Sashe 42
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwana uku da suna dan kishiyar Umma ya rasu, daga ciwon ciki kawai sai mutuwa, dole ta tafi, ta taya yar uwarta zama da juyayi! mutuwar matashi akwai gigitarwa.
Kwanaki biyu a jere Inna ke zuwa da safe ta mata wanka da sauran hidima, sai ta mata wankan yamma sannan ta tafi.
Ganin zirga zirgar zata mata yawa kullum, yasa ta roki Baffa ya bari Sa'adah ta zo gida ko sati biyu ne, ta kula ta ita, ita kadai tasan me ta gani, da dukkan alama daki daya suke kwana da mijin ta, tunda Umma ta bar gidan.
Bai tsananta ba, ya amince amma da sharadin idan mijinta bai amince ba, baza'a matsa masa ba.
Tace "Ni ai da iyayensa zan yi magana, idan ka bani dama a daren nan zanje gunsu".
Bai hana ba, itakuma bata yi sanya ba, tana idar da magariba ta tafi gidansu Mk, a falo duk ta same su har Hajiyan Bichi, bata bata lokaci gurin fayyace bu'katar ta ba.
Dukkansu sun yi shiru!sai Hajiya Babba ce ta yi kundunbalar cewa "tunda har kika zo ba za'a hanaki ba, sai dai ki yi hakuri da kaina zan kawo miki ita, idan aka shirya".
Godiya sosai Inna ta yi ,har kofar gida suka rakota suna ta yiwa juna godiya.
Har ta isa gida tana mamaki! ko kishiyoyi nawa ne suka dace da kyakkawan zama irin na iyayen Mk? ko
Ana samun adalar uwargida irin Hajiya Babba, mai hade kan ahalin gida babu banbanci, ko kai sukar wani ga wani, da sauran gutsiritsoma irin na tsofaffin mata masu kitsa munafunci da sunan kishi? Ko
Ana samun amare masu kawaici da biyayya da sanin mutunci da alherin uwayen gida irin Hajiyan Bichi? sha'awar zamansu ya kamata tana jin inama, itama tana da abokiyar zama, ba yabon kai ba, da zata yi koyi da Hajiya Babba.
Da murna ta bawa Baffa labarin yadda suka yi, shi da kansa sai ya zaku Iyah ta dawo kusa da shi duk da dai bai furta ba.
Suna komawa gida, Hajiya Babba ta Kira Mk a waya, ta sanar da shi bu'katar mahaifiyar Sa'adah! ya yi shiru ya rasa mai zaice, jin shirunsa ya tabbatar mata da bai ji dadin maganarta ba, bashi kuma da niyyan amincewa.
Dan haka sai ta kwantar da murya cikin hikima tace " Da na yi karambanin amincewa, har naci alwashin da kaina zan kai musu ita, amma ba zai zama komai ba, idan banyi daidai ba, sai na koma na lashe amai na".
Cikin takaici iri iri yace "Ni bance ba, tunda kin amsa shikenan! amma dai sati daya za ta yi".
"Akan mai zaka 'kayyadewa iyayen ta kwanakin da zata yi a gaban su, ba ka ga mutunci irin nasu ba? neman alfarma suka zo yi gaban iyayenka, saboda girmama hakkin aure. ba dan basa sonta, ko dan sun gaji da ita suka dauketa suka baka ba, yau kusan shekara guda. me zai sa ka shata musu layi dan su nemi su kula da lafiyar yarsu?"
Ya yi shiru yana jin maganar na shigarsa sosai, ya nisa yace "Shikenan Hajiya duk yadda kika yi dai-dai ne"
Dadi ya kamata! ta shiga jero masa addu'ar albarkar ubangiji a dukkan kasafin sa.
"Tunda ka yarda da hukuncin da nayi, duk da ba ka so! Ni kuma zan fada musu sati uku za ta yi maimakon wata guda".
Takaici ya sha'ke masa wuya, wai har sati uku, shi ya dauka anyi wuta ta yi sati biyu, to da fiye da wata ake nufi zata yi ko me?
Sa'adah na zaune a daki tana shayar da Jawad, shi yana falo yana musu guga, ya tattara kayan ya kulle ya kashe iron din saboda yadda jikinsa ya mutu da 'bacin rai.
'
Jiki a mace ya shiga 'dakin bai kalleta ba, ya wuce ya hau gado yana jin zazzabi na namen kama shi.
A gigice ta dinga tambayar sa lafiya kuwa, me ya same shi?
Jinsa shiru yasa ta shimfi'de Jawad! ta isa kusa da shi tana ta'ba jikinsa ta ji ko zazzabi ne yake san'darsa.
Ras ta ji jikinsa, sai rashin kuzari, ta shiga tambayar sa, ya kasa bu'de baki ya mata bayani, amma ganin zata masa kuka, ya fisgota jikinsa ya kankameta, yana sakin ajiyar zuciya.
Tsawon lokaci suna haka, cikin rashin kuzari yace "Tun yanzu na fara kewar ku"
Gabanta ya fadi ta kalleshi ido a bude "Tafiya zaka yi ka barmu?"
Sai kawai ta fara hawaye, ya kalleta yana jin sonta na sake daskarewa a zuciyarsa, shagwabarta, rauninta, soyayyarta na sake gigita shi.
Ya sake kankameta sosai yace " Kune dai za ku tafi ku barni, yanzun nan wayar da kika ji inayi!Hajiya Babba ce, wai na shirya miki tafiya gida, ki yi wankan acan".
Da'di ya cika 'kalbinta! ta ji tamkar ta tashi ta taka rawa, sai kuma ta ga yadda ya shiga damuwa akan tafiyar ta, idan har ta nuna murna! Tamkar ta baro bacin rai a tsakaninsu, dan haka sai ta hadiye dukkan murnar ta!
Ta tattaro dukkan damuwa ta yaba akan fuskarta da jikinta.
Cikin shagwabe fuska har da sake matso hawaye ta hau fadin
" Ni dai ba zan je ba, ai kaima kana kula da mu sosai".
Idan yace bai ji dadin kalamin ta ba yayi karya, ya shiga kissing dinta ba kakkautawa, ganin zai wuce iyaka, yasa ta katse shi, ta lura ya manta da halin da ta ke ciki na rashin tsarki.
Idonsa sunyi ja, sun kankance saboda fitina, ya zuba mata su,ya ce "Hajiya Babba da Innah ne suka zartar da hukuncin nan, hakuri zamu yi, mu yi yadda suke so".
Wani irin farin ciki ya sake kamata, amma a iya zuciyarta ya tsaya, tana jin zumudin sake zama da mahaifanta na taso mata.
Haka suka kwana yana jaddada mata irin kewarta da zai yi, tamkar wadda kasar za ta bari.
Kwanaki biyu a tsakani ta koma gida tare da dukkan abin da za'a bukata, Hajiya Babba ce kuma ta kaita kamar yadda ta yi al'kawari.
Sosai Inna ta ke kula da Sa'adah, wankan rumfu take mata ba tausayi, ga duren kunu, da tuwo, duk ranar da zata mata gardama kuwa cewa take yi " Na lura dakinki kike son komawa, zan 'kira Hajiya ta zo ta mayar da ke, tunda ina tattalinki, kina 'ki! idan kika kufu'de na ga yadda za kiyi rawar jiki akan mijin, ko shi ya yi rawar kai akan ki".
Shiru ta ke yi, kan dole kuma sai ta yi yadda Innar take so.
Jawad ya sami kyakkawan kulawa, kullum safe aka masa wanka ya sha nono, Inna take goya shi, haka zai yini a baya sai anyi azahar yake tashi, cikin 'kan'kanin lokaci ya bundume, kammaninsa da Mk suka bayyana 'karara.
A yini Mk na kiran Sa'adah kamar sau uku koma fiye, koyaushe cikin tambayar lafiyar su, ko yace Babana na kukan dare har yanzu, ko ya tambayi me take so, menene bata da shi, kar fa tace zata dinga 'dorawa Baffa nauyi.
Ire iren tambayar kenan a kullum, itakuma cewa take, komai akwai Uncle. Duka-duka ma yaushe muka zo ne?
Ranar da suka yi kwana biyar, ya je musu.
Ana idar da sallar la'asar ya Isa gidan, a zaure ya tsaya, yana faman kiran wayarta, tana ta ringing amma ba'a dauka ba, ya jingina da bango, yana ri'ke da wayar.
Baffah da yake faman jijjiga Jawad, saboda wankan da Inna ta ke yiwa Sa'adah, kullum ana idar da Sallar la'asar yake dawowa gidan dan ya ri'ke musu shi, su yi wankan, saboda riko da al'adar ba a barin jariri shi ka'dai.😁
Yau sai koke koke yake yi a dalilin cikinsa ya kumburaba a ankara ba, yana sa'be da shi a kafada ya doshi zauren, kwatsam yaga Mukhtar a tsaye.
Cike da girmamawa ya tsugunna ya gaida shi, Baffa sai fadin "ya ka tsaya anan? da ga yau ka dinga shiga kanka tsaye".
Baffah da kansa ya masa jagora har 'dakin Sa'adah yana cewa "wanka suke yi, zauna ka saurare su kadan".
Ya mika masa Jawad tare da fadin "dama so na ke na fita ana jirana za mu je dubiya asibitin Malam".
Cike da kunya ya karbe shi, yana masa godiya.
Baffah na shirin fita Inna ta fito duk ta hada zufa, ta kalle shi, ta ce "kwantar da abokin naka ka yi?"
"A a Babansa ne ya zo, yana gunsa, na shigo da shi, yana dakin Iyah ni fita zanyi, za mu je asibiti mu sake dubo Malam lado".
"Adawo lafiya, shikuma Allah ya bashi lafiya".
Ya fita, yana fadin "Ameen ameen".
Sai da ta sako hijabi sannan ta shiga suka gaisa da Mk, da yake ta fama da Jawad.
Ta karbe shi tana fa'din "Bari a masa wanka kar sanyin yamma ya sauka, ko idan ya ji ruwan dumi zai daina wannan koke koken".
Murmushi kawai ya yi, kansa a kasa, ya bata shi, a zuciyar sa tana jinjina kunyarsa, ko Idris din Sumayya bai kai shi kunya ba.
Yana zaune yana jin kukan wanka da Jawad ya ke tsalawa, jikinsa sai tsuma yake yi, yana jin tamkar ya leko yaronsa ko sabulu ne ya shigar masa ido, amma kawaici ya danne shi.
Ana cikin haka Sa'adah ta shigo da daurin kirji, ta yi mayafi da faffadan tawul.
Mamakin ganinsa a zaune ya daskarar da ita a tsaye.
Da azama tace " Uncle yaushe ka zo?"
"Tun dazu, dan Allah hanzarta ki dubo yaron nan , ki ji har shidewa ya ke yi?"
Ri'ke baki ta yi tare da cewa"oh oh wato Innah tace mini bani da kunya ko?"
"Haka yake da kukan wanka, da angama kuma ya yi ta barci, sai dare zai ishi Inna da kuka".
"Oh barinta ki ke da shi?"
Eh to, shi sai yace ba zai kwanta ba, sai dai a baya! itace kuma mai jure goyon, tace na kwanta na yi barci na huta".
"Amma kuwa dai ba ki da tausayi ko da ya ke, Auta ce ai".
Dariya suka yi a tare, ts shirya cikin doguwar rigar atamfa, irin dinkin masu shayarwa.
Kwanaki biyu a jere Inna ke zuwa da safe ta mata wanka da sauran hidima, sai ta mata wankan yamma sannan ta tafi.
Ganin zirga zirgar zata mata yawa kullum, yasa ta roki Baffa ya bari Sa'adah ta zo gida ko sati biyu ne, ta kula ta ita, ita kadai tasan me ta gani, da dukkan alama daki daya suke kwana da mijin ta, tunda Umma ta bar gidan.
Bai tsananta ba, ya amince amma da sharadin idan mijinta bai amince ba, baza'a matsa masa ba.
Tace "Ni ai da iyayensa zan yi magana, idan ka bani dama a daren nan zanje gunsu".
Bai hana ba, itakuma bata yi sanya ba, tana idar da magariba ta tafi gidansu Mk, a falo duk ta same su har Hajiyan Bichi, bata bata lokaci gurin fayyace bu'katar ta ba.
Dukkansu sun yi shiru!sai Hajiya Babba ce ta yi kundunbalar cewa "tunda har kika zo ba za'a hanaki ba, sai dai ki yi hakuri da kaina zan kawo miki ita, idan aka shirya".
Godiya sosai Inna ta yi ,har kofar gida suka rakota suna ta yiwa juna godiya.
Har ta isa gida tana mamaki! ko kishiyoyi nawa ne suka dace da kyakkawan zama irin na iyayen Mk? ko
Ana samun adalar uwargida irin Hajiya Babba, mai hade kan ahalin gida babu banbanci, ko kai sukar wani ga wani, da sauran gutsiritsoma irin na tsofaffin mata masu kitsa munafunci da sunan kishi? Ko
Ana samun amare masu kawaici da biyayya da sanin mutunci da alherin uwayen gida irin Hajiyan Bichi? sha'awar zamansu ya kamata tana jin inama, itama tana da abokiyar zama, ba yabon kai ba, da zata yi koyi da Hajiya Babba.
Da murna ta bawa Baffa labarin yadda suka yi, shi da kansa sai ya zaku Iyah ta dawo kusa da shi duk da dai bai furta ba.
Suna komawa gida, Hajiya Babba ta Kira Mk a waya, ta sanar da shi bu'katar mahaifiyar Sa'adah! ya yi shiru ya rasa mai zaice, jin shirunsa ya tabbatar mata da bai ji dadin maganarta ba, bashi kuma da niyyan amincewa.
Dan haka sai ta kwantar da murya cikin hikima tace " Da na yi karambanin amincewa, har naci alwashin da kaina zan kai musu ita, amma ba zai zama komai ba, idan banyi daidai ba, sai na koma na lashe amai na".
Cikin takaici iri iri yace "Ni bance ba, tunda kin amsa shikenan! amma dai sati daya za ta yi".
"Akan mai zaka 'kayyadewa iyayen ta kwanakin da zata yi a gaban su, ba ka ga mutunci irin nasu ba? neman alfarma suka zo yi gaban iyayenka, saboda girmama hakkin aure. ba dan basa sonta, ko dan sun gaji da ita suka dauketa suka baka ba, yau kusan shekara guda. me zai sa ka shata musu layi dan su nemi su kula da lafiyar yarsu?"
Ya yi shiru yana jin maganar na shigarsa sosai, ya nisa yace "Shikenan Hajiya duk yadda kika yi dai-dai ne"
Dadi ya kamata! ta shiga jero masa addu'ar albarkar ubangiji a dukkan kasafin sa.
"Tunda ka yarda da hukuncin da nayi, duk da ba ka so! Ni kuma zan fada musu sati uku za ta yi maimakon wata guda".
Takaici ya sha'ke masa wuya, wai har sati uku, shi ya dauka anyi wuta ta yi sati biyu, to da fiye da wata ake nufi zata yi ko me?
Sa'adah na zaune a daki tana shayar da Jawad, shi yana falo yana musu guga, ya tattara kayan ya kulle ya kashe iron din saboda yadda jikinsa ya mutu da 'bacin rai.
'
Jiki a mace ya shiga 'dakin bai kalleta ba, ya wuce ya hau gado yana jin zazzabi na namen kama shi.
A gigice ta dinga tambayar sa lafiya kuwa, me ya same shi?
Jinsa shiru yasa ta shimfi'de Jawad! ta isa kusa da shi tana ta'ba jikinsa ta ji ko zazzabi ne yake san'darsa.
Ras ta ji jikinsa, sai rashin kuzari, ta shiga tambayar sa, ya kasa bu'de baki ya mata bayani, amma ganin zata masa kuka, ya fisgota jikinsa ya kankameta, yana sakin ajiyar zuciya.
Tsawon lokaci suna haka, cikin rashin kuzari yace "Tun yanzu na fara kewar ku"
Gabanta ya fadi ta kalleshi ido a bude "Tafiya zaka yi ka barmu?"
Sai kawai ta fara hawaye, ya kalleta yana jin sonta na sake daskarewa a zuciyarsa, shagwabarta, rauninta, soyayyarta na sake gigita shi.
Ya sake kankameta sosai yace " Kune dai za ku tafi ku barni, yanzun nan wayar da kika ji inayi!Hajiya Babba ce, wai na shirya miki tafiya gida, ki yi wankan acan".
Da'di ya cika 'kalbinta! ta ji tamkar ta tashi ta taka rawa, sai kuma ta ga yadda ya shiga damuwa akan tafiyar ta, idan har ta nuna murna! Tamkar ta baro bacin rai a tsakaninsu, dan haka sai ta hadiye dukkan murnar ta!
Ta tattaro dukkan damuwa ta yaba akan fuskarta da jikinta.
Cikin shagwabe fuska har da sake matso hawaye ta hau fadin
" Ni dai ba zan je ba, ai kaima kana kula da mu sosai".
Idan yace bai ji dadin kalamin ta ba yayi karya, ya shiga kissing dinta ba kakkautawa, ganin zai wuce iyaka, yasa ta katse shi, ta lura ya manta da halin da ta ke ciki na rashin tsarki.
Idonsa sunyi ja, sun kankance saboda fitina, ya zuba mata su,ya ce "Hajiya Babba da Innah ne suka zartar da hukuncin nan, hakuri zamu yi, mu yi yadda suke so".
Wani irin farin ciki ya sake kamata, amma a iya zuciyarta ya tsaya, tana jin zumudin sake zama da mahaifanta na taso mata.
Haka suka kwana yana jaddada mata irin kewarta da zai yi, tamkar wadda kasar za ta bari.
Kwanaki biyu a tsakani ta koma gida tare da dukkan abin da za'a bukata, Hajiya Babba ce kuma ta kaita kamar yadda ta yi al'kawari.
Sosai Inna ta ke kula da Sa'adah, wankan rumfu take mata ba tausayi, ga duren kunu, da tuwo, duk ranar da zata mata gardama kuwa cewa take yi " Na lura dakinki kike son komawa, zan 'kira Hajiya ta zo ta mayar da ke, tunda ina tattalinki, kina 'ki! idan kika kufu'de na ga yadda za kiyi rawar jiki akan mijin, ko shi ya yi rawar kai akan ki".
Shiru ta ke yi, kan dole kuma sai ta yi yadda Innar take so.
Jawad ya sami kyakkawan kulawa, kullum safe aka masa wanka ya sha nono, Inna take goya shi, haka zai yini a baya sai anyi azahar yake tashi, cikin 'kan'kanin lokaci ya bundume, kammaninsa da Mk suka bayyana 'karara.
A yini Mk na kiran Sa'adah kamar sau uku koma fiye, koyaushe cikin tambayar lafiyar su, ko yace Babana na kukan dare har yanzu, ko ya tambayi me take so, menene bata da shi, kar fa tace zata dinga 'dorawa Baffa nauyi.
Ire iren tambayar kenan a kullum, itakuma cewa take, komai akwai Uncle. Duka-duka ma yaushe muka zo ne?
Ranar da suka yi kwana biyar, ya je musu.
Ana idar da sallar la'asar ya Isa gidan, a zaure ya tsaya, yana faman kiran wayarta, tana ta ringing amma ba'a dauka ba, ya jingina da bango, yana ri'ke da wayar.
Baffah da yake faman jijjiga Jawad, saboda wankan da Inna ta ke yiwa Sa'adah, kullum ana idar da Sallar la'asar yake dawowa gidan dan ya ri'ke musu shi, su yi wankan, saboda riko da al'adar ba a barin jariri shi ka'dai.😁
Yau sai koke koke yake yi a dalilin cikinsa ya kumburaba a ankara ba, yana sa'be da shi a kafada ya doshi zauren, kwatsam yaga Mukhtar a tsaye.
Cike da girmamawa ya tsugunna ya gaida shi, Baffa sai fadin "ya ka tsaya anan? da ga yau ka dinga shiga kanka tsaye".
Baffah da kansa ya masa jagora har 'dakin Sa'adah yana cewa "wanka suke yi, zauna ka saurare su kadan".
Ya mika masa Jawad tare da fadin "dama so na ke na fita ana jirana za mu je dubiya asibitin Malam".
Cike da kunya ya karbe shi, yana masa godiya.
Baffah na shirin fita Inna ta fito duk ta hada zufa, ta kalle shi, ta ce "kwantar da abokin naka ka yi?"
"A a Babansa ne ya zo, yana gunsa, na shigo da shi, yana dakin Iyah ni fita zanyi, za mu je asibiti mu sake dubo Malam lado".
"Adawo lafiya, shikuma Allah ya bashi lafiya".
Ya fita, yana fadin "Ameen ameen".
Sai da ta sako hijabi sannan ta shiga suka gaisa da Mk, da yake ta fama da Jawad.
Ta karbe shi tana fa'din "Bari a masa wanka kar sanyin yamma ya sauka, ko idan ya ji ruwan dumi zai daina wannan koke koken".
Murmushi kawai ya yi, kansa a kasa, ya bata shi, a zuciyar sa tana jinjina kunyarsa, ko Idris din Sumayya bai kai shi kunya ba.
Yana zaune yana jin kukan wanka da Jawad ya ke tsalawa, jikinsa sai tsuma yake yi, yana jin tamkar ya leko yaronsa ko sabulu ne ya shigar masa ido, amma kawaici ya danne shi.
Ana cikin haka Sa'adah ta shigo da daurin kirji, ta yi mayafi da faffadan tawul.
Mamakin ganinsa a zaune ya daskarar da ita a tsaye.
Da azama tace " Uncle yaushe ka zo?"
"Tun dazu, dan Allah hanzarta ki dubo yaron nan , ki ji har shidewa ya ke yi?"
Ri'ke baki ta yi tare da cewa"oh oh wato Innah tace mini bani da kunya ko?"
"Haka yake da kukan wanka, da angama kuma ya yi ta barci, sai dare zai ishi Inna da kuka".
"Oh barinta ki ke da shi?"
Eh to, shi sai yace ba zai kwanta ba, sai dai a baya! itace kuma mai jure goyon, tace na kwanta na yi barci na huta".
"Amma kuwa dai ba ki da tausayi ko da ya ke, Auta ce ai".
Dariya suka yi a tare, ts shirya cikin doguwar rigar atamfa, irin dinkin masu shayarwa.