Sashe 6
Ke Alheri Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu yanda zatayi dashi da ya wuce ta bi bayanshi, tafia yake a nutse kamar be son taka kasa, fuskar nan tamke tamau duk inda suka wuce ji kake ana "R-Lema" mutane ba su damu da yanda yake basar da su ba idan sun kira sunan shi, ita ko Seebi ta kasa dauke idanuwan ta daga kallon shi, karantar shi take yi, komi nashi daban, ba kamar wasu mazan ba, ta tabbatar da wani ne suka jero haka sai ya isheta da magana, amma shi ko wannan ko kallo bata ishe shi ba, haka suka iso bakin Lecture hall din, Nasiba ta ja ta tsaya, tana kallon yan latti nan suna leke ta window, Rafeek ya taka har gaban kofar ajin da ke kulle ya sa hannu ya kwankwasa.
Daga ciki Mr Wagini ne ke tunanin wani me kasadan ne ya ke kwankwasa mai, bayan shi da hannun shi ya kulle kofar, rai bace yace da na kusa da kofar"open the door" da sauri yaron ya je ya cire sakatar kofar ya bude, idon kowa a kan kofar, so suke su ga mai karfin halin kwankwasa ma Mr. Wagini.
Shigo wa yayi yana tafian nan nashi,ya na bouncing a hankali, ba Matan ba harta mazan sai da su kaji ya burge su, kowa ya shiga tofa albarkacin bakin sa, da yawa za su so Mu'amala ko da ta gaisuwa ce ya hada su da Rafeek, Miemee tayi saurin tabo Ushee "OMG, ga wani Azababbe nan, ya tafi da imani na" Ushee tace "ni baki ji nayi shiru ba? Ai ya hadu ne over, mu dai kalli draman da zasuyi da Wagini".
Har gaban Lecturern yaje, da alamun akwai sanayya tsakanin su, magana suka danyi kafin Rafeek ya juya ya bar Lecture hall din, Nasiba na tsaye inda ya barta, ta gaban ta ya wuce ta bishi da kallon mamaki, shi kuma wannan lafian shi kalau kuwa? Ko be gane ta bane ya wuce ta gaban ta ba tare da ya kalle ta ba? Ko kuma ya na nufin ta bishi ne? Duk a zuci take zancen nan, ba ta gama zancen zuci ba taji ana cewa "Mr Wagini yace duk na waje su shigo aji" da sauri suka fara tururuwar shiga ajin. Wuri ta samu ta zauna ta na tunanin Wannan Bawan Allah me tarin ban mamaki har a ka gama lectures ba ta fahimci komai ba.
Kusan kowa zancen gayen da ya shigo aji dazun suke, wasu suce daga ganin shi dan zafin kai ne, wasu suce ya burgesu, Miemee ta kalli Seebi tace "kinyi missing, ba ki ga wani Azababben guy da ya shigo ji dazun ba" Ushee tace ni abun da ya daure min kai shine, yau Mr wagini yayi abun da be ta bayi ba shine barin late comers su shigo aji, Miemee tace "kuma fa immediately after fitan wannan ne yace ace su shigo" toh ko shi ya rok'i alfarmar abar su su shigo? Miemee tace wane shi? Be yi kama da lecturers ba, yaro ne student kamar mu, da kwai abun da ya kawo shi" kawai muce yau yan kirkin Mr Wagini suna kanshi" Ushee tace "gaskia kam" ta zunguro Seebi da kwata-kwata ba ta tare dasu, tafiya kadai takeyi, Seebi ta dan firgita ta k'akalo murmushi tace "Uhm" cikin zuciyarta kuma tunani take "Is it possible shi ya roke Mr Wagini akan a barsu su shiga?" Meyasa fuskar sa fa ba annuri? Meyasa da ya fito ko kallon ta beyi ba? Meyasa ko sunan ta ya kasa tambaya? Meyasa fuskar sa yake cikin yanayi na damuwa ko rashin walwala ne bata san ya za ta sa abun ba? Tambayoyi da yawa da take bukatar amsoshin su. Haka kurum taji tana son sanin Wanene wannan R-Lema?
Nima biebee nace waye Rafeek Habib Lema??
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg🔟
CAIRO INTERNATIONAL AIRPORT
"Assalam Alaikum, that's my seat" ta dago fararren idanuwan ta ta kalleshi tace "oh sorry" tare da mik'ewa ta rabe ya shige ciki ya zauna itama ta zauna. Wayar shi ya ciro ya kira Alhaji Tijjani Salam Baba gani nan cikin jirgi yanzu zamu tashi" dsga bangaren Alh yace to ya an dace? Habibullah yace "Eh baba, zuwa karshen sati zasu iso" Alh yace toh MashaAllah, Allah ya kawo ku lafiya Amin"
Sanarwa akayi jirgi zai tashi kowa ya sa seat belt dinsa, duk suka yi yanda aka umarta, cikin mintuna kalilan jirgi ya fara yunkurin tashi.
Runste ido ta kusa dashi tayi, da yazo daidai tashi ta yi saurin dafa Habib tare da ririke mai hannu gam, ba yau ta fara hawan jirgi ba, amma Duk sanda jirgi yazo tashi haka take tsintar kanta cikin tsananin tsoro.
Sai da Jirgi ya daidai ta a sararin samaniyya ta dawo hayyacin ta, da sauri ta kalli Habib baki bude, tace "donAllah kayi hakuri, i'm always like this duk sanda jirgi zai daga" Habib ya kalleta baki bude, yace "dama kinajin hausa" ta harareshi cikin sigar wasa tace "wai ma, ga zahiri ka gani"
Habib dai kasa magana yayi, yana satar kallon ta. Kwata-kwata bata yi kama da bahausa ba, tafi kama da larabawa, a hankali ya karance ta; Fara ce sol, mai siririyar fuska, hancinta kamar fensir, tana da dan tsawo, sanye take da bakar Jallabiya ta nade kanta da bakin gyale, kai duk yadda akayi ta hada iri da Larabawa. Tana sane da irin satar kallon ta da yake yi, murmushi kadai tayi ba tace komai ba, ta ciro wani novel daga cikin handbag dinta.
Habi dai ya kasa hakuri sai da ya tanka ta, yace " Erhm, amma ke ba bahaushiya bace ba ko?" ta dan daga kai sama tarw da murmushi tace "bahausa ce mana, bakaji hausa na radam ba amma meyasa kace haka?" yace "anya kuwa ke hausa ce?" kila zama da hausawa ya sa kika iya hausa, ko kadan bakiyi kama da hausa ba kinfi kama da balarabiya" dariya takeyi sosai, tace toh Baba na bahaushe ne gaba da baya mama tace yar kasar lebanon" Habib ya dan tafa hannayen shi biyu, yace "Ahap, ga magana nan ta fito, kin dai hada jini da Larabawan" dariya tayi, haka suka cigaba da fira har suka iso Aminu Kano Airport.
Bayan sun gama Clearance ne suka fito wajen Airport din, Habibullah yace "nan garin kike?" tace "aa, katsina nake" Habib ya zare ido yace "Lah,ashe yar garin mu ce" yace toh zaa zo daukan ki ne? Tace noo ai bama su san yau zan dawo na, i want to make it a suprise" yace "that's nice, toh muje mu yi shatar motar chan" ya fada y na nuna motar kwamkwasiya da sukayi layi a chan gefe, tace "kar ka damu, i can take myself home" ya harareta ba tare da yace mata komai ba ya ja trollyn ta ya yi gaba, bata da zabin da ya wuce ta bishi a baya tana murmushi.
Kafin ta isa har sun daidaita da da mai motar ya sa akwatin ta a booth, Habib ya bude mata baya yace "Bismillah", ba gardama ta shige baya, shi kuma ya bude kofar gaba ya shiga direba ya ja suka dau hanyar Katsinan Dikko dakin kara.
Karfe 8 suka iso, Yace wani unguwa kikayi tace "GRA Bayan gidan Govenor", ya juyo da sauri yana fuskantar ta, yace ai unguwar mu ce, tace wai dagaske? Ya ce eh, to wani gida kike?" tace gidan Alhaji Tijjani Masanawa ai nan Habib ya hangame baki Yace u must be kidding me, Gidan Baba na kike? Itama da mamaki tace "nifa bana son zolaya" yace dagaske ba wasa ba" shine last person da nayi magana da shi a jirgi, Abokin baba na ne sosai, he's like a 2nd father to me and my siblings" tace "banyi mamaki ba, its a small world afterall, yace "haka ne but ya akayi ni ban sanki ba? Tace "da yake a Cairo nayi College zuwa Masters dina, so ban fiye zama a Nigeria ba, ko na zo banyin 1month nake koma wa" Habib yayi mamaki matuk'a yace wai ko kece Aisha?" Tayi murmushi tace ya akayi kasan sunana? Yace ai na kanji baba na waya dake, na taba tambayan shi wacece suke yawan waya?" Yace "kanwarka ce Aisha, tana Misra tana karatu" a haka suka iso Gidan Alhaji Tijjani, wani tangamemen Gida ne, har ciki direba ya shiga dasu.
Habib ya fito ya bude mata ya ciro kayan ta yace" Shatu, Allah ya huta gajia ko?" sunan da ya kira ta dashi ya bata daria, tace "wato ba zaka shigo ba? Ko daman labari ne kawai ka keyi?" yayi darian shima yace mutum da gidansu sai an gayyace shi ciki?" karki damu inaso naje gida na huta, zuwa da safe zanzo ma gaida Baba " tace to shikenan, ta shige gida, shikuma ya koma mota suka fita daga gidan.
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg2⃣0⃣
"Inalillahi wa ina ilaihir rajiun" duk suke fada, Alhaji Habib ya zauna ragajab kan kujera ya dafe kanshi da hannuwan shi, tunani yake me Hafiz yayi haka da aka kulle shi for 10years ba? Zaid yace yaya "meye abunyi?" Habib ya hadiye miyau yace "Zaid, a siyo ticket mu wuce Lagos din kawai, Zaid,yace "Yaya ka bari ni zanje Lagos din gobe da safe" Habib yace shi sam be San wannan ba, tare zasu tafi, nan da nan Zaid yayi waya Chanchangi Airlines ya siya tickets biyu.
Shiru sukayi kamar anyi mutuwa, Rafee'ah ta yanke shirun tace "Abba wanene Hafiz?" Abba ya kasa magana sai Uncle Zaid yace "Yaya na ne, you were too little when he left, i dont think ko Feeq zai ganeshi" Rafeeq yace "na tunashi but i can't remember anything about him" Uncle Zaid yace yeah u were all young then" duk sukayi shiru, kowa da abun da yake sakawa a zuciyar sa, tunanin su daya, me hafix yayi a ka kulle shi har tsawon shekara 10?.
Daga ciki Mr Wagini ne ke tunanin wani me kasadan ne ya ke kwankwasa mai, bayan shi da hannun shi ya kulle kofar, rai bace yace da na kusa da kofar"open the door" da sauri yaron ya je ya cire sakatar kofar ya bude, idon kowa a kan kofar, so suke su ga mai karfin halin kwankwasa ma Mr. Wagini.
Shigo wa yayi yana tafian nan nashi,ya na bouncing a hankali, ba Matan ba harta mazan sai da su kaji ya burge su, kowa ya shiga tofa albarkacin bakin sa, da yawa za su so Mu'amala ko da ta gaisuwa ce ya hada su da Rafeek, Miemee tayi saurin tabo Ushee "OMG, ga wani Azababbe nan, ya tafi da imani na" Ushee tace "ni baki ji nayi shiru ba? Ai ya hadu ne over, mu dai kalli draman da zasuyi da Wagini".
Har gaban Lecturern yaje, da alamun akwai sanayya tsakanin su, magana suka danyi kafin Rafeek ya juya ya bar Lecture hall din, Nasiba na tsaye inda ya barta, ta gaban ta ya wuce ta bishi da kallon mamaki, shi kuma wannan lafian shi kalau kuwa? Ko be gane ta bane ya wuce ta gaban ta ba tare da ya kalle ta ba? Ko kuma ya na nufin ta bishi ne? Duk a zuci take zancen nan, ba ta gama zancen zuci ba taji ana cewa "Mr Wagini yace duk na waje su shigo aji" da sauri suka fara tururuwar shiga ajin. Wuri ta samu ta zauna ta na tunanin Wannan Bawan Allah me tarin ban mamaki har a ka gama lectures ba ta fahimci komai ba.
Kusan kowa zancen gayen da ya shigo aji dazun suke, wasu suce daga ganin shi dan zafin kai ne, wasu suce ya burgesu, Miemee ta kalli Seebi tace "kinyi missing, ba ki ga wani Azababben guy da ya shigo ji dazun ba" Ushee tace ni abun da ya daure min kai shine, yau Mr wagini yayi abun da be ta bayi ba shine barin late comers su shigo aji, Miemee tace "kuma fa immediately after fitan wannan ne yace ace su shigo" toh ko shi ya rok'i alfarmar abar su su shigo? Miemee tace wane shi? Be yi kama da lecturers ba, yaro ne student kamar mu, da kwai abun da ya kawo shi" kawai muce yau yan kirkin Mr Wagini suna kanshi" Ushee tace "gaskia kam" ta zunguro Seebi da kwata-kwata ba ta tare dasu, tafiya kadai takeyi, Seebi ta dan firgita ta k'akalo murmushi tace "Uhm" cikin zuciyarta kuma tunani take "Is it possible shi ya roke Mr Wagini akan a barsu su shiga?" Meyasa fuskar sa fa ba annuri? Meyasa da ya fito ko kallon ta beyi ba? Meyasa ko sunan ta ya kasa tambaya? Meyasa fuskar sa yake cikin yanayi na damuwa ko rashin walwala ne bata san ya za ta sa abun ba? Tambayoyi da yawa da take bukatar amsoshin su. Haka kurum taji tana son sanin Wanene wannan R-Lema?
Nima biebee nace waye Rafeek Habib Lema??
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg🔟
CAIRO INTERNATIONAL AIRPORT
"Assalam Alaikum, that's my seat" ta dago fararren idanuwan ta ta kalleshi tace "oh sorry" tare da mik'ewa ta rabe ya shige ciki ya zauna itama ta zauna. Wayar shi ya ciro ya kira Alhaji Tijjani Salam Baba gani nan cikin jirgi yanzu zamu tashi" dsga bangaren Alh yace to ya an dace? Habibullah yace "Eh baba, zuwa karshen sati zasu iso" Alh yace toh MashaAllah, Allah ya kawo ku lafiya Amin"
Sanarwa akayi jirgi zai tashi kowa ya sa seat belt dinsa, duk suka yi yanda aka umarta, cikin mintuna kalilan jirgi ya fara yunkurin tashi.
Runste ido ta kusa dashi tayi, da yazo daidai tashi ta yi saurin dafa Habib tare da ririke mai hannu gam, ba yau ta fara hawan jirgi ba, amma Duk sanda jirgi yazo tashi haka take tsintar kanta cikin tsananin tsoro.
Sai da Jirgi ya daidai ta a sararin samaniyya ta dawo hayyacin ta, da sauri ta kalli Habib baki bude, tace "donAllah kayi hakuri, i'm always like this duk sanda jirgi zai daga" Habib ya kalleta baki bude, yace "dama kinajin hausa" ta harareshi cikin sigar wasa tace "wai ma, ga zahiri ka gani"
Habib dai kasa magana yayi, yana satar kallon ta. Kwata-kwata bata yi kama da bahausa ba, tafi kama da larabawa, a hankali ya karance ta; Fara ce sol, mai siririyar fuska, hancinta kamar fensir, tana da dan tsawo, sanye take da bakar Jallabiya ta nade kanta da bakin gyale, kai duk yadda akayi ta hada iri da Larabawa. Tana sane da irin satar kallon ta da yake yi, murmushi kadai tayi ba tace komai ba, ta ciro wani novel daga cikin handbag dinta.
Habi dai ya kasa hakuri sai da ya tanka ta, yace " Erhm, amma ke ba bahaushiya bace ba ko?" ta dan daga kai sama tarw da murmushi tace "bahausa ce mana, bakaji hausa na radam ba amma meyasa kace haka?" yace "anya kuwa ke hausa ce?" kila zama da hausawa ya sa kika iya hausa, ko kadan bakiyi kama da hausa ba kinfi kama da balarabiya" dariya takeyi sosai, tace toh Baba na bahaushe ne gaba da baya mama tace yar kasar lebanon" Habib ya dan tafa hannayen shi biyu, yace "Ahap, ga magana nan ta fito, kin dai hada jini da Larabawan" dariya tayi, haka suka cigaba da fira har suka iso Aminu Kano Airport.
Bayan sun gama Clearance ne suka fito wajen Airport din, Habibullah yace "nan garin kike?" tace "aa, katsina nake" Habib ya zare ido yace "Lah,ashe yar garin mu ce" yace toh zaa zo daukan ki ne? Tace noo ai bama su san yau zan dawo na, i want to make it a suprise" yace "that's nice, toh muje mu yi shatar motar chan" ya fada y na nuna motar kwamkwasiya da sukayi layi a chan gefe, tace "kar ka damu, i can take myself home" ya harareta ba tare da yace mata komai ba ya ja trollyn ta ya yi gaba, bata da zabin da ya wuce ta bishi a baya tana murmushi.
Kafin ta isa har sun daidaita da da mai motar ya sa akwatin ta a booth, Habib ya bude mata baya yace "Bismillah", ba gardama ta shige baya, shi kuma ya bude kofar gaba ya shiga direba ya ja suka dau hanyar Katsinan Dikko dakin kara.
Karfe 8 suka iso, Yace wani unguwa kikayi tace "GRA Bayan gidan Govenor", ya juyo da sauri yana fuskantar ta, yace ai unguwar mu ce, tace wai dagaske? Ya ce eh, to wani gida kike?" tace gidan Alhaji Tijjani Masanawa ai nan Habib ya hangame baki Yace u must be kidding me, Gidan Baba na kike? Itama da mamaki tace "nifa bana son zolaya" yace dagaske ba wasa ba" shine last person da nayi magana da shi a jirgi, Abokin baba na ne sosai, he's like a 2nd father to me and my siblings" tace "banyi mamaki ba, its a small world afterall, yace "haka ne but ya akayi ni ban sanki ba? Tace "da yake a Cairo nayi College zuwa Masters dina, so ban fiye zama a Nigeria ba, ko na zo banyin 1month nake koma wa" Habib yayi mamaki matuk'a yace wai ko kece Aisha?" Tayi murmushi tace ya akayi kasan sunana? Yace ai na kanji baba na waya dake, na taba tambayan shi wacece suke yawan waya?" Yace "kanwarka ce Aisha, tana Misra tana karatu" a haka suka iso Gidan Alhaji Tijjani, wani tangamemen Gida ne, har ciki direba ya shiga dasu.
Habib ya fito ya bude mata ya ciro kayan ta yace" Shatu, Allah ya huta gajia ko?" sunan da ya kira ta dashi ya bata daria, tace "wato ba zaka shigo ba? Ko daman labari ne kawai ka keyi?" yayi darian shima yace mutum da gidansu sai an gayyace shi ciki?" karki damu inaso naje gida na huta, zuwa da safe zanzo ma gaida Baba " tace to shikenan, ta shige gida, shikuma ya koma mota suka fita daga gidan.
_Bibilicious Biebee_
👧🏽KE ALHERI CE 🙇🏼♀
NA
BIEBEE ISA
® NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
Pg2⃣0⃣
"Inalillahi wa ina ilaihir rajiun" duk suke fada, Alhaji Habib ya zauna ragajab kan kujera ya dafe kanshi da hannuwan shi, tunani yake me Hafiz yayi haka da aka kulle shi for 10years ba? Zaid yace yaya "meye abunyi?" Habib ya hadiye miyau yace "Zaid, a siyo ticket mu wuce Lagos din kawai, Zaid,yace "Yaya ka bari ni zanje Lagos din gobe da safe" Habib yace shi sam be San wannan ba, tare zasu tafi, nan da nan Zaid yayi waya Chanchangi Airlines ya siya tickets biyu.
Shiru sukayi kamar anyi mutuwa, Rafee'ah ta yanke shirun tace "Abba wanene Hafiz?" Abba ya kasa magana sai Uncle Zaid yace "Yaya na ne, you were too little when he left, i dont think ko Feeq zai ganeshi" Rafeeq yace "na tunashi but i can't remember anything about him" Uncle Zaid yace yeah u were all young then" duk sukayi shiru, kowa da abun da yake sakawa a zuciyar sa, tunanin su daya, me hafix yayi a ka kulle shi har tsawon shekara 10?.