Sashe 98
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Sa'adah ta saki murfin kofar, ta dawo ta zuba mata ido, sai kuma ta sassauta fishinta tace "Da a ce Sa'adatu Kika kira ni da shi, da ko kula ki ba zan yi ba, sai dai na ce miki to, ko da ba zan yi abinda kika ce din ba, sai dan na nuna miki am matured now. Amma tunda Kika 'Kira ni da Gogel zan tabbatar miki har yanzu waccan Gogel din ce dai da kika sani, Billahillazi ki fita a idona, kada ki sake yun'kurin shiga tsakani na da shi, ko ki nuna mini ga yadda zan yi masa, if not kin dai sani. Ba zai zamewa Iyah Basiru komai ba wajen nuna miki har yanzu ina cikin shekarun da ba a mini kan kara ban yi na ice ba".
Daga haka ta juya tana cewa "Zainab zo muje, idan na gama sai mu wuce ba sai na dawo nan ba".
Suka fita bayan Zainab ta cewa Farida Allah ya Kara lafiya.
Sun zo inda su Mk suke zaune, Zainab ta yi masa addu'ar samun lafiya mai dorewa ta yi gaba, haka Abbas ma ya mike suka basu wuri.
Sa'a ta zauna tamkar gaske magana zata yi masa, amma ban da cika tana batsewa ba abin da take yi.
Ta tabbatar Farida na hango su ta windo, shiyasa ma da ta zata zauna sai ta juya baya ta yadda ba zata ga fuskarta, ba haka ma Mk bayansa zata hango.
Banda son ta nunawa Farida dan taki tafiya ba shine dalilin da zata hanata magana da shi ba, da bata tsaya kula Mk ba, tunda agabanta yake nunawa Farida soyayya har ya na lallaba ta.
Dukkansu kowa fishi yake da dan'uwansa, domin ganin ta da ya yi da Khalil ba karamin kidima shi yake yi ba, dan haka, ya danne zuciyar sa ya ki mata magana.
Amma dai a kasan ransa sun bashi dariya ita da Farida kwarai da gaske.
Mintina ashirin na cika ta tashi ga mamakin Mk ya ga ta mi'ke tana murmushi ta fito da wayarta ta Kira Zainab tana fa'din idan Abbas na kusa ki ce masa ya zo mun gama".
Aikuwa sai da Abbas ya zo, ta tafi bata ce da shi uffan ba, sai Abbas ta yiwa sallamah da fatan samun lafiya ga marar lafiya. Mk ya bita da ido yana ganin yadda take tafiya, sai ayyanawa yake yi ko sai yaushe zata daina rikicin gan-gan?
Ban da karfin halin Sa'a ya zata zo ta tarar da mace da mijinta, sannan ta ce sai ya fito waje sun yi magana alhalin ba maganar zata yi ba, kawai son rikici ne da son nunawa Farida karfin da take da shi a zuciyar sa.
A mota Zainab ta ce "Tabdi yau na ga kishi, ashe haka abin yake?"
Sa'a da dama kiris take jira sai kawai ta fashe da kuka.
Jikin Zainab ya yi sanyi sai kuma ta ce "Menene abin kukan kuma? Duk irin jarumtar da Kika yi".
Ta kasa magana illah kukan da ya ki yankewa, tana ta hararo hannun Mk a cikin na wata a gabanta kuma, tabbas har ta mutu ba zata daina kokawa ba.
Da kyar Zainab ta shawo kanta, "kin samu labarin auren Halima next week?"
Murya a dakushe ta ce " a a"
Zainab ta ce "to ai ke ce kinki shiga cikin group din mu na old girls a WhatsApp".
A sanyaye sosai ta ce "Bar ni kin ji, inace ga abin da biyewa 'kawayen ya janyo mini, kina kallon yadda wai magana da Malam ya zama sai an mini iyaka. Ta rushe da kukan da ya sanyaya jikin Zainab, itama idonta ya ciko ta kasa ce mata komai, tana tuki tana taya Sa'adah kuka.
Da kyar Zainab ta shanye kukan ta ce "Ai Halima tana cikin bala'i ke har Safinan ma, domin dai saurayin Halima ya ki aurenta ne adalilin wastewarsu suke yi. Dake akwai alaka tsakanin su da gidan iyayen saurayin shine aka masta masa amma ko kadan babu kwanciyar hankali a tare da ita.
"Ita Kuma Safina har yau dai bata karbi result dinta ba, kiga dai a bayansu da shekaru masu yawa kika shiga makarantar amma kin kammala kin barta".
Aure kuwa shiru kake ji sai dai ana nan ana addu'a. Komai lokaci ne. Amma su kam hakkin kashe aure ne ya saka suka kasa samun nasu auren".
Cikin kuka sosai Sa'a ta ce "Tabbas su Halima sun yi wa rayuwa ta illah, Amma kuma ai da gudunmawata, yarda na yi da su, sannan nima ina da tawa matsalar, bayan wadda suka cusa min, kawai iza mini wutar suke yi, Amma ni na hura abata.
Dan haka na yafe musu, amma bana fatan mua'amala ta sake hadamu, rabona da su tun ina gidan Malam, in sha Allah kuma rabuwarmu kenan domin tarayya da su halaka ce, na rufe babinsu har abada, dan haka kema daina yi mini maganar su".
Zainab ta dinga lallashin Sa'adah da maganganu masu taushi, tana nuna mata, ta yawaita addu'ar sau'kin kishi, itama zata taya ta, sannan yadda ta yi maganar a fita mata da shi waje suyi magana a gadarance, amma ya tashi duk da baya jin da'di ya isa ta gane har gobe ita ke jan ragamar zuciyar sa, sai dai dole ya yiwa Farida adalci domin matarsa ce, dole kuma zai sota.
Zainab ta nisa ta ce "Dan Allah Sa'adah ki 'dore da kyawawan dabi'un ki, kar ki bari kishi ya mayar da ke 'yar gidan jiya, kin san dai yanzu ba ke ka'dai bace, kuma Wallahi duk son da namiji yake yiwa mace indai ta cika kishi da korafi, fita fit take yi a zuciyarsa.
Ke ce uwargida tunda baki yi wani auren ba, dole ki 'dauki hakuri mai yawa. Ki koyi hakuri da juriya, duk yadda kike da mutum kar kiyi zancen abokiyar zamanki da ita mussaman dangin miji, domin duk ranar da abu ya ha'do ku da su, sai sun zayyane mata komai, a hada da sharri ma, daga nan girman ki ya zube a idonta, itama kuma ta sami damar da zata dinga fa'din munanan dabi'un ki".
"Na gode miki Zainab! Na sani ke din mai sona ce ubangiji ya sanya mu cikin masu zumunci dominsa".
Sa'a ta fa'di hakan a sanyaye.
Zainab ta ce "gida zan ajiye ki, ko gidan Anty Sumayya?".
A tunzure ta ce "gidan ubana zaki ajiye Ni, ai Ni da gidanta sai ta neme Ni".
Zainab ta yi shiru! ta san tana tofawa baza su rabu cikin da'din rai ba.
Wasu daga cikin halayyar Sa'a a jinita ne ilimi ko shekaru ba zai sa ta sauya ba, rikici na cikin abin da ba zata daina ba.
A Daren ranar Baba Isa ya dawo asibitin ya fa'dawa Mk ranar juma'ah mai zuwa za'a mayar da aurensa da Sa'adatu, amma ta nemi abarta ta kintsa kafin ayi maganar tariya tunda titsiye ubanta ya yi mata, ba dan tana so ba.
Ya ce " Na kuma yi mata wannan laminin, dan haka ba zata tare ba, sai ta shirya, wannan umarni na ne".
Baban ya nisa ya ce "Soyayya da sanin darajar Dan Adam ne kawai ya sanya Malam Basiru zai sake baka aure a Karo na biyu! Ka sani da ni da mahaifinka ra'ayin mu daya, shawarar mu daya, hakanan neman kudinmu daya, abin da Zan fa'da maka yau, na tabbatar da yana raye a gabansa zan fa'da maka domin ka sani idan ina waje baya ta'ba nuna shine ubanku yana dora ni akan komai nasa matu'kar anan Kano ne, da bashi da dan'uwan jini.
To ka saurare ni da kyau ni na karba maka amanar yarinyar nan, idan har ka bari ta wulakanta ina rantse maka da Allah ni ka wulakanta, na kuma tabbatar idan har ka wulakanta ni, zaka wulakanta Kabiru, hakkin abotarmu ba zai bari ka ga haske ba, ko bayan ba raina, ina maka wasiyya akan yarinyar Malam Basiru domin ni dai banga mai arziki a wannan zamanin irinsa ba, Ubangiji ya bashi wadatar zuciya, ya bashi alheri mai yawa, wadannan kuma sune kololuwar arziki".
Da tsananin farin ciki Mk ya ce "Na ji Baba, in sha Allah ba zan sake kunyata ku ba, komai zata yi zan yi ta ha'kuri, zan kara hakuri akan ha'kuri. Ya sauko ya durkushe a gaban dattijon ya ru'ko hannun sa ya ce " Baba ina maka shaida baka watsar da iyalin amininka ba, har yau din nan da tsufa ya cimma maka sosai, baka huta da yi mana hidima ba. Ina yi maka fatan samun aljannar da Annabi ya yi bishara ga masu kyautatawa iyalan wadda suka rasu".
Jin wannan albishir din ya sake 'karfafawa Mk jiki, domin zuciyarsa ta yi haske. Washagari da safe aka sallame shi.
Ya isa gida bisa rakiyar Dr 'Karfi, tarba na mussaman ya samu daga Farida.
'Karfi bai jima sosai ba ya tafi. Mk ya dinga biyewa Farida na yadda take ina ka saka da shi.
Ya fito wanka ya tarar da ta ajiye masa kaya a bakin gado, gajeran wando ne tiri kwata kalar ruwan 'kasa, sai farar riga ti.shet ya fesa body spray ya sanya kayan da ta riga ta feshe su da turaransa na Versace.
Tawul din da ya dauro, ya dauka ya rataye shi a bandakin, yana fitowa ita kuma ta shigo dauke da tiren kayan abinci.
Yana zaune bakin gado yana kallon yadda ta yi masa shimfida, ta fara zuba masa abincin da ya kasance dankalin turawa da miyar albasa sai gashashiyar kaza, gefe yankakkiyar kankana ce jawur da ita, an lullubeta da ledar rufe abinci.
Sama sama ya ci abincin, ya mayar da hankalinsa wurin shan kankana, ya kalleta ya ce "zanga ranar da zaki daina bani lemo da safe".
Ta mike da sauri tana cewa"wallahi na dafa maka shayin ga su cups nan flask din na manta".
Cikin kankanin lokaci ta kawo masa, da kanta ta zuba masa, tunda ba ma'abocin shan shayi da madara bane.
Bayan ya kammala ta 'ballo masa magungunansa ya sha.
Ya mike ya ce " Bari na sauka na dan kewaya, bana jin ciwo a tare da ni, amma sam jikina babu karfi".
Ta ce "hakan ma babu laifi, ko na dauko maka lucozade it will help".
Daga haka ta juya tana cewa "Zainab zo muje, idan na gama sai mu wuce ba sai na dawo nan ba".
Suka fita bayan Zainab ta cewa Farida Allah ya Kara lafiya.
Sun zo inda su Mk suke zaune, Zainab ta yi masa addu'ar samun lafiya mai dorewa ta yi gaba, haka Abbas ma ya mike suka basu wuri.
Sa'a ta zauna tamkar gaske magana zata yi masa, amma ban da cika tana batsewa ba abin da take yi.
Ta tabbatar Farida na hango su ta windo, shiyasa ma da ta zata zauna sai ta juya baya ta yadda ba zata ga fuskarta, ba haka ma Mk bayansa zata hango.
Banda son ta nunawa Farida dan taki tafiya ba shine dalilin da zata hanata magana da shi ba, da bata tsaya kula Mk ba, tunda agabanta yake nunawa Farida soyayya har ya na lallaba ta.
Dukkansu kowa fishi yake da dan'uwansa, domin ganin ta da ya yi da Khalil ba karamin kidima shi yake yi ba, dan haka, ya danne zuciyar sa ya ki mata magana.
Amma dai a kasan ransa sun bashi dariya ita da Farida kwarai da gaske.
Mintina ashirin na cika ta tashi ga mamakin Mk ya ga ta mi'ke tana murmushi ta fito da wayarta ta Kira Zainab tana fa'din idan Abbas na kusa ki ce masa ya zo mun gama".
Aikuwa sai da Abbas ya zo, ta tafi bata ce da shi uffan ba, sai Abbas ta yiwa sallamah da fatan samun lafiya ga marar lafiya. Mk ya bita da ido yana ganin yadda take tafiya, sai ayyanawa yake yi ko sai yaushe zata daina rikicin gan-gan?
Ban da karfin halin Sa'a ya zata zo ta tarar da mace da mijinta, sannan ta ce sai ya fito waje sun yi magana alhalin ba maganar zata yi ba, kawai son rikici ne da son nunawa Farida karfin da take da shi a zuciyar sa.
A mota Zainab ta ce "Tabdi yau na ga kishi, ashe haka abin yake?"
Sa'a da dama kiris take jira sai kawai ta fashe da kuka.
Jikin Zainab ya yi sanyi sai kuma ta ce "Menene abin kukan kuma? Duk irin jarumtar da Kika yi".
Ta kasa magana illah kukan da ya ki yankewa, tana ta hararo hannun Mk a cikin na wata a gabanta kuma, tabbas har ta mutu ba zata daina kokawa ba.
Da kyar Zainab ta shawo kanta, "kin samu labarin auren Halima next week?"
Murya a dakushe ta ce " a a"
Zainab ta ce "to ai ke ce kinki shiga cikin group din mu na old girls a WhatsApp".
A sanyaye sosai ta ce "Bar ni kin ji, inace ga abin da biyewa 'kawayen ya janyo mini, kina kallon yadda wai magana da Malam ya zama sai an mini iyaka. Ta rushe da kukan da ya sanyaya jikin Zainab, itama idonta ya ciko ta kasa ce mata komai, tana tuki tana taya Sa'adah kuka.
Da kyar Zainab ta shanye kukan ta ce "Ai Halima tana cikin bala'i ke har Safinan ma, domin dai saurayin Halima ya ki aurenta ne adalilin wastewarsu suke yi. Dake akwai alaka tsakanin su da gidan iyayen saurayin shine aka masta masa amma ko kadan babu kwanciyar hankali a tare da ita.
"Ita Kuma Safina har yau dai bata karbi result dinta ba, kiga dai a bayansu da shekaru masu yawa kika shiga makarantar amma kin kammala kin barta".
Aure kuwa shiru kake ji sai dai ana nan ana addu'a. Komai lokaci ne. Amma su kam hakkin kashe aure ne ya saka suka kasa samun nasu auren".
Cikin kuka sosai Sa'a ta ce "Tabbas su Halima sun yi wa rayuwa ta illah, Amma kuma ai da gudunmawata, yarda na yi da su, sannan nima ina da tawa matsalar, bayan wadda suka cusa min, kawai iza mini wutar suke yi, Amma ni na hura abata.
Dan haka na yafe musu, amma bana fatan mua'amala ta sake hadamu, rabona da su tun ina gidan Malam, in sha Allah kuma rabuwarmu kenan domin tarayya da su halaka ce, na rufe babinsu har abada, dan haka kema daina yi mini maganar su".
Zainab ta dinga lallashin Sa'adah da maganganu masu taushi, tana nuna mata, ta yawaita addu'ar sau'kin kishi, itama zata taya ta, sannan yadda ta yi maganar a fita mata da shi waje suyi magana a gadarance, amma ya tashi duk da baya jin da'di ya isa ta gane har gobe ita ke jan ragamar zuciyar sa, sai dai dole ya yiwa Farida adalci domin matarsa ce, dole kuma zai sota.
Zainab ta nisa ta ce "Dan Allah Sa'adah ki 'dore da kyawawan dabi'un ki, kar ki bari kishi ya mayar da ke 'yar gidan jiya, kin san dai yanzu ba ke ka'dai bace, kuma Wallahi duk son da namiji yake yiwa mace indai ta cika kishi da korafi, fita fit take yi a zuciyarsa.
Ke ce uwargida tunda baki yi wani auren ba, dole ki 'dauki hakuri mai yawa. Ki koyi hakuri da juriya, duk yadda kike da mutum kar kiyi zancen abokiyar zamanki da ita mussaman dangin miji, domin duk ranar da abu ya ha'do ku da su, sai sun zayyane mata komai, a hada da sharri ma, daga nan girman ki ya zube a idonta, itama kuma ta sami damar da zata dinga fa'din munanan dabi'un ki".
"Na gode miki Zainab! Na sani ke din mai sona ce ubangiji ya sanya mu cikin masu zumunci dominsa".
Sa'a ta fa'di hakan a sanyaye.
Zainab ta ce "gida zan ajiye ki, ko gidan Anty Sumayya?".
A tunzure ta ce "gidan ubana zaki ajiye Ni, ai Ni da gidanta sai ta neme Ni".
Zainab ta yi shiru! ta san tana tofawa baza su rabu cikin da'din rai ba.
Wasu daga cikin halayyar Sa'a a jinita ne ilimi ko shekaru ba zai sa ta sauya ba, rikici na cikin abin da ba zata daina ba.
A Daren ranar Baba Isa ya dawo asibitin ya fa'dawa Mk ranar juma'ah mai zuwa za'a mayar da aurensa da Sa'adatu, amma ta nemi abarta ta kintsa kafin ayi maganar tariya tunda titsiye ubanta ya yi mata, ba dan tana so ba.
Ya ce " Na kuma yi mata wannan laminin, dan haka ba zata tare ba, sai ta shirya, wannan umarni na ne".
Baban ya nisa ya ce "Soyayya da sanin darajar Dan Adam ne kawai ya sanya Malam Basiru zai sake baka aure a Karo na biyu! Ka sani da ni da mahaifinka ra'ayin mu daya, shawarar mu daya, hakanan neman kudinmu daya, abin da Zan fa'da maka yau, na tabbatar da yana raye a gabansa zan fa'da maka domin ka sani idan ina waje baya ta'ba nuna shine ubanku yana dora ni akan komai nasa matu'kar anan Kano ne, da bashi da dan'uwan jini.
To ka saurare ni da kyau ni na karba maka amanar yarinyar nan, idan har ka bari ta wulakanta ina rantse maka da Allah ni ka wulakanta, na kuma tabbatar idan har ka wulakanta ni, zaka wulakanta Kabiru, hakkin abotarmu ba zai bari ka ga haske ba, ko bayan ba raina, ina maka wasiyya akan yarinyar Malam Basiru domin ni dai banga mai arziki a wannan zamanin irinsa ba, Ubangiji ya bashi wadatar zuciya, ya bashi alheri mai yawa, wadannan kuma sune kololuwar arziki".
Da tsananin farin ciki Mk ya ce "Na ji Baba, in sha Allah ba zan sake kunyata ku ba, komai zata yi zan yi ta ha'kuri, zan kara hakuri akan ha'kuri. Ya sauko ya durkushe a gaban dattijon ya ru'ko hannun sa ya ce " Baba ina maka shaida baka watsar da iyalin amininka ba, har yau din nan da tsufa ya cimma maka sosai, baka huta da yi mana hidima ba. Ina yi maka fatan samun aljannar da Annabi ya yi bishara ga masu kyautatawa iyalan wadda suka rasu".
Jin wannan albishir din ya sake 'karfafawa Mk jiki, domin zuciyarsa ta yi haske. Washagari da safe aka sallame shi.
Ya isa gida bisa rakiyar Dr 'Karfi, tarba na mussaman ya samu daga Farida.
'Karfi bai jima sosai ba ya tafi. Mk ya dinga biyewa Farida na yadda take ina ka saka da shi.
Ya fito wanka ya tarar da ta ajiye masa kaya a bakin gado, gajeran wando ne tiri kwata kalar ruwan 'kasa, sai farar riga ti.shet ya fesa body spray ya sanya kayan da ta riga ta feshe su da turaransa na Versace.
Tawul din da ya dauro, ya dauka ya rataye shi a bandakin, yana fitowa ita kuma ta shigo dauke da tiren kayan abinci.
Yana zaune bakin gado yana kallon yadda ta yi masa shimfida, ta fara zuba masa abincin da ya kasance dankalin turawa da miyar albasa sai gashashiyar kaza, gefe yankakkiyar kankana ce jawur da ita, an lullubeta da ledar rufe abinci.
Sama sama ya ci abincin, ya mayar da hankalinsa wurin shan kankana, ya kalleta ya ce "zanga ranar da zaki daina bani lemo da safe".
Ta mike da sauri tana cewa"wallahi na dafa maka shayin ga su cups nan flask din na manta".
Cikin kankanin lokaci ta kawo masa, da kanta ta zuba masa, tunda ba ma'abocin shan shayi da madara bane.
Bayan ya kammala ta 'ballo masa magungunansa ya sha.
Ya mike ya ce " Bari na sauka na dan kewaya, bana jin ciwo a tare da ni, amma sam jikina babu karfi".
Ta ce "hakan ma babu laifi, ko na dauko maka lucozade it will help".