Sashe 43
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana shiga Dakin shi ya ga Rafeeq kwance kan Gado, ya bubbuga mai k'afa, kamar ba zai tashi ba, ya mike sukayi side hug, Maalesh cike da doki yace "I met her, Wallahi naganta yau" da k'yar Rafeeq yace "Who?" Maalesh yace "The love of my life, Seebi, Uncle Zaid ya aike ni Gidan su yanzu in kai ma Nene sak'o" a dan tsorace Rafeeq ya kalleshi, kamar zaice wani abu sai ya fasa, be damu da Rashin Ansashi da Rafeeq yayi ba, Maalesh ya cigaba "Shes beautiful, ai kasanta, ta hadu ko? Zamu dace? Haka ya ishe Rafeeq da maganar Nasiba, yace " Guy do you think she'll like me? Wallahi ina sonta, kawai ganinta nayi gefe na kamar an jefo ta, ina ganin ta naji She's the one, wannan shi ake kira "LOVE AT FIRST SIGHT" cikin kufula da daga murya Rafeeq yace "Will you Shut the f**k up?
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg4⃣0⃣
A tsorace ta dan kalleshi, ko bi ta kanta beyi ba ya hau titi kanshi a tsaye, Maimakon suyi hanyar Asibiti, sai bani tayi ya dauki hanyar *Sally's Cuisine* ba tace da shi komai ba har ya iso yayi parking, fita yayi ya shiga, nan ta samu damar amsa Wayar Usheey da tun da suja aje su take ta faman kiran ta, "Hello Seebi ina zai kaiki?" tayi daria tace "Asibiti" "haba har hankalin mu ya kwanta" tana ganin ya fito tayi saurin katse wayar, Hannun shu dauke da ledoji 4 ya aje mata 3, dayan kuma ya aje a seat din baya yaja mota sukayi Asibiti.
Ko da suka isa Asibtin, har ta bude murfin mota zata fita, Zuciyar ta ta bata shawara, ko bazai amsa ba, ki masa godiar dawainiyar da yake tayi daku, Abinci lunch da dinner baya fashin kawo muku, ga kai ki makaranta da dawo dake duk da ba kullum ba.
Ta juyo ta gyara zama yanda tana fuskantar sa tace *"Hamma Rafeeq, Yau Dr ke sa ran Sallamar mu, mun gode kwarai da dawainiyar da kakeyi da mu, Allah ya biya ka, Allah ya saka da Alheri ya, Allah ya ji kan Magabata, Albarkaci Rayuwar ka, Allah ya kuma Saka maka duk Zalincin da aka taba maka, wanda ba za ka iya yafe su ba"* tana kaiwa nan ta fice daga motar, bata tsaya sauraren abun da zai ce ba, Yanda kuka san Hoto, haka Rafeeq ke zaune a gun, ko yatsar shi ya kasa dagawa, be san lokacin da ya furta *"Ameen*" ba.
Haka kurum yaji dadin Adduointa, Shi be san meyasa ba, amma yana jinta a jikin shi, kawai yaji ya bata babban matsayi a ran shi, jinta kamar FEE'AH.
Da k'yar ya kunna mota, saboda jikin sa ya mace gabaki daya, ji yayi ya kasa tafiya, guntun tsaki ya sake ya duba Aljihun motar shi ya ciro paper da biro, rubutu yayi sannan ya fita ya shiga Asibitin, daidai Dakin ya chokara a jikin kofar yadda in an bude zaa gani, yayi tafiayar sa.
Seebi na idar da Sallah ta dauki Abincinta, Su Nene har sun gama da Abincin da Nasiba ta shigo dashi,nan zaman jiran Sallama sukeyi, Nasiba tace "bari inje in ga Dr, k'ila ma ya mance da yace yau zai sallame mu" Nene tace "E danAllah, na k'agara inga nayi juyi kan Gadon K'arfe na" sukayi daria duka.
Tana murda kofa wata kaaramar Takarda ta fado, duk'awa tayi ta dauka, ta na budewa tabi rubutun da ido, Murmushi tayi a hankali tace "R-Lema" a nutse ta fita daga dakin ta fara karantawa ga abun da yace
_"Ameen to your Duas. Idan an sallame ku, ga number na ki min text you DONT have to Call just TEXT"_.
Seebi tayi murmushi ta sake karantawa, tace *"R-LEMA kenan Allah ka bani ikon taimaka ma beautiful soul dinnan"*. Tasa kai ta wuce office din Dr. A hanya suka hadu da Dr da Nurse Sai suka juya suka koma dakin.
Nurse ta gwada Bp da Temperaturen Nene, komai daidai, Likita yace "Mama, kin ji sauki sosai, zan sallame ku, Amma donAllah ki rage cin Jan Nama" Nene ta bishi da kallon kai gaja, tace *"yaro wani Nama ne Ja?"* yace "Naman Sa, ko na Awaki" Nene ta tuntsire da daria, tace "Su balangu da tsiren da nake ci kake son hanani ci ko? Yace " Mama saboda Lafiyar ki ne, bawai ina son hanaki bane" ta tabe baki tace "toh dai bari kaji Ubana *Mamman* Shanun shi 31, duk bayan wata ake kashe mana daya, ba saidawa ake ba ci mukeyi, kuma ban taba jin ance wani naman Shanu yasa shi ciwo ko wani abun Allah sauwak'a ba, toh nidai _Aminene Mamman_ da bakin ciki ya kashe ni gwara Dadi ya kasheni Ehe" Nasiba tayi saurin cewa "I'm so sorry, She's always like this, InshaAllah she'll regulte it" Dr yace "Dont worry i have someone exactly like her at home" Nene ta cika tayi fam tace "Oho dai, Sai ka sallame mu yau, Ke kuma ni zaki chanzawa ko? To in ma zagina kukai da Ubanki Mahammadu kuke" Dr ya fashe da Daria yace "yi hakuri Mama ga takardar sallamar ki" yafi maka don yau ko baka sallameni ba gida zan kwan" Nasiba ta girgiza kai cike da takaici, Hajjo kuwa sai daria take tayi.
Dr na fita Nene tace " _kinga latso min Zaidu bawan Allah a waya, ba gardama Seebi tayi yadda nene tace, Yana ganin kiranta ya yanke ya sake k'ira
Zaid yayi Murna kwarai da jin Sallamar su Nene, kuma ya bata shawaran bin yanda Likita yace, jin shi kawai Nene tayi don ba ta da Mak'iyi kamar me son rabata da Nama, nan dai ta hau yi mishi Godia da Adduoi, Ya tsaidata ta hanyar cewa Haba Nene, Kun wuce nan, babu godia a tsakanin mu. Sukayi Sallama. Bayan Seebi ta karba wayar ne yace mata zai turo a maida su gida, tace ai "Hamma Rafeeq yace in gaya mai idan an sallame mu" da Mamaki Zaid yace "Rafeeq dai?" tace "eh shi" shi da kanshi yace haka?" tace "eh" "Rafeeq yana zuwa ne?" tace "Duk da ba shigowa yake ba, amma yana kawo mana Abinci Rana da Dare, sometimes ya na aje ni makaranta" Allahu Akbar zo ku ga jin dadi gun Zaid, Ashe Rafeeq na da sauran Mutunci da tausayi a tattare dashi? Be taba ganin Rafeeq ya damu da lamuran wasu ba kamar su Seebi lallai akwai Improvement, yace da Seebi "to sai kun koma gida mayi waya" sukayi Sallama. Duk zaton Nasiba da Nene Zaid ne ya sa Rafeeq dawainiya dasu, duk abunda yake yi saboda Zaid ne, nan suka gane cewa ashe Rafeeq ne ya sa Kanshi, ba kowa ba. Nan Nasiba ta k'ara samun wani k'warin guiwar Aiwatar da Kuddirinta.
Seebi ta kwafi numbern da Rafeeq ya bata, ta masa text din as he demanded. Ga abun da tace;
_"Assalamu alaikum Hamma Rafeeq anyi discharging din mu, mun shirya, we are good to go"_
Yana wanka yaji wayarsa alamar shigowar sak'o, bayan yayi Sallah, ne ya daga wayar ya ga message daga new number, ya bude ya karanta, dan guntun tsaki ya ja (Ikon Allah! sak kace bashi yace ta mai ba).
Key kawai ya dauka ya fice daga gidan sai Asibiti, yana isa ya mata text "Ku fito".
Seebi na jin shigowar text ta duba taga Shine, ba su wani dau lokaci ba suka fito harabar Asibitin da kayan su. Inda yake aje Motar shi sukayi, ta na zuwa ta iske Booth a bude, be fito ba haka Seebi ta shiga saka a kayan boot sai da ta gama, sannan ta bude gaba ta shiga ta zauna su nene kuma sun shiga baya.
Sai da suka bar Asibitin, da kyar yace " Ya Jikin?" Nene ta murmusa a ranta tace Uban Kasaita, a fili kuma tace "Alhamdulilah, na watsake" kamar ba zai ce wani abu ba yace "Sannu Fah" tace "yauwa" a hankali tace kamar dangin Maguzawa wai sannu" Hajjo da Nasiba kadai suka jita, Murmushi kawai sukayi, tun daga nan ba wamda ya sake magana har sai da suka iso gida, ya juya ya dan kalli Hajjo yace "Hajjo Mom tace ki k'ara Sati daya sai ki koma gida" tayi murmushi tace "ba damuwa"
Tare da taimakon Hajjo suka shiga da kayan su ciki, sai da ya tabbatar sun gama kwashe wa ya danna horn, ta lek'o ta window, ya mik'a mata manyan ledojin Abinci, yaja motar sa yayi gidan su Maalesh.
*England*
Zaid ne kwance kan tafkeken Gadonsa yana waya da Mami, inda aka bashi Ayman ta dinga mai gwaran cin ta, har sukayi Sallama sannan ya kira Nasiba,
Suk gaisa ya tambayeta ya jikin Nene ta amsa masa da sauk'i.
Suka danyi hira sannan ya gaisa da Nenen itama ya musu Sallama.
Nan ya hau tunanin wanda zai sa ya musu Grocery shopping, don ya tabbatar suna da Buk'ata, baya son takura wa Rafeeq, Saboda abunda ya fahinta, Rafeeq has done more than Enough, kuma baya so ya k'ure shi .
Maalaesh ya fado ransa, Take ya kira wayansa, Ringing biyu ya dauka "Hello Mahmud" nan take ya gane Uncle Zaid ne, don shi yasan shi kadai ke kiran shi da sunan shi na Asali, "UncleZee ina wuni" suka gaisa, yace "Mahmud ina so donAllah ka min Shopping na kayan Abinci, da kayan buk'ata na Gida, ina so ka kai wani Gida na nan ku sa da gidanku na Layout(Gidansu Rafeeq yake nufi) Nan ya mishi kwatancen gidan. Malaesh yace "Angama, anything for you uncle Z" barin je yanzu ma, "barin maka transferring kudin" da sauri yace "Noo akwai kudi hanuna Uncle Z" "dont be Silly Son, i'm sending now" Murmushi Maalesh yayi yace "Nagode" suka yi Sallama, Nan take Zaid ya mai Transfer din 100k.
2:47pm
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg4⃣0⃣
A tsorace ta dan kalleshi, ko bi ta kanta beyi ba ya hau titi kanshi a tsaye, Maimakon suyi hanyar Asibiti, sai bani tayi ya dauki hanyar *Sally's Cuisine* ba tace da shi komai ba har ya iso yayi parking, fita yayi ya shiga, nan ta samu damar amsa Wayar Usheey da tun da suja aje su take ta faman kiran ta, "Hello Seebi ina zai kaiki?" tayi daria tace "Asibiti" "haba har hankalin mu ya kwanta" tana ganin ya fito tayi saurin katse wayar, Hannun shu dauke da ledoji 4 ya aje mata 3, dayan kuma ya aje a seat din baya yaja mota sukayi Asibiti.
Ko da suka isa Asibtin, har ta bude murfin mota zata fita, Zuciyar ta ta bata shawara, ko bazai amsa ba, ki masa godiar dawainiyar da yake tayi daku, Abinci lunch da dinner baya fashin kawo muku, ga kai ki makaranta da dawo dake duk da ba kullum ba.
Ta juyo ta gyara zama yanda tana fuskantar sa tace *"Hamma Rafeeq, Yau Dr ke sa ran Sallamar mu, mun gode kwarai da dawainiyar da kakeyi da mu, Allah ya biya ka, Allah ya saka da Alheri ya, Allah ya ji kan Magabata, Albarkaci Rayuwar ka, Allah ya kuma Saka maka duk Zalincin da aka taba maka, wanda ba za ka iya yafe su ba"* tana kaiwa nan ta fice daga motar, bata tsaya sauraren abun da zai ce ba, Yanda kuka san Hoto, haka Rafeeq ke zaune a gun, ko yatsar shi ya kasa dagawa, be san lokacin da ya furta *"Ameen*" ba.
Haka kurum yaji dadin Adduointa, Shi be san meyasa ba, amma yana jinta a jikin shi, kawai yaji ya bata babban matsayi a ran shi, jinta kamar FEE'AH.
Da k'yar ya kunna mota, saboda jikin sa ya mace gabaki daya, ji yayi ya kasa tafiya, guntun tsaki ya sake ya duba Aljihun motar shi ya ciro paper da biro, rubutu yayi sannan ya fita ya shiga Asibitin, daidai Dakin ya chokara a jikin kofar yadda in an bude zaa gani, yayi tafiayar sa.
Seebi na idar da Sallah ta dauki Abincinta, Su Nene har sun gama da Abincin da Nasiba ta shigo dashi,nan zaman jiran Sallama sukeyi, Nasiba tace "bari inje in ga Dr, k'ila ma ya mance da yace yau zai sallame mu" Nene tace "E danAllah, na k'agara inga nayi juyi kan Gadon K'arfe na" sukayi daria duka.
Tana murda kofa wata kaaramar Takarda ta fado, duk'awa tayi ta dauka, ta na budewa tabi rubutun da ido, Murmushi tayi a hankali tace "R-Lema" a nutse ta fita daga dakin ta fara karantawa ga abun da yace
_"Ameen to your Duas. Idan an sallame ku, ga number na ki min text you DONT have to Call just TEXT"_.
Seebi tayi murmushi ta sake karantawa, tace *"R-LEMA kenan Allah ka bani ikon taimaka ma beautiful soul dinnan"*. Tasa kai ta wuce office din Dr. A hanya suka hadu da Dr da Nurse Sai suka juya suka koma dakin.
Nurse ta gwada Bp da Temperaturen Nene, komai daidai, Likita yace "Mama, kin ji sauki sosai, zan sallame ku, Amma donAllah ki rage cin Jan Nama" Nene ta bishi da kallon kai gaja, tace *"yaro wani Nama ne Ja?"* yace "Naman Sa, ko na Awaki" Nene ta tuntsire da daria, tace "Su balangu da tsiren da nake ci kake son hanani ci ko? Yace " Mama saboda Lafiyar ki ne, bawai ina son hanaki bane" ta tabe baki tace "toh dai bari kaji Ubana *Mamman* Shanun shi 31, duk bayan wata ake kashe mana daya, ba saidawa ake ba ci mukeyi, kuma ban taba jin ance wani naman Shanu yasa shi ciwo ko wani abun Allah sauwak'a ba, toh nidai _Aminene Mamman_ da bakin ciki ya kashe ni gwara Dadi ya kasheni Ehe" Nasiba tayi saurin cewa "I'm so sorry, She's always like this, InshaAllah she'll regulte it" Dr yace "Dont worry i have someone exactly like her at home" Nene ta cika tayi fam tace "Oho dai, Sai ka sallame mu yau, Ke kuma ni zaki chanzawa ko? To in ma zagina kukai da Ubanki Mahammadu kuke" Dr ya fashe da Daria yace "yi hakuri Mama ga takardar sallamar ki" yafi maka don yau ko baka sallameni ba gida zan kwan" Nasiba ta girgiza kai cike da takaici, Hajjo kuwa sai daria take tayi.
Dr na fita Nene tace " _kinga latso min Zaidu bawan Allah a waya, ba gardama Seebi tayi yadda nene tace, Yana ganin kiranta ya yanke ya sake k'ira
Zaid yayi Murna kwarai da jin Sallamar su Nene, kuma ya bata shawaran bin yanda Likita yace, jin shi kawai Nene tayi don ba ta da Mak'iyi kamar me son rabata da Nama, nan dai ta hau yi mishi Godia da Adduoi, Ya tsaidata ta hanyar cewa Haba Nene, Kun wuce nan, babu godia a tsakanin mu. Sukayi Sallama. Bayan Seebi ta karba wayar ne yace mata zai turo a maida su gida, tace ai "Hamma Rafeeq yace in gaya mai idan an sallame mu" da Mamaki Zaid yace "Rafeeq dai?" tace "eh shi" shi da kanshi yace haka?" tace "eh" "Rafeeq yana zuwa ne?" tace "Duk da ba shigowa yake ba, amma yana kawo mana Abinci Rana da Dare, sometimes ya na aje ni makaranta" Allahu Akbar zo ku ga jin dadi gun Zaid, Ashe Rafeeq na da sauran Mutunci da tausayi a tattare dashi? Be taba ganin Rafeeq ya damu da lamuran wasu ba kamar su Seebi lallai akwai Improvement, yace da Seebi "to sai kun koma gida mayi waya" sukayi Sallama. Duk zaton Nasiba da Nene Zaid ne ya sa Rafeeq dawainiya dasu, duk abunda yake yi saboda Zaid ne, nan suka gane cewa ashe Rafeeq ne ya sa Kanshi, ba kowa ba. Nan Nasiba ta k'ara samun wani k'warin guiwar Aiwatar da Kuddirinta.
Seebi ta kwafi numbern da Rafeeq ya bata, ta masa text din as he demanded. Ga abun da tace;
_"Assalamu alaikum Hamma Rafeeq anyi discharging din mu, mun shirya, we are good to go"_
Yana wanka yaji wayarsa alamar shigowar sak'o, bayan yayi Sallah, ne ya daga wayar ya ga message daga new number, ya bude ya karanta, dan guntun tsaki ya ja (Ikon Allah! sak kace bashi yace ta mai ba).
Key kawai ya dauka ya fice daga gidan sai Asibiti, yana isa ya mata text "Ku fito".
Seebi na jin shigowar text ta duba taga Shine, ba su wani dau lokaci ba suka fito harabar Asibitin da kayan su. Inda yake aje Motar shi sukayi, ta na zuwa ta iske Booth a bude, be fito ba haka Seebi ta shiga saka a kayan boot sai da ta gama, sannan ta bude gaba ta shiga ta zauna su nene kuma sun shiga baya.
Sai da suka bar Asibitin, da kyar yace " Ya Jikin?" Nene ta murmusa a ranta tace Uban Kasaita, a fili kuma tace "Alhamdulilah, na watsake" kamar ba zai ce wani abu ba yace "Sannu Fah" tace "yauwa" a hankali tace kamar dangin Maguzawa wai sannu" Hajjo da Nasiba kadai suka jita, Murmushi kawai sukayi, tun daga nan ba wamda ya sake magana har sai da suka iso gida, ya juya ya dan kalli Hajjo yace "Hajjo Mom tace ki k'ara Sati daya sai ki koma gida" tayi murmushi tace "ba damuwa"
Tare da taimakon Hajjo suka shiga da kayan su ciki, sai da ya tabbatar sun gama kwashe wa ya danna horn, ta lek'o ta window, ya mik'a mata manyan ledojin Abinci, yaja motar sa yayi gidan su Maalesh.
*England*
Zaid ne kwance kan tafkeken Gadonsa yana waya da Mami, inda aka bashi Ayman ta dinga mai gwaran cin ta, har sukayi Sallama sannan ya kira Nasiba,
Suk gaisa ya tambayeta ya jikin Nene ta amsa masa da sauk'i.
Suka danyi hira sannan ya gaisa da Nenen itama ya musu Sallama.
Nan ya hau tunanin wanda zai sa ya musu Grocery shopping, don ya tabbatar suna da Buk'ata, baya son takura wa Rafeeq, Saboda abunda ya fahinta, Rafeeq has done more than Enough, kuma baya so ya k'ure shi .
Maalaesh ya fado ransa, Take ya kira wayansa, Ringing biyu ya dauka "Hello Mahmud" nan take ya gane Uncle Zaid ne, don shi yasan shi kadai ke kiran shi da sunan shi na Asali, "UncleZee ina wuni" suka gaisa, yace "Mahmud ina so donAllah ka min Shopping na kayan Abinci, da kayan buk'ata na Gida, ina so ka kai wani Gida na nan ku sa da gidanku na Layout(Gidansu Rafeeq yake nufi) Nan ya mishi kwatancen gidan. Malaesh yace "Angama, anything for you uncle Z" barin je yanzu ma, "barin maka transferring kudin" da sauri yace "Noo akwai kudi hanuna Uncle Z" "dont be Silly Son, i'm sending now" Murmushi Maalesh yayi yace "Nagode" suka yi Sallama, Nan take Zaid ya mai Transfer din 100k.
2:47pm