Sashe 51
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Sannun ku da zuwa, kun sha hanya" Ya mutan Kaduna? Duk suna lafia, Nene ta gabatar musu da Danwaken da ta musu, tana basu labarin zaman kadaicin da tayi, Nasiba tace "Oho dai, ke kika jawo, sai da na ce miki ki taho mu tafi kaduna, ki ka k'i" tace "ke ni ban son mita ba gashi kin dawo ba? Ko wani abun ya kamani?" tace"kin daiyi kewa ta" Nene tace ko kadan, ban k'i ki koma ba, ko a habar zane na" Abbi dai na jin su sai dariya yake musu. Suna cikin cin danwake sai ga Maalesh da Rafeeq sunyi Sallama, da Sauri Nasiba ta kalli kofar zaure don jin muryar shi, sanin kanta ne tayi missing din Hamman ta, shima karaf idonshi kanta wani naunauyar Ajiyar Zuciya yayi, "Finally! shes back" Maalesh kuwa Murmushi ya bita dashi, Maalesh ya matso ya ba Abbi hannu, ko be sani ba yasan Baban Nasiba ne, Abbi ya bashi bayan hannu don yana cin danwake da hannun, Maalesh a ladabce ya gaida shi, Nene kuwa cewa takeyi Sannu da Zuwa Malush, Nasiba ta tashi da sauri tayi kamar zata shiga kichin, daidai yanda zaijita tace "He's my Dad, show some Respect" harara ya bi bayanta dashi, yayi dan guntun gajeren tsaki ya da zata ji shi ita kadai, ya dan matsa kusa da Abii da k'yar yace dashi "Barka da Yamma" Abii yace "Muna lafiya?" Ido Cikin Ido suka kalli juna, nan da nan yaga baban Nasiba ya mai kwarjini, haka kurum ya kasa shiru ya amsa da "Lafiya k'alau, anzo lafiya?" Abbi yace "Alhamdulilah" Nene tace "Ahh su Dunkum yau anyi Wayau" Hararar ta yayi ya dauke kai, Abbi na kallon shi, akwai wani Hikima tattare da yaron, akwai wani abun da ya hango game da yaron, daga gani Yaron dan Baiwa ne, yanda yake abubuwan shi, yana kallon yanda Maalesh ke bin Nasiba da ido, amma shi wannan kallo bata ishe shi ba, haka kurum yaji yana son sanin game da Yaron, bude baki yayi yace "Seebin Nene, zubo ma bak'i danwake" Maalesh Yace "Aa Baba mungode bana cin danwake" "Abokin ka fa?" da sauri Nene tace "Ya k'oshi da dai Fara ne, wannan ko ba a bashi ba zai dauka" duk suka bita da ido cikin rashin Fahimta, dauke kai Rafeeq yayi, Abii ya k'ara cewa "a zubo maka Danwaken?"Kamar jira Rafeeq yake yayi saurin hadiye wani miyau, tun da ya shigo gidan ya ke bin Danwaken plate din Abbi da ido, ya sha Mai, da kayan hadi, yana iya cewa Danwake ne best food dinshi, rabon shi da ci tun Mami na nan, kuma gani yake wannan tsohuwar da gayya take abubuwa don ya nuna ya na son ci ta samu damar Wulakanta shi, girgiza kai kawai yayi alamun aa, in har yace baya son cin danwaken nan to yayi k'arya, har ranshi ya biya, kuma besan dalilin da ya sa Nene keyin duk wani abun da yake son ci ba, shi da abinci be damai ba, tsaki kawai yayi, Duk abunda yakeyi a idon Abbii, ya kalli Maalesh yace "ya sunanka?" Maalesh cikin ladabi yace "Sunana Mahmud" Nene tace "laah gaka da suna me dadi amma ka yarda ake ce maka Malush" daria kawai yayi, Abii ya maida hankalin shi kan Rafeeq da kwatakwata ya dauke kai, yace "Kai fa ya Sunan ka?" Rafeeq yayi kamar be ji ba, shi kuma Abii be sake tambayan shi ba, Nasiba kuwa jikin ta ya fara rawa, bata so Rafeeq yayi banza da mahaifinta, bata so mahaifinta ya tsani Rafeeq kan halaiyar shi, da Rafeeq yaji shiru, ba a sake tambayan shi ba, ya dago kai a hankali ya kalli Abii, shima shi din yake kallo, gajeren tsaki yayi a hankali yace "Sunana Rafeeq" Abii ya jishi sarai, yace "Banji ba" kamar ba zai tanka ba, amma Abii ya mai girman da ba zai iya share shi ba, ya dan bude murya yace "Sunana Rafeeq". Abii ya jinjina kai, Rafeeq yayi Zumbur ya mik'e sabida yana jinshi wani iri gaban Abii, ganin haka Maalesh yace "to Nene mun gaida ku, bari mu wuce" tace "Toh Malush mungode, su Dunkum a gaida gida" tuni ya kusa Zaure, Abi ya bude murya yace "Rafeeq" k'yam ya tsaya ya kasa tafia, da k'yar ya juyo, Abii ya kalli Nasiba yace "Je ki zubo mishi Danwaken" a hankali Rafeew yace "Nak'oshi" Abbi yace "Ka tafi dashi anjima sai kaci" dama tuni Nasiba ta cika Umurnin Mahaifinta, ta kawo ma Rafeeq Coolern, dauke kai kawai yayi, ganin haka yasa ta ba Maalesh Coolern, Maalesh ya amsa yayi Godia, ya ja Rafeeq suka bar Gidan. Nene tace "Yau kam me ke damun Dunkum?" Abii ya zauna yace "Seebin Nene, Wanene wannan? Me kika sani game dashi?" Gaban Nasiba ya yanke ya fadi, Nene tace " ai wannan shin d'an Zaidu Bawan Allah da na jima ina baka labari, shi haka yake, wani Dunkum, ba fara'a, ba ilhamar fuska, yanda kasan takashin shanu, haka fuskar shi take murtuk'e kullum" Abbi ya jinjina kai, yace "Seebi, bakin ki akwai Magana, me kikasani game dashi? Ni na hango bak'in duhu tattare dashi" Nene tayi karaf tace "bawani bak'in duhu, Fadin Rai ne kawai ya mai yawa" Seebi tace "aa Nene, akwai wani Labarin da ban sanar dake game da Rafeeq ba, kunji kunji••••••••••. Tsaf ta kwashe labarin Gidan Lema ta basu, kamar yanda Baba Maigadi ya sanar da ita, kamar Yanda ta gaya ma Mami, Ta dai b'oye Mafarkin da take da Rafee'ah. Allahu Akbar inji Nene "Allah Sarki Dunkum, ashe ba yin ka bane, Lallai akwai B'oyayyen Alamari a tattare da Gidan nan, ni gaskia ina zargin matar Baban su" "aa Nene kar kiyi saurin zargi" "tace dole iz zargeta mana Mahamman, ita kadaice zata yi hakan" Abbii yace "kamar yanda shi da kawun shi suka taimaka miki lokacin da baki da lafiya, InshaAllah zan taimaka mishi da wasu Adduoi, kuma kafin in bar Katsina zanje gun Abokina Me *Arriyadh Islamic Medicine* a taimaka mishi da magunguna, har shi mahaifin shi, in ma akwai Kaidin Mace da yardar Ubangiji komai zai warware cikin iko na Allah" Nene cikin jin dadi tace "Yauwa dan Mallam Jikan Mallam, da ba ka shashanatar da kanka kan boko ba, da yanzu ni nasan kai babban Malami ne da ake tak'ama dashi a k'asa baki daya, yanzu ma na san zakayi k'okarin ka" Nasiba kuwa bata san kalar Farincikin da zata yi ba, hak'k'un ta yarda da Mahaifinta, kuma ta na murnan zai taimaka ma Rafeeq, sai dai su Rok'i Allah ya basu nasara.
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Assalam Alaikum, ina muku fatan Alheri, ina godia da yanda kuke biye dani a wannan labarin, ina me baku hak'urin rashin ji na da kukeyi kullum, hakan na faruwa ne saboda wasu 'yan dalillai, kuyi min uzuri don zan dinga tsallake kwana daya banyi typing ba, in kuma an samu yanda nikeso, zaku dinga jina kullum kullum, Nagode Allah bar zumunci.
Pg4⃣5⃣
Abbii da Nasiba gaban Mallamin *Arriyadh Islamic Medicine* bayan Abbii ya karanto ma Mallam Matsalolin Gidan Lema. Mallam Usman ya jinjina kai, yace "Alhamdulilah, wannan labari da kuka bani akwai 'kulalliya, ko ba sihiri zamu taimaka da adduoi, balle wannan ma daga ji an san akwai Sihiri, ta iya yiwuwa Shi Alhajin an sa shi ya mance Uwargidansa, tunda kunce be sake waiwayarta ba, sai kuma shi Rafeeq baa so ya gama Makaranta tunda ance shekarar sa ta biyu kenan yana maimaita aji, kuma ba wai don ba ya ganewa ba, kuma ba ya k'aunar uwarsa, alhalin duk yanda Uwarka take to akwai wannan So da K'auna dake tsakanin su, toh tabbas akwai Mak'arkashiya a ciki kuma InshaAllah zaa warware komai da yardan Ubangiji. Abu na farko;
Ina so su sa a ransu cewa duk abunda ya samu bawa to da yarda da ikon Allah ya same shi. Su kasance masu Adduoi da Tauhid, Zaa musu magani duka, Shi Alhaji zaa bashi maganin da zai taimake shi ya tuno abubuwan da suka faru a baya, shi kuma Rafeeq zaa bashi Maganin da zai sa mai dangana a ranshi, yanda zai yafe ma Mahaifiyar shi, wani Jarka Mallan ya dauko, yace "Wannan Ruwan Karatun Kurani mai girma da Addu'oin Shifa, Lallai Rafeeq da Habib su maida shi ruwan Sha din su, in so samu ne ko abinci a dinga dafa musu da shi, shi zai tsare su daga Sharrin mai Sharri" ya ciro wani robar swan, yace wannan kuma Man itattuwa ne, Man Habbatussauda, Man Ridi, Man Hulba, Man Zaitun, Man tafarnuwa, Garin Luban, da Adduoi kama daga AmanarRasulu, Ayatul kursiyu, da zikirin Safe da Maraice, Wannan na Rafeeq ne, shi ne zai saka mishi Salama da dangana a rai har yaji cewa yana son sanin abun da ya faru a wannan bak'in rana. Sai Kuma Saukar Alkurani da zaa musu sai ayi tawassali da Karatun sai a rok'i Allah ya baiyanar da Gaskia. Amma dole sai sun yarda da hakan, maana sai sunyi Imani da Allah shi zai firda su daga Abun da ya shige musu duhu".
Abbii yayi Godia Sosai, yace "InshaAllah zaayi yanda kace Mallam Usman, Nasiba kina ji ko?" Nasiba da zufa ya gama keto mata, tana tunanin yanda zaa sa Rafeeq shan wadannan Magungunan. Da sauri ta gyada kai, tace "Eh Abii, zaayi yanda yace" yace to Madallah. Magungunan Dubu Sha biyar ne, amma saboda Sanayyar da ke tsakanin Mallam da Abii yace su bada dubu 10, kafin Abii yace wani abu Nasiba ta zaro kudin da Mami ta bata ta mika ma Mallam, Abii ya bita da ido, ta shaida mishi "ai kudin da Mamian Ayman ta bata ne" haka suka dawo gida cikin Keke Napep.
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Assalam Alaikum, ina muku fatan Alheri, ina godia da yanda kuke biye dani a wannan labarin, ina me baku hak'urin rashin ji na da kukeyi kullum, hakan na faruwa ne saboda wasu 'yan dalillai, kuyi min uzuri don zan dinga tsallake kwana daya banyi typing ba, in kuma an samu yanda nikeso, zaku dinga jina kullum kullum, Nagode Allah bar zumunci.
Pg4⃣5⃣
Abbii da Nasiba gaban Mallamin *Arriyadh Islamic Medicine* bayan Abbii ya karanto ma Mallam Matsalolin Gidan Lema. Mallam Usman ya jinjina kai, yace "Alhamdulilah, wannan labari da kuka bani akwai 'kulalliya, ko ba sihiri zamu taimaka da adduoi, balle wannan ma daga ji an san akwai Sihiri, ta iya yiwuwa Shi Alhajin an sa shi ya mance Uwargidansa, tunda kunce be sake waiwayarta ba, sai kuma shi Rafeeq baa so ya gama Makaranta tunda ance shekarar sa ta biyu kenan yana maimaita aji, kuma ba wai don ba ya ganewa ba, kuma ba ya k'aunar uwarsa, alhalin duk yanda Uwarka take to akwai wannan So da K'auna dake tsakanin su, toh tabbas akwai Mak'arkashiya a ciki kuma InshaAllah zaa warware komai da yardan Ubangiji. Abu na farko;
Ina so su sa a ransu cewa duk abunda ya samu bawa to da yarda da ikon Allah ya same shi. Su kasance masu Adduoi da Tauhid, Zaa musu magani duka, Shi Alhaji zaa bashi maganin da zai taimake shi ya tuno abubuwan da suka faru a baya, shi kuma Rafeeq zaa bashi Maganin da zai sa mai dangana a ranshi, yanda zai yafe ma Mahaifiyar shi, wani Jarka Mallan ya dauko, yace "Wannan Ruwan Karatun Kurani mai girma da Addu'oin Shifa, Lallai Rafeeq da Habib su maida shi ruwan Sha din su, in so samu ne ko abinci a dinga dafa musu da shi, shi zai tsare su daga Sharrin mai Sharri" ya ciro wani robar swan, yace wannan kuma Man itattuwa ne, Man Habbatussauda, Man Ridi, Man Hulba, Man Zaitun, Man tafarnuwa, Garin Luban, da Adduoi kama daga AmanarRasulu, Ayatul kursiyu, da zikirin Safe da Maraice, Wannan na Rafeeq ne, shi ne zai saka mishi Salama da dangana a rai har yaji cewa yana son sanin abun da ya faru a wannan bak'in rana. Sai Kuma Saukar Alkurani da zaa musu sai ayi tawassali da Karatun sai a rok'i Allah ya baiyanar da Gaskia. Amma dole sai sun yarda da hakan, maana sai sunyi Imani da Allah shi zai firda su daga Abun da ya shige musu duhu".
Abbii yayi Godia Sosai, yace "InshaAllah zaayi yanda kace Mallam Usman, Nasiba kina ji ko?" Nasiba da zufa ya gama keto mata, tana tunanin yanda zaa sa Rafeeq shan wadannan Magungunan. Da sauri ta gyada kai, tace "Eh Abii, zaayi yanda yace" yace to Madallah. Magungunan Dubu Sha biyar ne, amma saboda Sanayyar da ke tsakanin Mallam da Abii yace su bada dubu 10, kafin Abii yace wani abu Nasiba ta zaro kudin da Mami ta bata ta mika ma Mallam, Abii ya bita da ido, ta shaida mishi "ai kudin da Mamian Ayman ta bata ne" haka suka dawo gida cikin Keke Napep.