Maalesh ya doka Sallama "Assalam Alaikum" daga Ciki Nene ta Amsa, tare da cewa "Bismillan ku" Maalesh a gaba Rafeeq na bin shi a baya sai shan k'amshi yake tayi, kamar an ce dole sai ya shiga, ta Window Nene ta hango su, da sauri ta fito tana tafa hannayen ta, tana fadin "Ga Maalush ga Maalush" wani Murmushi Rafeeq ya saki ba tare da ya sani ba, suna hada ido da Nene yayi saurin daure fuska tare da dauke kai, ko meyasa be so taga Murmushin shi oho,a fili Nene tace "Chan ta Matse maka a matsatsen wandon ka"Maalesh ya fashe da daria, yace Nene ke dawa?" ya juya ya kalli Rafeeq da ya hade girar sama da ta kasa, Nene tace ni rabani da wannan Mara fara'a, Sannun ku da zuwa dai" ta bude baki tace "Seebi, fito da tabarma, ga Malush da Dunkum" Maalesh dai sai daria yake tayi, Hajjo ta fito, suka gaisa da Maalesh, tace "Rafeeq" Murmushi kadai ya mata, ya dauke kai, Nene sai ikon Allah take kallo, a ranta tace "Lallai yaro, kazo gidana ka dinga sha min kunu? To uban tauri ma yaci ubanshi" ta gyada kai ta shiga cikin kichin don ita kadai tasan me zata ma Rafeeq, Nasiba taji dadin zuwan su, ta dauko Tabarma ta fito kanta a k'asa ta shinfida musu, Maalesh ya fara zama sai Rafeeq, Maalesh ya bita da ido, ta dukursa ta gefen da Rafeeq ke Zaune tace "Ya Maalesh, Ina Wuni?" Maalesh yace "Lafiya lao Beautiful, ya Jikin Nene?" "Nene ta ji sauk'i Alhamdulilah" Kafin yace komi wayar shi ta fara ringing, ya dauka, Nasiba ta kalli Rafeeq, duk da ba ita yake kallo ba yasan shi take kallo, kamar ance ya kalleta, Idanuwan su suka hadu, ido cikin ido suke kallon Juna, a sanyayye Nasiba tace "Hamma na Ina wuni?" tsaki yayi ya dauke kansa, ko a jikinta ta tashi ta koma ciki, da sauri ya bi bayanta da ido, duk ya ji haushin da be amsa ta ba, tsaki yayi ya juya ga Maalesh, ashe tuni ya gama wayar, kallon juna sukayi, Nene ta katse musu hanzari, gaban Maalesh ta ajiye kwano, tace "Maalush dan Albarka, ga Zogale na kwandon ta maka kaci kai kadai kar ka ba kowa" ta karasa fadin haka tana kallon Rafeeq ta gefe ido, sosai ta ba Rafeeq daria, kallon Gefen shi yayi ya dinga Murmushin mara sauti a ranshi yace "Chill Tsohuwa, i cant eat this Sh*t" Maalesh yace "Kai Nenen mu kina ji dani fa, duk wannan ni kadai?" Ehmana dole nake ji da kai, wasu ko kallo basu isheni ba ai" Rafeeq ya kawar da kanshi gefe don yana gudun kar daria ta kubuce mai, wai don shi tsohuwar nan ke habaice habaice, lallai tana da damuwa, ta shekara tanayi ko a jikin shi, haka Maalesh ya zage sai cin Zogale yakeyi, da yake shi yana son abubuwan gargajia, Nene ta dauko kujerar tsakar gida ta zauna, don ta na ta Rok'on Allah sa Rafeeq ya nuna yana son ci ta k'are mai tanadi. Ga Mamakin ta har Maalush ya gama Rafeeq be dago kanshi ba, Rafeeq ya zunguro Maalesh, ya k'agara su tafi, Maalesh yace "Nene, bari mu tafi, gobe zan koma kano InshaAllah" Nene ta hau suburbuda mai Adduo'i kala kala, ta kwalawa Seebi kira tace kuzo kuyi bankwana Gobe zai tafi, ta fito ta raka su har Waje.
"Ya Maalesh a kano kake aiki? Yace aa, Service nakeyi, befi wata 2 in gama ba, sai in samu aiki sai in fito a sa bikin mu ko? Dariya tayi sosai tace "you are funny" yace "you think so ko?" ya kalli Rafeeq yace "Guy, tell her ba wasa nakeyi" tsaki Rafeeq ya buga tare da bude mota ya shiga, duk ba su damu ba don sun san saran Rafeeq na tsaki, sai da sukayi Sallama kafin ya Shiga mota suka wuce.
*MAFARKI*
"Assalam Alaikum Nasiba" Murmushi tayi tace "Sai yau Ko Yaruwa ta Rafee'ah?" "Afuwan Ukhti, Ya Hakuri da Hidima?" Nasiba tace "Toh mungode Allah" Rafee'ah ta fara magana cike da natsuwa "Da farko zan fara da gode miki, kin aiwatar da Aikin Farko da na saka ki, ina me miki albishir da kin riga da kin shiga Rayuwar Rafeeq, kinyi Namijin k'ok'ari, ina jinjina miki, abu na gaba shine, kinsan ance duk yanda mutum keso ya ci Nasara, ya kuma samu Albarka da Ribar Rayuwa, to ya bi Mahaifanshi, Musamman Mahaifiya, duk yanda kake son samun Nasarar Rayuwa, Idan baka bi Mahaifiyar ka ba, to ba zaka taba ganin daidai ba, duk me ka taba zai ruguje, kai ko da ka samu to bazaiyi Albarka ba" Nasiba ta jinjina kai tace "Haka ne" Rafee'ah ta cigaba "Toh abu na gaba shine, ki daidaita tsakanin Rafeeq da Mahaifiyar shi, indai kina so Rafeeq ya gama Makaranta wannan Zangon, to dole sai ya samu Albarkar Uwa, ba wannan ba dai, Duk da yana cikin Duhu, ya nemi gafarar Uwarsa, don ko yau ya fadi ya mutu sai Allah ya tambaye shi, don be nema samun Haske ba, ki Daidaita tsakanin su, Nasiba" Nasiba cikin Firgici tace "Ta ya zanyi haka? Kinfi kowa sannin kafiyar Rafeeq, ina zan nema Mahaifiyar ku? Ina zan ganta? Ta ina zan fara?" *Ke Alheri Ce* *Ke Alheri Ce* *Ke Alheri Ce Nasiba Muhammad* bat ta Rafee'ah ta bace, a firgice Nasiba ta farka daga Baccinta, "ki taimake ni Rafee'ah, atleast give me hint ya zanyi? duk ta bi ta jike da zufa, Minsharin Hajjo ya tunasar da ita Mafarki ne tayi, da sauri ta sauka kan Gado ta fita daga Dakin, ta dauro Alwala tazo ta kabbara Sallah, sai da tayi Raka'ah Shidda kafin ta dukufa da Adduoi, Alkah ya shige mata gaba, ya kawo mata komai a Sauk'ak'e.
*9:45am*
"Ki tsaya kiyi Kallaci Seebi" "Aa Nene zanyi a Makaranta, sauri nake kar bus ta tashi" "to Allah ya taimaka, a gaida miemo gayu" "Zataji sai na dawo" da sauri ta bar Gidan ta na ciro yar Tecno dinta a jakka ta latso number Usheey, "Usheey, kin isa National? Akwai Bus? Usheey tace " Eh Seebi, biyu sun tashi saura daya, kiyi sauri kar ta cika mu tafi" Seebi kamar tayi kuka, tace Gani nan na kusa bakin Titi, zan samu Napep" "Okay to sai kinzo" Ji take kamar tayi gudu, don in Last bus ta wuce bata san yadda zatayi ba.
Kamar a sama ta ga Motar Rafeeq a gabanta, bata san lokacin da ta sake Murmushin da ke kara ma fuskar ta kyau ba, ba watawata ta zagaya ta bude K'ofar ta shiga, k'amshin sa ya sa ta lumshe ido, ta bude baki zata gaishe shi, sai kuma ta tuna wani abu sai ta fasa, har ya ja motar shi shiru shiru bata gaida shi ba, ya saurara yana jiran ta gaishe shi amma bata ce ko 'a' ba, a ranshi yace ko lpy? Ta gefen ido ya kalleta sai hura hanci take yi, tana girgiza kaf'a tana kallon window, yau kuwa meye Haka? Guntun tsaki yayi yace ma kanshi "why do i even care?" ya dauki hanyar Makaranta, kusan minti 10 ba wanda yace da danuwan sa k'ala, Nasiba tayi wani shu'umin Murmushi, sun kusa Makaranta daidai Daji-dajin hanyar, Nasiba ta daddage ta buga tsaki da k'arfi, har cikin kunnen Rafeeq, da sauri ya dafe kunnensa da hannu daya, be yi magana ba, Tsut ta k'ara jan wani tsakin da ya fi na farkon k'ara, Haushi ya cika Rafeeq, kamar yayi me, be dai tanka ta ba, ya tsani Tsaki (kuji mun Rafeeq, wai ya tsani Tsaki) Nasiba na lura dashi, ta k'ara jan wani dogon tsaki daidai ta taka burkin Motar da Rafeeq yayi ji kake k'iiiiiiii, Nasiba ta tsorata sosai, ta kalleshi cike da tsoro, ba tare da ya kalleta ba yace "Get Out" Nasiba ta juya ta kalli dajin nan ga sanyi, gashi bata tunanin zata samu na Allahn da zai karasar da ita Makaranta, har zata bashi hak'uri, sai kuma ta fasa, bude k'ofar tayi ta fita, kamar jira yake ya ja motar shi ya wuce, ya barta nan tsaye, hawaye suka soma kwaranyowa, tayi dana sani, meyasa take son k'ureshi? Ita dake son fiddo shi daga yanayin da yake ciki, Meyasa ta k'osa, to gashi ya direta kan hanya, kuma ba zata iya takawa ba, don tafiar da saura, ta rasa yanda zatayi ta zauna gefen Titi ta na me rokan Allah ya kawo Bus ta tsaida su ko a tsaye sai ta tsaya.
"Mtswwww" tsakin da Rafeeq yayi kenan Karo Na 8 bayan ya dire Nasiba, meyasa zai ajiye ta bakin hanya? Yanzu if shes not careful Mota ya bugeta fa? Tsaki ya sake yi tare da kallon Mirror dinshi, chan ya hango ta zaune gefen Titi kamar Almajira, Tsaki ya sake yi yasa trafficator yayi U Turn ya koma Baya, horn ya mata da sauri ta dago ta sake Murmushi, a ranta tace "Ba zai iya bari na anan ba" kawar da kanta tayi gefe kamar bata ganshi ba, tsaki yayi da k'arfi, ya danna mata horn, ko dagowa batayi ba, takaici kamar me, wai shi yau ake ma haka? Allah Allah take kar yayi zuciya ya barta nan, amma wani zuciyar ta bata karfin guiwa, Matso da motar yayi kusa da ita ganin zai take mata k'afa yasa ta tashi ta hau kan dakali, da k'yar yace "Get In the Car" A takaice tace "No thanks" tsaki yayi yace " Nace ki shigo ko? So kike kiyi Missing Lectures?" a tsiwance ta murguda baki tace" What do you care idan nayi missing lectures? Werent you the one that dropped me here? Ba zan shiga ba" ta sake murguda bakinta, kamar Tv ya ke kallonta, mamakin ta yake, yaushe ta koyi Rashin kunya? Yaushe ta samu guts din mai magana haka? Yau Shi R-Lema ake ma haka? Lallai Yarinyar nan bata sanshi ba, be san me ta taka ba. Abun Mamaki be daddara ba yace "ki shigo motar nan" ta juya tace "ba fa zan shiga ba nace" kamar zaiyi kuka, besan lokacin da yace "Will you Please get in the Car now? Please".
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
"Ya Maalesh a kano kake aiki? Yace aa, Service nakeyi, befi wata 2 in gama ba, sai in samu aiki sai in fito a sa bikin mu ko? Dariya tayi sosai tace "you are funny" yace "you think so ko?" ya kalli Rafeeq yace "Guy, tell her ba wasa nakeyi" tsaki Rafeeq ya buga tare da bude mota ya shiga, duk ba su damu ba don sun san saran Rafeeq na tsaki, sai da sukayi Sallama kafin ya Shiga mota suka wuce.
*MAFARKI*
"Assalam Alaikum Nasiba" Murmushi tayi tace "Sai yau Ko Yaruwa ta Rafee'ah?" "Afuwan Ukhti, Ya Hakuri da Hidima?" Nasiba tace "Toh mungode Allah" Rafee'ah ta fara magana cike da natsuwa "Da farko zan fara da gode miki, kin aiwatar da Aikin Farko da na saka ki, ina me miki albishir da kin riga da kin shiga Rayuwar Rafeeq, kinyi Namijin k'ok'ari, ina jinjina miki, abu na gaba shine, kinsan ance duk yanda mutum keso ya ci Nasara, ya kuma samu Albarka da Ribar Rayuwa, to ya bi Mahaifanshi, Musamman Mahaifiya, duk yanda kake son samun Nasarar Rayuwa, Idan baka bi Mahaifiyar ka ba, to ba zaka taba ganin daidai ba, duk me ka taba zai ruguje, kai ko da ka samu to bazaiyi Albarka ba" Nasiba ta jinjina kai tace "Haka ne" Rafee'ah ta cigaba "Toh abu na gaba shine, ki daidaita tsakanin Rafeeq da Mahaifiyar shi, indai kina so Rafeeq ya gama Makaranta wannan Zangon, to dole sai ya samu Albarkar Uwa, ba wannan ba dai, Duk da yana cikin Duhu, ya nemi gafarar Uwarsa, don ko yau ya fadi ya mutu sai Allah ya tambaye shi, don be nema samun Haske ba, ki Daidaita tsakanin su, Nasiba" Nasiba cikin Firgici tace "Ta ya zanyi haka? Kinfi kowa sannin kafiyar Rafeeq, ina zan nema Mahaifiyar ku? Ina zan ganta? Ta ina zan fara?" *Ke Alheri Ce* *Ke Alheri Ce* *Ke Alheri Ce Nasiba Muhammad* bat ta Rafee'ah ta bace, a firgice Nasiba ta farka daga Baccinta, "ki taimake ni Rafee'ah, atleast give me hint ya zanyi? duk ta bi ta jike da zufa, Minsharin Hajjo ya tunasar da ita Mafarki ne tayi, da sauri ta sauka kan Gado ta fita daga Dakin, ta dauro Alwala tazo ta kabbara Sallah, sai da tayi Raka'ah Shidda kafin ta dukufa da Adduoi, Alkah ya shige mata gaba, ya kawo mata komai a Sauk'ak'e.
*9:45am*
"Ki tsaya kiyi Kallaci Seebi" "Aa Nene zanyi a Makaranta, sauri nake kar bus ta tashi" "to Allah ya taimaka, a gaida miemo gayu" "Zataji sai na dawo" da sauri ta bar Gidan ta na ciro yar Tecno dinta a jakka ta latso number Usheey, "Usheey, kin isa National? Akwai Bus? Usheey tace " Eh Seebi, biyu sun tashi saura daya, kiyi sauri kar ta cika mu tafi" Seebi kamar tayi kuka, tace Gani nan na kusa bakin Titi, zan samu Napep" "Okay to sai kinzo" Ji take kamar tayi gudu, don in Last bus ta wuce bata san yadda zatayi ba.
Kamar a sama ta ga Motar Rafeeq a gabanta, bata san lokacin da ta sake Murmushin da ke kara ma fuskar ta kyau ba, ba watawata ta zagaya ta bude K'ofar ta shiga, k'amshin sa ya sa ta lumshe ido, ta bude baki zata gaishe shi, sai kuma ta tuna wani abu sai ta fasa, har ya ja motar shi shiru shiru bata gaida shi ba, ya saurara yana jiran ta gaishe shi amma bata ce ko 'a' ba, a ranshi yace ko lpy? Ta gefen ido ya kalleta sai hura hanci take yi, tana girgiza kaf'a tana kallon window, yau kuwa meye Haka? Guntun tsaki yayi yace ma kanshi "why do i even care?" ya dauki hanyar Makaranta, kusan minti 10 ba wanda yace da danuwan sa k'ala, Nasiba tayi wani shu'umin Murmushi, sun kusa Makaranta daidai Daji-dajin hanyar, Nasiba ta daddage ta buga tsaki da k'arfi, har cikin kunnen Rafeeq, da sauri ya dafe kunnensa da hannu daya, be yi magana ba, Tsut ta k'ara jan wani tsakin da ya fi na farkon k'ara, Haushi ya cika Rafeeq, kamar yayi me, be dai tanka ta ba, ya tsani Tsaki (kuji mun Rafeeq, wai ya tsani Tsaki) Nasiba na lura dashi, ta k'ara jan wani dogon tsaki daidai ta taka burkin Motar da Rafeeq yayi ji kake k'iiiiiiii, Nasiba ta tsorata sosai, ta kalleshi cike da tsoro, ba tare da ya kalleta ba yace "Get Out" Nasiba ta juya ta kalli dajin nan ga sanyi, gashi bata tunanin zata samu na Allahn da zai karasar da ita Makaranta, har zata bashi hak'uri, sai kuma ta fasa, bude k'ofar tayi ta fita, kamar jira yake ya ja motar shi ya wuce, ya barta nan tsaye, hawaye suka soma kwaranyowa, tayi dana sani, meyasa take son k'ureshi? Ita dake son fiddo shi daga yanayin da yake ciki, Meyasa ta k'osa, to gashi ya direta kan hanya, kuma ba zata iya takawa ba, don tafiar da saura, ta rasa yanda zatayi ta zauna gefen Titi ta na me rokan Allah ya kawo Bus ta tsaida su ko a tsaye sai ta tsaya.
"Mtswwww" tsakin da Rafeeq yayi kenan Karo Na 8 bayan ya dire Nasiba, meyasa zai ajiye ta bakin hanya? Yanzu if shes not careful Mota ya bugeta fa? Tsaki ya sake yi tare da kallon Mirror dinshi, chan ya hango ta zaune gefen Titi kamar Almajira, Tsaki ya sake yi yasa trafficator yayi U Turn ya koma Baya, horn ya mata da sauri ta dago ta sake Murmushi, a ranta tace "Ba zai iya bari na anan ba" kawar da kanta tayi gefe kamar bata ganshi ba, tsaki yayi da k'arfi, ya danna mata horn, ko dagowa batayi ba, takaici kamar me, wai shi yau ake ma haka? Allah Allah take kar yayi zuciya ya barta nan, amma wani zuciyar ta bata karfin guiwa, Matso da motar yayi kusa da ita ganin zai take mata k'afa yasa ta tashi ta hau kan dakali, da k'yar yace "Get In the Car" A takaice tace "No thanks" tsaki yayi yace " Nace ki shigo ko? So kike kiyi Missing Lectures?" a tsiwance ta murguda baki tace" What do you care idan nayi missing lectures? Werent you the one that dropped me here? Ba zan shiga ba" ta sake murguda bakinta, kamar Tv ya ke kallonta, mamakin ta yake, yaushe ta koyi Rashin kunya? Yaushe ta samu guts din mai magana haka? Yau Shi R-Lema ake ma haka? Lallai Yarinyar nan bata sanshi ba, be san me ta taka ba. Abun Mamaki be daddara ba yace "ki shigo motar nan" ta juya tace "ba fa zan shiga ba nace" kamar zaiyi kuka, besan lokacin da yace "Will you Please get in the Car now? Please".
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)