← Book details Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 95

Sashe 7

Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Lagos
Karfe 9 na safe Uncle Zaid da Alhaji Habib na Secret Service Agency (SSA), bayan long process aka sa da su da wani Oga, tambayoyi ya musu na Alakar su da Hafiz, Habib ya bashi amsa da "mu yanuwan sa ne, ni yayan shi, wannan kuma kanin shi" Ogan ya dauki wasu files guda biyu ya mika ma Alhaji Habib, ya amsa hannu biyu ya bude, hotuna ne na Hafiz da wasu 6, Zaid ya gane daya daga cikin su, abokin Hafiz nr wato Anas, a cikin hoton aka ga Boma-bomai,Bindigogi da wuk'ak'e, cikin su ya juya, Habib ya bude dayan file din, paper ce doguwa, ya shiga karantawa, Hafiz was an accomplice to Armed Robbers. Hankalin Habib ya tashi, ya fara hawaye, Zaid ya amsa ya karanta shima, kanshi ya girgiza cike da takaici. Oga yace "toh sati 2 da suka wuce ne ya cika Shekarun da aka diba mishi, an ki sakin shi ne sai ya bada 500usd, mun ta tamabyan shi wa zaizo bailing dinshi, yak'i magana, da ya ga bamu da niyyar sakin shi ne shine ya bada numbern ku, Zaid yace "yanzu 500usd za a baku sai ku sake shi?" Oga yace "eh" Zaid ya danyi guntun tsaki ya sa hannu cikin aljihun shi, ya ciro rafar dubu 3 ya dora ma Oga kan table, mutumin yayi murmushi yace "Sir we dont do it this way, u go to the bank and draft it to our Account" Zaid ya dan daga murya yace "you should have said that at first, u think we have time for this? Habib ya kalli Zaid yace "Calm down Engr" Mutumin yace "unless you'll pay here the change will be mine, you know 500usd is approximately to N250,000, and this is 300k" Zaid ya mai tsawa yace "shut the fuckup, take d goddam money and get us our Brother" Mutumin yayi daria ya mike tare da kallon Alhaji Habib, yace "i see your bro has guts, i'll get ur brother now" ya fita.

Alhaji Habib yace "Zaid, kayi hakuri, muke nema gurin su, dole mu kwantar da kan mu" Zaid cikin fushi yace "yaya rabu dasu, iskanci ne, ji fa yanda yake magana, matsiyaci, kudi ne matsalan shi" Habib yace "ayi dai hakuri" duk sukayi shiru.

Turo kofa akayi, Habib da Zaid suka mik'e tsaye, idon su kan kofar shigowa, Ogan ne ya fara shigowa Hafiz a bayan shi, Hafiz yayi bak'ih duk kyaun nan ya disashe, ga wata uwar k'asumba ya ajiye, duk yayi ba kyan gani, Rige rigen zuwa gunshi Zaid da yayan shi sukayi, Hafiz ya fashe da kuka, suko ba su damu da yananyin da yake ba suka rungume shi suna hawayen suma. Da kyar hafiz yace "ku gafarce ni yanuwa na, na san ban kyauta muku ba" Alhaji Habib yace "shhh, Hafiz not now, lets get outta here"

Suka nufa hanyar fita, Zaid ya watsa ma Oga harara, shi ko dariya ya bashi don yaga Zaid ya dauki abun da Zafi, yace ga Kayan shi da aka amsa kafin a kulle shi, Zaid yace "ka jika ka sha an bar maka" sosai Officern yayi daria, yace "till we meet again ko" Zaid yace "ganinka ba Alheri ba, ba Amin ba" ya fita shima.

Drivern Office din Lema textile Company Zaid ya kira, within some minutes ya hallara Agency din, ba jira suka shiga, Golden Hotels suka nufa, Hafiz ya shiga dakin shi, yafi 1hour yana wanka, yana fitowa ya ga Wasu riga da Wando da Zaid ya siyi mishi, ya dauka ya saka yaci abinci yayi Sallah. Bayan sun huta Driver ya sake zuwa ya dauke su, yayi Airport dasu, don yau suke son wuce wa. Bayan mintuna kalilan jirgin su ya tashi, Cikin Awa daya suka iso Kano ta dabo. Kafin suje masauki sai da suka biya Barbers Corner don a ma Hafiz Aski, Tsaf hafiz ya fito da kyau, don yini dayan da yayi ya fara kyau. Washegari driver ya dauke su sai Katsina ta dikko dakin kara.

Tana tsaye tsakar Gida tana jiran isowar su, don tun da suka shigo KT Alhaji ya kirata yace sun iso, ga su nan karasowa. Rafeeq da Rafee'ah na school, Mota na shigowa Haraban Gidan gaban Hafiz ya bada Hinqim, komai ya dawo mai sabo, a ranshi yace "it all started here" Sannu da zuwa Aisha take ta faman yi ma Hafiz, harda hawayenta, Hafiz duk ya koma wani sukuku, be sakin jikin shi, ta gabatar musu da abinci, kadan Hafiz yaci, yanda kuka san bak'o sai rab'e rab'e yake tayi. Alhaji Habib ya lura dashi yace "ka sake jikinka Hafiz dis is your home" Hafiz yayi murmushin takaici, yace "Yaya, nasan duk kuna da miliyoyin tambayoyin da kuke so ku min, kuna so kuji yanda na tsinci kaina a kurkuku" Habib ya katseshi yace " Aa Hafiz, abunda ya wuce ya riga ya wuce, kar a maida hannun Agogo baya, muyi addua Allah ya tsayar nan kawai" Hafix ya girgiza kai yace "Aa yaya, dole ku san me ya faru, dole kusan irin rayuwan da nayi bayan bari na Gida" Zaid yace "Gaskia ne, muna sauraronka" Hafiz ya fara labarinshi kamar haka:

Shekaru Goma da suka gaba ta(Last 10years)

Muna barin Katsina, Straight dauki hanyar Porthacourt, ni da Abokaina 2, Anas da Eskaley, mun kwana mun yini a hanya, har muka isa wani gida, Gidan Thug Gang (Sunfi kama da kauraye )din su Anas ne Amstrong da Willy, Kwanan mu 2 a PH Anas suka nuna min wuraren bude idanuwa, kamar Night Club, Gambling Center, Da Gidajen giya, duk na kware a harkokin nan.

Ba mu rufe Sati 2 ba naji Armstrong na gaya ma Anas su shirya akwai Operation yau da daddare gidan Commisioner, yace "okay we'll prepare" nace da Anas wani irin operation ne wannan? Anas yayi daria yace "my guy, ba zaka gane bane, share kawai" Nace "haba Anas, kar ka mun haka, ka fada min mana" yace "kagane, Amstrong ce min kawai yayi zamuje iperation, amma be gaya min takamaimin me zamuyi ba" Nace "then i will go with u" Anas yayi dariya yace "no u cant, yi shiru kar ma Armstrong ya jika" ashe Armstrng na jin mu, yace "he's right you cannot come with us boy" boy ne sunan da Armstrong ke cemin kenan tun zuwan su PH, a ganinshi ni karamin dan iska ne, cikin fusata nace "i am not a boy" Armstrong yayi murmushi yace "show me, today get ready and be prepared" Anas yace "Oga i dont think this is a good idea" Armstrong yace "its time we train him".

3:00am
Gidan Commisioner of Youths suka kai ma farmaki, duk suka hade kan mutanen gidan cikin babban parlor harda shi Commisioner din. Hafiz aka bari a Cikin mota, da bindigar Katako, bayan Armstrong ya buge mai warning, kar ya bar bakin mota, no matter what, don zasu iya fitowa at anytime, Anas, Eskaley, da armstrong suka shiga ciki, duk a zaton shi sauran ma bindigar katakon ne, duk a zaton shi kudi kawai zasu amsa suyi gaba, sai labari ya sha bambam da yaji karar bindiga, sosai ya tsorata, Be ankara ba yaji Siren din motocin police, Hafiz ya kidime ya fito daga motan da gudu, charap police suka kamashi da yake Ajebo ne be iya gudu ba.

Su Eskaley kuwa sai fafatawa suke da jamian tsaro, suna harbin junan su, nan take a ka harbe su 3, ko shurawa basuyi ba suka mutu, Iyalan Commisioner kuwa ba wanda ya mutu, sai dan shi da Anas ya harba a kafada, an garzaya dashi Ambulance.

Abun da ya faru shine, Ashe Akwai diyar Commisioner da take wayan dare(NightCall) ta bayan dakin ta taji ana cewa "Idan ya kawo gaddama kawai mu harbesu mu shiga mu nemi golds a dakun nan su, yanzu kawai mu nemi hanyar shiga cikin gidan" da gudu ta diro a kan gado ta fita da gudu, straight dakin babanta tayi ta gaya mai Abun da taji, da sauri ya danna waya ya kira Jami'an tsaro ya sanar da su, suka bashi tabbacin gasu nan zuwa, da sauri ya nufa dakin matar shi da babban danshi don sanar da su, kafin kace meye wannan yaji an dora mai bindiga a kai, Anas ne yace "idan ka motsa sai na tarwatsa kanka" Commisioner ya sandare, Eskaley da Amstrong suka shiga sauran dakuna suka fito da duka mutanen gidan, suna tambayan kud'adde ne Police sukayi surrounding dinsu duka har suka kashe su Anas.

Hafiz ya cigaba da cewa" ko bincike ba a tsayayi ba aka maka ni kotu, kasancewar ni kadai suka kama jikina yayi sanyi, na fada musu gaskia, na amsa laifi na, Kotu me adalci ta ya yanke min hukuncin 10years a Jail+ hardships da 500usd Fine, to kunji abunda ya faru dani bayan bari na Gida. Allah sarki danuwa mai dadi, daga Alhaji Habib da Zaid kuka suke barin ma Aisha da tun farkon Labarin Hafiz take kuka. Sai da sukayi me isar su duka kafin Hafiz ya duk'a har k'asa ya nemi gafarar su duka, Habib yace bakomai Hafiz Allah shi kyauta gaba, Allah ya sa kuma ka koyi darasi, duk wanda ya bar gida gida ya barshi. Hafiz yace "InshaAllah Yaya, ba za ku sake kamani da wani laifin ba", yace "toh Allah yasa" ya juya ya kalli Aunty Aisha yace "Aunty kiyi hakuri da duk abunda na miki, da sauri ta katse shi tace baka min komai ba, Allah ya yafe mana" Hafiz ya kalli Zaid zai yi magana, Zaid ya tareshi da murmushi yace "Welcome home Brother".
(Muma munce Welcome Hafiz Lema, Lubie maitafsir tace "Dont cause any trouble" Aisha Yau kuma tace "Allah ya sa ba tuban muzuru kayi ba😐", nidai Biebee nace ku biyoni kuji rayuwan Gidan Lema bayan dawowar Hafiz Lema)

_Bibilicious Biebee
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼‍♀

NA

BIEBEE ISA

® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)

Pg1⃣9⃣

Amarya ta dan daga kai taga tabbas Rafeeq ne ke wannan chashewar, wuri ya dauu sowa sabida Rafee'ah ta tashi cikin takun ta ta biyo Rafeeq filin rawa tana mishi like, shi ko sai rawa yakeyi iya karfin shi. Sai da Zaid ya mishi alamun ya isa kafin ya tsagaita.
Chapter 7 · 0% Book details