← Book details Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 95

Sashe 34

Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari
Tunda tayi Sallahn Asuba ta dinga tunanin Mafarkinta na jiya, Neneta lura da ita tace "lafiya Seebi?" Nene nayi mafarki da wata jiya, tana rokona in biya mata bashin lemun da ta siya, ina so in yi yanda tace" Nene tace "Sannu Sharifiya, wa yace miki Mafarki Gaskia ne?" nan Nasiba ta shashantar da maganar.
Tun daga ranar Nasiba ta dinga wasu Mafarkai masu tsoro, sai in dai bata kwanta bacci ba, da ta kwanta sai mafarkai masu ban tsoro, Yau dai ta tsaya tunanin dalilin mafarkanta, zuciyarta tace k'ila wannan mafarki na da nasaba da k'in biya ma wannan matar bashinta, tunda rana daya ta fara wannan mafarke mafarken, dole zata je ta biya mata bashin, ko ta samu kwanciyar hankali ta daina Mafarki.

Yau ta na zuwa Makaranta ta wuce Masanawa Super Market, ta ciro dari biyu ta mik'a ma me shago, yace "me zaa baki?" tace bakomai, wata rana kawata ta zo siyan Lacsera da dubu kace ba chanji, shine ta aiko ni in kawo maka, me shago ya amsa ya mika mata chanji, tazo juyawa taji ta taka kafar wani, a tsorace ta dago, ganin Rafeeq ya sa zuciyanta halbawa, be tsaya bin ta kanta ba ya wuce fridge ya ciro Soy milk, yazo gun biya ya ciro dari 5 ya bashi, be tsaya karban chanjin shi ba ya bar Shagon. Me shago yayi Murmushi yace "R-Lema kenan" Nasiba tace "mallam ka san shi ne?" yace ai ba wanda be san Rafeeq ba" Nasiba ta matso gunshi tace donAllah kasan dalilin da yasa yake haka? Yace "da Rafeeq na kowa ne, da da ya shigo zai dinga ja na da surutu, rana daya ya chanza, ba wanda yasan dalilin chanjin shi, gashi da k'okarin shi, duk Sciences shine over roll, amma Shekarar shi 6 a jamian nan, mates dinshi duk sun gana services dinsu, ba wai be da k'okari bane, aa ba wanda yasan dalilin Spilling din da yake tayi" Nasiba ta jinina kai tace "abun akwai ban mamaki, amma me ya maida shi hakan? Yace "ba wanda ya sani, iyakar abunda na sani kenan". Nasiba a ranta taji tana son sanin me ya maida R-Lema haka.

*MAFARKI*

"Ina Godia da Biyan bashin da kika min, Nagode, don yanzu na samu kwanciyar hankali" Nasiba tace toh "Alhamdulilah, bakomai" Yauwa kinyi abu na farko cikin Uku da na keso ki min, abu na biyu da nake so kimin shine; ina So ki binciki wani Makwabcin ku mai suna Rafeeq Habib Lema, ina so ki san ko shi waye, sannan kuma ina so ki shiga rayuwar shi" a razane Nasiba tace what? Kinsan me kike fada ne? Saboda mene zaki ce inyi haka, baiwar Allah don na taimaka miki dazun ba shi zai saki ki dinga sani abubuwa ba, ba zanyi ba, ba zan yi ba, mutumin da ko kallon arziki ban ishe shiba, toh ba zanyi yanda kike so ba, Musulmi na kwarai shine wanda be shiga hakkin da ba nashi ba" Yarinyar ta kama hannun Nasiba, kamar zatayi kuka, donAllah ki taimakeni, ki yarda dani" Cikin masifa Nasiba tace "Sabida mene zan yarda dake? Bansanki ba, bansan komai game dake ba, kinzo kina sani abubuwa? Toh wannan karon ba zan tainaka miki ba, kizo kiyi abunda kike sani da kanki, duk nisan da kike kizo ki yi aikin ki da kanki, idan kinso daga yau ki di ga zuwa min da mummunar siffa, ki hanani bacci, ba zanyi yanda kike si ba" . Yarinyar tayi dan murmushi, tace "da zan iya da nayi" Nasiba tace" zaki iya mana tunda kina tunanin ni zan iya" tace ke zaki iya don kina nan duniya, ni kuma ba zan iya ba, don bana duniya" cikin firgici Nasiba tace "me kike nufi da hakan?" Yarinyar tace " *My Name was Rafee'ah Habib Lema, na Rasu Shekara daya da Rabi da suka wuce*".

_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼‍♀

NA

BIEBEE ISA

® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

*Allah Sarki Yanuwa da Abokan Arzikki, da Masoya❤ duk na ga sak'onnin Ta'aziyoyin da kuka min, nagode Allah shi karb'a, ya biya ku, shikuma mamaci Allah ya ji k'anshi (Baba Hashimu) Allah ya gafarta mishi, Allah kasa ya huta. Da duk Musulman da suka riga mu Gidan Gaskia, mukuma in tamu tazo, Allah ya sa mucika da kyau da Imani Amin, Nagode Nagode Nagode, Allah ya barmu tare.👏🏽👏🏽👏🏽.*

Pg3⃣5⃣

Firgici da tsoro suka ziyarci zuciyar Nasiba, ta fara karkarwa, ta na ja da baya, baki na rawa tace "Fa+ta-talwa" Rafee'ah ta yi saurin cewa "DonAllah kar ki ji tsoro, banda niyyar cutar dake, ke musulma ce, kuma kinyi Imani da hakan, karda ki sa ma ranki ni Fatalwa ce, ni ba Fatalwa bace, da iko da k'uddirar Allah nazo miki a Mafarki, Mafarki kike yi dani, DonAllah ki kwantar da hankalin ki, banda niyyar cutar da ke .(Mu sani Ba Fatalwa a musulunci, Wanda ya mutu ya mutu, ba yanda matacce zaizo cutar da kai, in ka ga Mattace a ido, to gizo yake maka, ko kuma kayi mai mugun abu kafin ya mutu, ka sa ma ranka ne,shine kake ganin kamar zaizo maka, amma Tabbas ana mafarki da Matattu, _to Nasiba dai Mafarki takeyi da Rafee'ah_.)
Nasiba ta sauke numfashi, hankalin ta ya dan kwanta, Sai da Rafee'ah ta ga Nasiba ta samu natsuwa sai tace "Kamar yanda nace, ina so kin dan wanene Rafeeq, ina so ki shiga Rayuwar Rafeeq, ina so ki sauya duk wani abu da ya danganci Rafeeq, ina so ki warware zare da abawan cikin gidan Lema, akwai abubuwa da yawa da zaki fuskanta, akwai hadari a cikin wannan aikin, amma ki sa Allah a gabanki, ba zai barki ke kadai ba, sai kin jure kin daure". "Bazan iya ba, ni ala musuru ce? Da zan miki duk wadannan abubuwan? Saboda mene zaki dinga bibiyata cikin mafarki kina sani abubuwa?" inji Nasiba, Rafee'ah ta nuna ta da yatsa, tace saboda *"KE ALHERI CE"* cikin rashin fahimta Nasiba tace *"NI ALHERI CE?"* Rafee'ah ta gyada kai tace *"Eh, KE ALHERI CE"* ba za ki gane ba yanzu, amma a sannu zaki fahimci dalilina na ce miki haka, ta dan sasautar da murya tace "Nasiba, Rafeeq yaya na ne ina sonshi sosai, Rayuwar shi na cikin 6ata, ki taimake ni ki min wannan aikin, Allah kadai zai biya ki" Nasiba tayi shiru tana tunani, tabbas ita shaida ce kan halin Rafeeq na Shariya, da k'yaliya, itana tana kwadayin jin labarin shi, kuma tasan tabbas yana cikin damuwa, chan tace "Shikenan, Allah ya mana jagora" dadi ya lullube Rafee'ah, tace "Nagode Sosai, but one more thing, you must not tell anyone about your Dreams and your Mission, kar ki gaya ma kowa, komai kusancin ki da mutum, ki min Alkawari kinji?" Nasiba tace "InshaAllah ba wanda zai sani" Nagode sosai, ki fara binciken ki da wuri, ba mu da lokaci" Rafee'ah tace "InshaAllah". Rafee'ah ta mata sallama ta tafi, daidai nan Nasiba ta sauke ajiyar zuciya me nauyi cikin bacci, gyara kwanciyarta tayi.

_7:50am_

"Nene yi zaman ki, barin je in siyo k'osan", aa Seebi budurwa dake sai a ga kin tsaya bakin titi siyan k'osai? Yo meye? Wa ke bina bashi?" ni zanje, ba me bina bashi" Nene tace "kawai sai a ga yar budurwa kamar ki na bin layin k'osai?" Nasiba tace "ni kuma gani mara tausayi, kina fama da Masassara don kar ace gani budurwa, sai in barki kije siyan k'osai, to ba dani ba, kinga tafiya ta" Nenen tace "ai sai kiyi, tun yaushe zazzabin ya sauka?" Nasiba ba ta tsaya tanka ta ba ta fita daga dakin, Nene kuwa ta dan kishingida, ko minti daya baayi ba wayar Nasiba ta hau ruri, Nene ta buga tsoki " wani dan anacen ne ke kiran waya da fara saffiyan nan? Sun maida waya Kamar wata Ramadana, haka ta dinga mita har wayar ta tsinke, chan ta hau ruri, Nene ta mik'e ta zaro wayar k'ark'ashin pillown Nasiba ta latsa tare da cewa "Hello" "Assalam Alaikum Seebin mu ni da Nene" Nene tace "Laaah, Zaidu bawan Allah, Kai ne?" yayi murmushi kamar yana gavanta, yace "Eh Nene, nine, kamar kinsan kiran nan naki ne" tace "Allah ko? In ka ji kira Samu ne" yayi daria, yace "Addua nake buk'ata, an tura ni Ingila wani Aiki, kuma zanyi sati 3zuwa wata 1 a chan, shine muke barar addua" tace ai addua kullum cikin yinta muke, Allah ya kareka daga masu jan Kunne" yace "su waye masu jan kunne?" "Tabdijam! Turawa mana" Dariya Zaid yayi sosai, tace "Af! Daria na baka ko? Ai turawa muggai ne, sai an hadasu da *Li'ilafi kuraysh*" Sosai Zaid ke dariya, yasan idsn ya biye ma Nene, haka zata dinga sa shi daria har yayi missing flight dinshi, yace "nikam ina Seebin mu?" Taje siyo K'osai da burodi" Zaid tayi dan jim, Nene ta fuskanci shirun Xaid, Ehtace "kai ma kagani ai, gardama tsiya gareta sai da nace mata ta bari in siyo, tace wai aa, wai ban lafiya ita zata ta siyo" Zaid yace "baki Lafiya Nene? "Zazzabi ne ya lullube ni jiya da daddare, amma yanzu ta sauka, na ji sauki" "Nene ko zakije asibiti? "Kai ni rabani, komi Asibiti, to naji sauki" yace "to shikenan Nene, ni zan tafi, kice da Seebi zan kirata idan na sauka" Nenen tayi Murmushi tace "to Zaidun Seebi, Allah ya tsare ya kare ya bada saa" kiris ya rage dadi ya kashe Zaid, yaji dadin wannan kalami na Nene, yace "Amin Nenen mu".

*Kaskon Mai K'osai*
Chapter 34 · 0% Book details