Sashe 22
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_Kamar yadda kuka sani duk wadda tabi littafina daga page one zuwa yanzu tasan inda littafina ya dosa.. Kamar yarda kuka karanta kuka gani there is darkness in *Rafeeq's* life wanda yake saka shi yin duk wani abu da wasu dabiu da ba halinshi bane a da, wanda har na gangaro zuwa page 24 inda kowa ya gane dalilin shigar *Rafeeq* wannan yanayin da yake na yanzu._
_Kaidi irin na mata( *Wanda ko shaidan tsoronsu yake*) ya kuma hadu da kaidi na kishiya mara imani babu abinda baya janyowa.. abinda ya faru da Mami is well planned by Saude so ko sirikinta ne zai iya ganinta a yanayin data samu kanta_ _balle kuma dan cikinta sbd dama burinta ta kafa shaida mai kyau ta ido sbd idan dunia zata taru tana gaya ma *Rafeeq* abinda_ _mahaifiyarshi tayi bazai taba yarda ba kamar yarda uncle Zaid da iyayenta basu yarda ba..Saude tayi hakan ne dama don su gani da idonsu su zama shaidar kansu,wanda hakan ya tabi zuciyar Rafeeq har ya_ _haddasa mai duhu da bakin cikin da yake kwana yana tashi dashi kullu yaumun.._ _haka kuma rayuwarshi ta watse ta tarwatse sbd abinda ya gani da idonshi._
*_Kowacce tayi addua Allah ya rabata da muguwar kishiya sbd babu abinda basu iya aikatawa tunda babu Allah a cikin al ammuransu._*
_Allah yasa muna fahimta da amfana da darussan rayuwa dake ciki_
*Biebie* luv u loads💖❣💕
Pg2⃣6⃣
Kuka yakeyi kamar karamin yaro harda majina, Uncle Zaid beyi yunkurin hanashi ba, sai da yayi ma ishi kafin ya tsagaita da kukan. Uncle Zaid ya kira Maalesh yace yazo ya iske shi ring road yana jiran shi, kar yazo da mota, baa fi 15mins ba sai gashi, a rude Maalesh ya fito don be san meke faruwa ba yace "guy howfa? Kallo isasshe Rafeeq be ma Maalesh ba, Zaid ya mai alama da yayi shiru. Key din motar shi ya ba Maalesh, ba tare da ya tambayi me zaiyi da key din ba ya shige motar Uncle Zaid, shikuma zaid ya tura Rafeeq cikin motar sa, Zaid ya zauna a mazaunin driver ya ja motar ba me cema danuwan sa k'ala, jefi jefi Rafeeq yake sauke ajiyar zuciya, hanyar gida suka dauka, a hankali Rafeeq yace "please dont take me home" ba musu Zaid ya chanza hanya ya nufa gidan su Maalesh, daidai gidan su Maalesh Zaid ya tsaya yin horn, Rafeeq be jira maigadi yazo ya bude gidan ba ya fita daga motar ya shige Gidansu Maalesh ya nufi side dinshi.
Zaid ya girgiza kai ya fito, Maalesh ma ya fito, yace Uncle Zaid me ya faru da Rafeeq ne? Ban taba ganninshi haka ba, da kyar Zaid yace "he is broken" ya sake bashi key din motar shi, yace "je ka kai motar Rafeeq gida ka dawo yanzu" Akwai mutane cikin gidan?" Maalesh yace "aa Mummy taje kaduna, ba kowa" yace key din dakin ka fa? Maalesh yace "akwai daya gun Rafeeq, amma ga wannan incase ya barshi gida" Zaid ya amsa ya nufa cikin Tangamemen Gidan su Maalesh.
Be ga Rafeeq ba a kofar dakin, hakan ne ya bashi tabbacin Rafeeq na ciki, ya murda kofa yaji ta rufe, key din da Maalesh ya bashi ya zaro ya bude kofar, tare da shiga da Sallama, chan kusurwa ya ga Rafeeq kwance, be kula shi ba ya shiga toilet yayi Alwala kasancewar lokacin Sallah yayi.
Bayan ya idar da Sallah ya zauna kusa da Rafeeq ya janyo hannun shi ya hade da nashi, yace Rafeeq ka saurareni, "Mamin ka ba tayi- da sauri yace kar kayi shaidar zir Uncle Zaid, ni nasan abin da nagani, naga zahiri ba labari aka ban ba" Zaid yace najih Rafeeq, kaga zahiri ba labari aka baka ba, amma shin kagan su suna aikata Zina? Mahaifiyar ka ba ta chanchanci haka daga gareka ba, kar ka mance irin So da K'auna da take maka, Rafe--" Uncle Zaid ya isheni, Wallahi zan bar maka gidan nan, idan kana min maganar ta kana sawa ina k'ara tsanar ta" jimm Zaid yayi, sai ya yi shiru don baiwa Rafeeq Lokaci, ya mik'e yace "bari inje in dawo".
Isketa yayi kitchen tana kokarin dafa ma Alhaji Habib Ruwan Zafi, Hafiz yace " Sauda, na san kina da hannu akan abun da ya faru da Aishatu, komai shirin kine ke ki ka k'ulla mata wannan sharrin." tayi wulwul da ido, tace haba Hafiz, me kake cewa? Rashin imani na be kai nan ba, muna zaman lafia da ita me zai sa in neme ta da sharri, ni bansan me ka mayar dani ba, yace "Sauda na san halinki sosai, wallahi nayi bincike nagano gaskia, to zan tona miki asiri wallahi" Sauda tayi daria tace "Hafiz kenan, to barin fito maka da real color dina, idan nice me zakayi? Uban me kake iya yi? Kasan dai halina ko? Ka ka shiga gona ta, idan ka min shishigi zakayi kuka da kanka, kar ka manta Rayuwarka a tafin hannuna yake. I own u, so watchit" ta fice ta barshi tsaye.
Bakin gate ya hadu da Maalesh, yace ka kai Motar? "Eh Uncle Zaid" ok ban key dina ni, Maalesh ya nika mishi, yace "Uncle Zaid" Zaid yace ina sane da kai Maalesh, nasan there are millions of questions da kake so kayi, ka jirani ina zuwa, and Rafeeq give him space" Maalesh yace "Sai Ka dawo". Ya shiga ciki Zaid kuma ya fito.
Da Zaid ya koma gida be ga Mami ba, hankalin shi ya tashi, ya sauka kasa ya tambayi baba mai gadi yace ko ya ga wucewar ta? Ya bashi tabbacin ya ga ta fita da kaya, da alamu tafia zatayi, da sauri ya shige mota ya nufa gidan Baba Tijjani.
A sukwane ya shiga Parlorn, Baba Tj na zaune yana Azkhar, yace Zaid "lafia ka shigo a haka?" yace "baba ina Mami?" cikin mamaki yace wace "mamin? "Ina Aunty Aisha mamar Rafeeq?" Zaid ya dan fada a fusace, Baba Tijjani yace tana gidan ta mana, ce maka tayi zata zo nan? Baba dagaske ba ta nan? Yace "dama Ina maka karya?"Zaid yace "aa baba ba haka nake nufi ba, tabar gida ne na zata nan tayo, kuma wayarta a kashe" yace "aa ba mu ganta ba" Zaid be jira ba ya fita ba tare da ya basu labarin abun da ya faru ba, a ganin shi abun kunya ne suji Yayan shi ya sakar musu diya bayan hallacin da Baba Tijjani ya musu.
Mama tace "Alhaji ya ba ka gaya mishi gaskia ba? Yace kinsan halin Zaid, ba zai barta ba, duk inda take sai yaje ya daukota, abar ta ta gama iddan ta, she needs time" tace "Hakane"
Hankalin Zaid a tashe Matuk'a, duk inda yasan zai bincike Mami Aisha yaje be ganta ba, ya kira wayarta yafi a irga a kashe, Zafi biyu, ga rashin sanin inda take, ga matsalar Rafeeq, a bayyane yace "Allah kayi mana Agaji" yayi niyyar zuwa gidansu Maalesh don ganin Rafeeq, sai ya fasa don yasan Rafeeq na bukatar lokaci sai kawai ya wuce gida.
Hafiz ya sake labarta mai abunda ya faru, Zaid yace "wallahi Hafiz Shiri ne, ban yarda ba, akwai wata manakisa, kuma i promise i wont rest har sai na gano who is behind this na sada shi da hukuma" Hafiz ya danyi jim, so yake ya gaya ma Zaid wacce yake zargi, amma sai ya tuna gargadin da ta mishi dazun, inda take cewa "Hafiz, dont try to bring me down, if i go down, i'll drag you down with me" miyau ya hadiye yace "gaskian ka Zaid, its hard to believe, Allah ya baiyanar da Gaskia cikin sauki" Zaid be ce komai ba saboda yanda Zuciyar sa ke tafasa. Wurin Yayan shi ya hau a sama, ya ci saa shi kadai ke Parlorn, ya shiga da Sallama, har yanzu be bar kukan ba, Zaid ya kalli yayan shi cike da Tausayi, yace "Yaya kaima kuka kakeyi?" Habib Yayi murmushin takaici yace Zaid " kaga abun da uwar dakin ka ta yi min ko?" Zaid cikin bacin rai yace "yaya kaima ka yarda? Haba yaya, wai ba ka san wacece Aisha ba? Shekarun ku nawa da ita? Tun kuruciyart bata kawo gardi gida ba sai yanzu da ta fara tsufa har da diyanta? Haba Yaya kai haka kake baka bincike? Haka fa kamin a baya, dai daga baya kazo kana da nasani, you should have give her a time to explain, am sorry but ka dinga amfani da hankali." Habib yayi shiru yana nazari, magananganun Zaid sun shige shi, daga kallo daya zaka san cewa jikin shi yayi sanyi, amma ya kasa cewa komai, Sauda da ke labe a bakin k'ofa ta ja tsaki, tace wannan Zaid din yana neman bata min shiri, amma da sannu zanyi maganin shi"
Tana shiga daki ta kira Boka na kan tudu, ta nemi da ya janye tunanin Aishatu daga kan Habib, Boka yace ba matsala, anyi an gama, tace "yauwa, saura Maganan k'anin nan nashi, Zaid, Boka yace "uhm uhm Sauda, kar ki b'allo ma kanki ruwa, ki rabu da wannan, amma shi kina iya hadawa da kissan ku na mata" tace "to shikenan yanzu dai ka janye min hankalin Alhajin".
"Rafeeq be kamata ace kana fadan mugun kalamai kan mahaifiyar ka ba" Maalesh ne ke zancen nan cikin bacin rai, Rafeeq ya kalleshi galala yace "Maalesh, ka min shiru, idan kuma so kake ka nuna min nan Gidan ku ne, sai na tafi na bar maka gidanku yanzu, ba wai ce maka akayi na rasa wurin zuwa bane" Maalesh ya buga tsaki tare da fita ya bar mai dakin don idan ya biye ma Rafeeq zasuyi ba dadi cikin daren nan.
Bayan Kwana 3
_Kaidi irin na mata( *Wanda ko shaidan tsoronsu yake*) ya kuma hadu da kaidi na kishiya mara imani babu abinda baya janyowa.. abinda ya faru da Mami is well planned by Saude so ko sirikinta ne zai iya ganinta a yanayin data samu kanta_ _balle kuma dan cikinta sbd dama burinta ta kafa shaida mai kyau ta ido sbd idan dunia zata taru tana gaya ma *Rafeeq* abinda_ _mahaifiyarshi tayi bazai taba yarda ba kamar yarda uncle Zaid da iyayenta basu yarda ba..Saude tayi hakan ne dama don su gani da idonsu su zama shaidar kansu,wanda hakan ya tabi zuciyar Rafeeq har ya_ _haddasa mai duhu da bakin cikin da yake kwana yana tashi dashi kullu yaumun.._ _haka kuma rayuwarshi ta watse ta tarwatse sbd abinda ya gani da idonshi._
*_Kowacce tayi addua Allah ya rabata da muguwar kishiya sbd babu abinda basu iya aikatawa tunda babu Allah a cikin al ammuransu._*
_Allah yasa muna fahimta da amfana da darussan rayuwa dake ciki_
*Biebie* luv u loads💖❣💕
Pg2⃣6⃣
Kuka yakeyi kamar karamin yaro harda majina, Uncle Zaid beyi yunkurin hanashi ba, sai da yayi ma ishi kafin ya tsagaita da kukan. Uncle Zaid ya kira Maalesh yace yazo ya iske shi ring road yana jiran shi, kar yazo da mota, baa fi 15mins ba sai gashi, a rude Maalesh ya fito don be san meke faruwa ba yace "guy howfa? Kallo isasshe Rafeeq be ma Maalesh ba, Zaid ya mai alama da yayi shiru. Key din motar shi ya ba Maalesh, ba tare da ya tambayi me zaiyi da key din ba ya shige motar Uncle Zaid, shikuma zaid ya tura Rafeeq cikin motar sa, Zaid ya zauna a mazaunin driver ya ja motar ba me cema danuwan sa k'ala, jefi jefi Rafeeq yake sauke ajiyar zuciya, hanyar gida suka dauka, a hankali Rafeeq yace "please dont take me home" ba musu Zaid ya chanza hanya ya nufa gidan su Maalesh, daidai gidan su Maalesh Zaid ya tsaya yin horn, Rafeeq be jira maigadi yazo ya bude gidan ba ya fita daga motar ya shige Gidansu Maalesh ya nufi side dinshi.
Zaid ya girgiza kai ya fito, Maalesh ma ya fito, yace Uncle Zaid me ya faru da Rafeeq ne? Ban taba ganninshi haka ba, da kyar Zaid yace "he is broken" ya sake bashi key din motar shi, yace "je ka kai motar Rafeeq gida ka dawo yanzu" Akwai mutane cikin gidan?" Maalesh yace "aa Mummy taje kaduna, ba kowa" yace key din dakin ka fa? Maalesh yace "akwai daya gun Rafeeq, amma ga wannan incase ya barshi gida" Zaid ya amsa ya nufa cikin Tangamemen Gidan su Maalesh.
Be ga Rafeeq ba a kofar dakin, hakan ne ya bashi tabbacin Rafeeq na ciki, ya murda kofa yaji ta rufe, key din da Maalesh ya bashi ya zaro ya bude kofar, tare da shiga da Sallama, chan kusurwa ya ga Rafeeq kwance, be kula shi ba ya shiga toilet yayi Alwala kasancewar lokacin Sallah yayi.
Bayan ya idar da Sallah ya zauna kusa da Rafeeq ya janyo hannun shi ya hade da nashi, yace Rafeeq ka saurareni, "Mamin ka ba tayi- da sauri yace kar kayi shaidar zir Uncle Zaid, ni nasan abin da nagani, naga zahiri ba labari aka ban ba" Zaid yace najih Rafeeq, kaga zahiri ba labari aka baka ba, amma shin kagan su suna aikata Zina? Mahaifiyar ka ba ta chanchanci haka daga gareka ba, kar ka mance irin So da K'auna da take maka, Rafe--" Uncle Zaid ya isheni, Wallahi zan bar maka gidan nan, idan kana min maganar ta kana sawa ina k'ara tsanar ta" jimm Zaid yayi, sai ya yi shiru don baiwa Rafeeq Lokaci, ya mik'e yace "bari inje in dawo".
Isketa yayi kitchen tana kokarin dafa ma Alhaji Habib Ruwan Zafi, Hafiz yace " Sauda, na san kina da hannu akan abun da ya faru da Aishatu, komai shirin kine ke ki ka k'ulla mata wannan sharrin." tayi wulwul da ido, tace haba Hafiz, me kake cewa? Rashin imani na be kai nan ba, muna zaman lafia da ita me zai sa in neme ta da sharri, ni bansan me ka mayar dani ba, yace "Sauda na san halinki sosai, wallahi nayi bincike nagano gaskia, to zan tona miki asiri wallahi" Sauda tayi daria tace "Hafiz kenan, to barin fito maka da real color dina, idan nice me zakayi? Uban me kake iya yi? Kasan dai halina ko? Ka ka shiga gona ta, idan ka min shishigi zakayi kuka da kanka, kar ka manta Rayuwarka a tafin hannuna yake. I own u, so watchit" ta fice ta barshi tsaye.
Bakin gate ya hadu da Maalesh, yace ka kai Motar? "Eh Uncle Zaid" ok ban key dina ni, Maalesh ya nika mishi, yace "Uncle Zaid" Zaid yace ina sane da kai Maalesh, nasan there are millions of questions da kake so kayi, ka jirani ina zuwa, and Rafeeq give him space" Maalesh yace "Sai Ka dawo". Ya shiga ciki Zaid kuma ya fito.
Da Zaid ya koma gida be ga Mami ba, hankalin shi ya tashi, ya sauka kasa ya tambayi baba mai gadi yace ko ya ga wucewar ta? Ya bashi tabbacin ya ga ta fita da kaya, da alamu tafia zatayi, da sauri ya shige mota ya nufa gidan Baba Tijjani.
A sukwane ya shiga Parlorn, Baba Tj na zaune yana Azkhar, yace Zaid "lafia ka shigo a haka?" yace "baba ina Mami?" cikin mamaki yace wace "mamin? "Ina Aunty Aisha mamar Rafeeq?" Zaid ya dan fada a fusace, Baba Tijjani yace tana gidan ta mana, ce maka tayi zata zo nan? Baba dagaske ba ta nan? Yace "dama Ina maka karya?"Zaid yace "aa baba ba haka nake nufi ba, tabar gida ne na zata nan tayo, kuma wayarta a kashe" yace "aa ba mu ganta ba" Zaid be jira ba ya fita ba tare da ya basu labarin abun da ya faru ba, a ganin shi abun kunya ne suji Yayan shi ya sakar musu diya bayan hallacin da Baba Tijjani ya musu.
Mama tace "Alhaji ya ba ka gaya mishi gaskia ba? Yace kinsan halin Zaid, ba zai barta ba, duk inda take sai yaje ya daukota, abar ta ta gama iddan ta, she needs time" tace "Hakane"
Hankalin Zaid a tashe Matuk'a, duk inda yasan zai bincike Mami Aisha yaje be ganta ba, ya kira wayarta yafi a irga a kashe, Zafi biyu, ga rashin sanin inda take, ga matsalar Rafeeq, a bayyane yace "Allah kayi mana Agaji" yayi niyyar zuwa gidansu Maalesh don ganin Rafeeq, sai ya fasa don yasan Rafeeq na bukatar lokaci sai kawai ya wuce gida.
Hafiz ya sake labarta mai abunda ya faru, Zaid yace "wallahi Hafiz Shiri ne, ban yarda ba, akwai wata manakisa, kuma i promise i wont rest har sai na gano who is behind this na sada shi da hukuma" Hafiz ya danyi jim, so yake ya gaya ma Zaid wacce yake zargi, amma sai ya tuna gargadin da ta mishi dazun, inda take cewa "Hafiz, dont try to bring me down, if i go down, i'll drag you down with me" miyau ya hadiye yace "gaskian ka Zaid, its hard to believe, Allah ya baiyanar da Gaskia cikin sauki" Zaid be ce komai ba saboda yanda Zuciyar sa ke tafasa. Wurin Yayan shi ya hau a sama, ya ci saa shi kadai ke Parlorn, ya shiga da Sallama, har yanzu be bar kukan ba, Zaid ya kalli yayan shi cike da Tausayi, yace "Yaya kaima kuka kakeyi?" Habib Yayi murmushin takaici yace Zaid " kaga abun da uwar dakin ka ta yi min ko?" Zaid cikin bacin rai yace "yaya kaima ka yarda? Haba yaya, wai ba ka san wacece Aisha ba? Shekarun ku nawa da ita? Tun kuruciyart bata kawo gardi gida ba sai yanzu da ta fara tsufa har da diyanta? Haba Yaya kai haka kake baka bincike? Haka fa kamin a baya, dai daga baya kazo kana da nasani, you should have give her a time to explain, am sorry but ka dinga amfani da hankali." Habib yayi shiru yana nazari, magananganun Zaid sun shige shi, daga kallo daya zaka san cewa jikin shi yayi sanyi, amma ya kasa cewa komai, Sauda da ke labe a bakin k'ofa ta ja tsaki, tace wannan Zaid din yana neman bata min shiri, amma da sannu zanyi maganin shi"
Tana shiga daki ta kira Boka na kan tudu, ta nemi da ya janye tunanin Aishatu daga kan Habib, Boka yace ba matsala, anyi an gama, tace "yauwa, saura Maganan k'anin nan nashi, Zaid, Boka yace "uhm uhm Sauda, kar ki b'allo ma kanki ruwa, ki rabu da wannan, amma shi kina iya hadawa da kissan ku na mata" tace "to shikenan yanzu dai ka janye min hankalin Alhajin".
"Rafeeq be kamata ace kana fadan mugun kalamai kan mahaifiyar ka ba" Maalesh ne ke zancen nan cikin bacin rai, Rafeeq ya kalleshi galala yace "Maalesh, ka min shiru, idan kuma so kake ka nuna min nan Gidan ku ne, sai na tafi na bar maka gidanku yanzu, ba wai ce maka akayi na rasa wurin zuwa bane" Maalesh ya buga tsaki tare da fita ya bar mai dakin don idan ya biye ma Rafeeq zasuyi ba dadi cikin daren nan.
Bayan Kwana 3