Sashe 49
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*Katsina*
Nene ina kika shige ana ta kira? tace kai dai bari, gani ina ta Soya Farar da Anan yace a soya mai in ka dawo da Seebi in baka ka kaimai" Abbi yace "kema dai Nene, sai ki biye ma Anan don yace yana son Fara, shi yanzu haka ya mance" tace "Tiya biyu na siyo mai, baka ga bak'ar wahalar da naci a kasuwa ba, kuma ina dawowa na gyara ta, yanzu har na soya tiya daya, gani ina soya gudan tiyar" Abbi yace "Taya b'era b'ari".
Yau be jira amsan Sallamar ta ba ya shigo ciki, sakamakon wani k'amshin da yaji, ya na tunanin k'amshin meye wannan? Wannan dai ya fi karfin suyan kaza, tana waya ta ganshi tsaye, tace " yau kuma Sallamar da akeyi k'asa k'asa baa samu damar yi ba? Ko muryar ce ta ida daukewa? Ni tashi min akai ga kujera chan" Abii yace "Nene ke da waye?" tace "ni da Dunkum" "wanene kuma Dunkum?" tace "ka tambayi Seebi waye Dunkum dangin Tsaka" Inaaaa Sam Rafeeq be san tana yi ba, hankalin shi na kan Soyayar Farar da ke cikin gwagwa, ya hadiye wani mugun miyau kamar tsohon maye, rabonshi da Fara shekari sun fi 10, tun suna zuwa Islamiyya, nan Rafee'ah zata siyo musu, suyi taci, har Farar dari 2 suke siya, haka kurum yaji yana son cin Farar nan, ko don tuna baya, yana son cin farar nan for times sake, kuma dai yana so. Nene ta sauke kaskon ta hadeshi da na gwagwan, tana dagowa taga idon Rafeeq tsam kan gwagwar Fara wani shu'umin Murmushi tayi, a ranta tace"Yau ranar Nene ce" Ta dauki soyayyar cinyar farar nan ta sa a baki, ta wani lumshe ido tace "kaii wannan fara zad dadi, kamar kunne na ya tsinke" Rafeeq ya sake hadiye miyau, suna hada ido da Nene yayi saurin shan mur ya dauke kai, a ranta tace "yaro da ni kake zance" ta shige daki ta zauna tana kallon shi ta windo, a ranshi yace "na san wannan tsohuwar ba bani Faran nan zatayi ba, kuma gashi raina ya biya, i want, i will just take it" be tsaya wata wata ba ya durkusa ya dibi guda biyu ya sa a baki, waiyo dadi, yana kara sa hannu yaji an damk'o bayan rigar sa tace "Yihuhu Na chafko shi, na chafko b'arawon fara ta" a hankali yace "Akwai matsala Lord Have Mercy".
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg4⃣4⃣
Ya dago fuska a daure kamar bai taba dariya ba, ya bi hannunta da ido, yanda ta rik'e mishi bayan riga, a hankali yace da ita "Sakeni" tace "nak'i na sake ka din, nace nak'i" yace "me na miki da zaki rike min riga?" "tambaya kakeyi? To Sata kai man, ka satar min Fara" ya sake tamk'e fuska, wai wani irin Sata?" wanda ka min mana, ai daukan abun da ba naka ba Sata ne, ni kuma ban baka Fara ta ba ka dauka" ya nuna farar da yatsa yace "wanchan abun zanci, Allah ya kiyaye in ci k'waro" tace "Kai Dunkum, ka fita idona, ni da na ganka durkushe, in ba ci min Fara kakeyi ba meyasa zaka durk'usa a gun? Ruku'u kakeyi?" da k'yar yace "da ki ka ganni Durkushe k'andagare na ga zai hau, shine na kore shi, dana sani da na barshi ya hau" tace "Ayiriri nanaye, kai Dunkum ka raina ma kanka wayau ba ni ba, Shekaru na Goma so Shidda da dori (60+) kasan ko ba kalar barikin da ban gani ba, tunda ka ci min Fara ta, ina so ka amsa laifin ka, ka bani hak'uri a wuce wurin" guntun tsaki yayi ya juya zai bar gidan, da sauri ta jawo rigar shi, tace "Sai fa ka ban hakuri" a k'agauce yace"Goodness, Wallahi kina da Damuwa, ga ki da Hayaniya" tace "zaka ga damuwa idan kaji ka a *Jakar Magori*" kallon Rashin Fahimta ya mata, tace "Too, ba ka san Jakar Magori ba ko? No radio a gida? To wurin da zan kai Labarin ka ne, k'arfe 11 dare in ka kunna Radio zakaji ance "Jakaaaar Magori, Dunkum ya Saci Farar Nene a garin Katsina" a ranshi yace "this Woman is Unbelievable, zata aika" ganin idan ya biye mata zasu ta Fafatawa ne, gashi kuma yau ta sashi magana fiye da Sentence 10, kanshi har ya fara ciwo, juyawa yayi zai fita, Nene ta sake Chafko Rigar shi, Tsoki ya buga da k'arfi yana cewa "wai ke wace iri ce?" "sai fa ka bada hakuri"
Daidai nan Maalesh ya shigo da Sallama, Nene na ganin shi tace "Yauwa Maalush, zo kayi Shaida, Dunkum ya min satar Fara" Maalesh da Murmushi kwance kan fuskar shi yace "Nene, ban gane ba?" tace ka tambayi "Dunkum ya maka bayani" ya juya ga Rafeeq ya ga irin rik'on da ta mai kamar wanda ya saci Mota, daria ya kubce mai, yace "Guy howfa? Looks like you've fall into the Old Woman's trap, what did you do?" Rafeeq cikin k'uluwa, yace "Tell her to let go" dak'yar Maaldsh ya sa Nene ta sake Rafeeq, tace " yo Maalush, ci min Fara yayi, kuma ni ban bashi ba, kuma ya k'i yarda ya ban hakuri, ni ko na kamashi kamar na kama Aradu" Maalesh ya fashe da Daria, ya juya ya kalli abun da aka kira da Fara, ya yamutse fuska kamar ya ga kashi, ga kalli Rafeeq da mamakin ta ya ya ci wanchan abun me kama da kyankyaso, yace "you ate that? Rafeeq yace "You are crazier than she is, i cant eat that" kamar ta san abunda yake cewa tayi saurin cewa "Karya yake, a shinshina hannun shi" Maalesh ya shashantar da maganar ta hanyar tambayar Nasiba tace "ai Nasiba kwananta 4 Kaduna Jibi zata dawo" "Lord of Mercy" inji Rafeeq, so All this While Nasiba na Kaduna? Yake bata lokacin shi on this Woman? Yazo ya sha zaman banza amma bata ce mishi Nasiba ba ta nan ba? (Ka tambayeta ne?) dogon tsaki yayi ya fincike mukullin hannun Maalesh ya fita, Nene ta bishi tana dariya tana fadin "Dunkum tsaya kaci Fara, tsaya a k'ulle maka Leda" daria takeyi sosai, don ta san yau tayi maganin Dunkum, Maalesh yayi Dariya, yace "ranshi ya baci, barin je" tace ranshi ne ya baci? To ya sa omo ko kilin ya wanke shi" Maalesh yayi dariya, yace barin je Nene zan dawo Anjima nima iso wata kenan" tace "Allah huta gajiya" ya fita amma be ga komai ba sai k'urar Motar shi, Murmushi yayi ya taka zuwa Gidan Lema a k'afa.
Yana shigowa dakin ya fada Toilet dinsa, Shower ya sakar ma kanshi, tunani kala kala, wai me ke kaishi gidan Nene ne? Zuciyar shi ta bashi amsa da "Kana kewar wannan Yarinyar ne" da sauri yace "Noo, ba ita nake missing ba, i only miss seeing my Sister in her" tsaki yayi yace "stop getting to my head i dont want" haka ya cigaba da magana shi kadai kamar zararre.
*5:00pm*
Zaman kadaici ya ishi Nene, ta rasa yanda zatayi, gashi ita ba gwanar shiga Makota ba, don gidajen makwabtan akwai Karnuka, kuma ai ta k'wank'wasa wa ba a amsa, Wayar Nasiba ta dauko ta kura wa wayar ido tana jira a kirata, shiru, ta na ta 'yan latse latsen ta, bata san ma dai abun da takeyi ba, tsaki ta buga "ina dalilin zaman mutum shi kadai" (Nene ke kika jawo) ta jawo Gyalenta ta fita waje,tana kallon Unguwar, Mugun tsaki ta buga da ta ga Unguwar Wayam ba ko dabban da ke wucewa, Kamar a sama taga wata Mota Me kalar bula(blue) ta doso ta, ai da murna ta fara sa ma Motar Hannu.
Birki na cikin motar su ka ja k'ii, don ba su lura da ita ba, a fusace Meema ta fito, Aneesa ma ta fito, Nene da Murmushin ta tace "Sannunku 'yan jikokina, kuyi hak'uri na tsaida ku, DonAllah ku dan latso min Zaidu bawan Allah a wayar nan" ta na me mik'a musu wayar Nasiba, Meema ta kalli wayar cike da tsana tace "Ke Almajira, in banda jahilci, ba ki sanmu ba zaki tsaida mu kice mu kira miki wani? Har kina daura k'azamin hannun ki kan mota ta?" Aneesa tace "Aunty Mee mu tafi don Allah, irin wannan da su ake conspiring a maka wani mugun abun, its all a ploy" Ta ja hannun Auntyn ta, suka koma Mota, Meema ta ja motar tare da bad'e Nene da k'ura, yanda kuka san Hoto haka Nene ta tsaya, wai yau ita a ka ci ma fuska kuma ba tace komai ba, haushinta daya da ba ta ci uwar babbar su ba, amma a fili tace "Ubangiji Allah ka sake hadani da su" ta koma Cikin Gida tana jin haushin kanta.
*Malali Kaduna*
Nene ina kika shige ana ta kira? tace kai dai bari, gani ina ta Soya Farar da Anan yace a soya mai in ka dawo da Seebi in baka ka kaimai" Abbi yace "kema dai Nene, sai ki biye ma Anan don yace yana son Fara, shi yanzu haka ya mance" tace "Tiya biyu na siyo mai, baka ga bak'ar wahalar da naci a kasuwa ba, kuma ina dawowa na gyara ta, yanzu har na soya tiya daya, gani ina soya gudan tiyar" Abbi yace "Taya b'era b'ari".
Yau be jira amsan Sallamar ta ba ya shigo ciki, sakamakon wani k'amshin da yaji, ya na tunanin k'amshin meye wannan? Wannan dai ya fi karfin suyan kaza, tana waya ta ganshi tsaye, tace " yau kuma Sallamar da akeyi k'asa k'asa baa samu damar yi ba? Ko muryar ce ta ida daukewa? Ni tashi min akai ga kujera chan" Abii yace "Nene ke da waye?" tace "ni da Dunkum" "wanene kuma Dunkum?" tace "ka tambayi Seebi waye Dunkum dangin Tsaka" Inaaaa Sam Rafeeq be san tana yi ba, hankalin shi na kan Soyayar Farar da ke cikin gwagwa, ya hadiye wani mugun miyau kamar tsohon maye, rabonshi da Fara shekari sun fi 10, tun suna zuwa Islamiyya, nan Rafee'ah zata siyo musu, suyi taci, har Farar dari 2 suke siya, haka kurum yaji yana son cin Farar nan, ko don tuna baya, yana son cin farar nan for times sake, kuma dai yana so. Nene ta sauke kaskon ta hadeshi da na gwagwan, tana dagowa taga idon Rafeeq tsam kan gwagwar Fara wani shu'umin Murmushi tayi, a ranta tace"Yau ranar Nene ce" Ta dauki soyayyar cinyar farar nan ta sa a baki, ta wani lumshe ido tace "kaii wannan fara zad dadi, kamar kunne na ya tsinke" Rafeeq ya sake hadiye miyau, suna hada ido da Nene yayi saurin shan mur ya dauke kai, a ranta tace "yaro da ni kake zance" ta shige daki ta zauna tana kallon shi ta windo, a ranshi yace "na san wannan tsohuwar ba bani Faran nan zatayi ba, kuma gashi raina ya biya, i want, i will just take it" be tsaya wata wata ba ya durkusa ya dibi guda biyu ya sa a baki, waiyo dadi, yana kara sa hannu yaji an damk'o bayan rigar sa tace "Yihuhu Na chafko shi, na chafko b'arawon fara ta" a hankali yace "Akwai matsala Lord Have Mercy".
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION(NWA)
Pg4⃣4⃣
Ya dago fuska a daure kamar bai taba dariya ba, ya bi hannunta da ido, yanda ta rik'e mishi bayan riga, a hankali yace da ita "Sakeni" tace "nak'i na sake ka din, nace nak'i" yace "me na miki da zaki rike min riga?" "tambaya kakeyi? To Sata kai man, ka satar min Fara" ya sake tamk'e fuska, wai wani irin Sata?" wanda ka min mana, ai daukan abun da ba naka ba Sata ne, ni kuma ban baka Fara ta ba ka dauka" ya nuna farar da yatsa yace "wanchan abun zanci, Allah ya kiyaye in ci k'waro" tace "Kai Dunkum, ka fita idona, ni da na ganka durkushe, in ba ci min Fara kakeyi ba meyasa zaka durk'usa a gun? Ruku'u kakeyi?" da k'yar yace "da ki ka ganni Durkushe k'andagare na ga zai hau, shine na kore shi, dana sani da na barshi ya hau" tace "Ayiriri nanaye, kai Dunkum ka raina ma kanka wayau ba ni ba, Shekaru na Goma so Shidda da dori (60+) kasan ko ba kalar barikin da ban gani ba, tunda ka ci min Fara ta, ina so ka amsa laifin ka, ka bani hak'uri a wuce wurin" guntun tsaki yayi ya juya zai bar gidan, da sauri ta jawo rigar shi, tace "Sai fa ka ban hakuri" a k'agauce yace"Goodness, Wallahi kina da Damuwa, ga ki da Hayaniya" tace "zaka ga damuwa idan kaji ka a *Jakar Magori*" kallon Rashin Fahimta ya mata, tace "Too, ba ka san Jakar Magori ba ko? No radio a gida? To wurin da zan kai Labarin ka ne, k'arfe 11 dare in ka kunna Radio zakaji ance "Jakaaaar Magori, Dunkum ya Saci Farar Nene a garin Katsina" a ranshi yace "this Woman is Unbelievable, zata aika" ganin idan ya biye mata zasu ta Fafatawa ne, gashi kuma yau ta sashi magana fiye da Sentence 10, kanshi har ya fara ciwo, juyawa yayi zai fita, Nene ta sake Chafko Rigar shi, Tsoki ya buga da k'arfi yana cewa "wai ke wace iri ce?" "sai fa ka bada hakuri"
Daidai nan Maalesh ya shigo da Sallama, Nene na ganin shi tace "Yauwa Maalush, zo kayi Shaida, Dunkum ya min satar Fara" Maalesh da Murmushi kwance kan fuskar shi yace "Nene, ban gane ba?" tace ka tambayi "Dunkum ya maka bayani" ya juya ga Rafeeq ya ga irin rik'on da ta mai kamar wanda ya saci Mota, daria ya kubce mai, yace "Guy howfa? Looks like you've fall into the Old Woman's trap, what did you do?" Rafeeq cikin k'uluwa, yace "Tell her to let go" dak'yar Maaldsh ya sa Nene ta sake Rafeeq, tace " yo Maalush, ci min Fara yayi, kuma ni ban bashi ba, kuma ya k'i yarda ya ban hakuri, ni ko na kamashi kamar na kama Aradu" Maalesh ya fashe da Daria, ya juya ya kalli abun da aka kira da Fara, ya yamutse fuska kamar ya ga kashi, ga kalli Rafeeq da mamakin ta ya ya ci wanchan abun me kama da kyankyaso, yace "you ate that? Rafeeq yace "You are crazier than she is, i cant eat that" kamar ta san abunda yake cewa tayi saurin cewa "Karya yake, a shinshina hannun shi" Maalesh ya shashantar da maganar ta hanyar tambayar Nasiba tace "ai Nasiba kwananta 4 Kaduna Jibi zata dawo" "Lord of Mercy" inji Rafeeq, so All this While Nasiba na Kaduna? Yake bata lokacin shi on this Woman? Yazo ya sha zaman banza amma bata ce mishi Nasiba ba ta nan ba? (Ka tambayeta ne?) dogon tsaki yayi ya fincike mukullin hannun Maalesh ya fita, Nene ta bishi tana dariya tana fadin "Dunkum tsaya kaci Fara, tsaya a k'ulle maka Leda" daria takeyi sosai, don ta san yau tayi maganin Dunkum, Maalesh yayi Dariya, yace "ranshi ya baci, barin je" tace ranshi ne ya baci? To ya sa omo ko kilin ya wanke shi" Maalesh yayi dariya, yace barin je Nene zan dawo Anjima nima iso wata kenan" tace "Allah huta gajiya" ya fita amma be ga komai ba sai k'urar Motar shi, Murmushi yayi ya taka zuwa Gidan Lema a k'afa.
Yana shigowa dakin ya fada Toilet dinsa, Shower ya sakar ma kanshi, tunani kala kala, wai me ke kaishi gidan Nene ne? Zuciyar shi ta bashi amsa da "Kana kewar wannan Yarinyar ne" da sauri yace "Noo, ba ita nake missing ba, i only miss seeing my Sister in her" tsaki yayi yace "stop getting to my head i dont want" haka ya cigaba da magana shi kadai kamar zararre.
*5:00pm*
Zaman kadaici ya ishi Nene, ta rasa yanda zatayi, gashi ita ba gwanar shiga Makota ba, don gidajen makwabtan akwai Karnuka, kuma ai ta k'wank'wasa wa ba a amsa, Wayar Nasiba ta dauko ta kura wa wayar ido tana jira a kirata, shiru, ta na ta 'yan latse latsen ta, bata san ma dai abun da takeyi ba, tsaki ta buga "ina dalilin zaman mutum shi kadai" (Nene ke kika jawo) ta jawo Gyalenta ta fita waje,tana kallon Unguwar, Mugun tsaki ta buga da ta ga Unguwar Wayam ba ko dabban da ke wucewa, Kamar a sama taga wata Mota Me kalar bula(blue) ta doso ta, ai da murna ta fara sa ma Motar Hannu.
Birki na cikin motar su ka ja k'ii, don ba su lura da ita ba, a fusace Meema ta fito, Aneesa ma ta fito, Nene da Murmushin ta tace "Sannunku 'yan jikokina, kuyi hak'uri na tsaida ku, DonAllah ku dan latso min Zaidu bawan Allah a wayar nan" ta na me mik'a musu wayar Nasiba, Meema ta kalli wayar cike da tsana tace "Ke Almajira, in banda jahilci, ba ki sanmu ba zaki tsaida mu kice mu kira miki wani? Har kina daura k'azamin hannun ki kan mota ta?" Aneesa tace "Aunty Mee mu tafi don Allah, irin wannan da su ake conspiring a maka wani mugun abun, its all a ploy" Ta ja hannun Auntyn ta, suka koma Mota, Meema ta ja motar tare da bad'e Nene da k'ura, yanda kuka san Hoto haka Nene ta tsaya, wai yau ita a ka ci ma fuska kuma ba tace komai ba, haushinta daya da ba ta ci uwar babbar su ba, amma a fili tace "Ubangiji Allah ka sake hadani da su" ta koma Cikin Gida tana jin haushin kanta.
*Malali Kaduna*