Sashe 111
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ji Sa'adah tana cewa "Ai shikenan tunda ba zaka dinga jin maganar da nake fa'da maka ba, idan wani hutun ka dawo kaga ba nan din na koma gidan Baffah, ai ka zauna dole a inda ya ce maka".
A sanyaye ya jiyo Jawad ya ce "sorry Mami na daina, zan dinga zama, har sai na yi wanka na karya.
Ya hango ta mika masa yatsa tana cewa "promise".
Wato ya miko nasa yatsar su K'ulla al'kawari.
Sai suka tuno masa da rayuwarsu ta baya.
Wannan hutun ba inda Jawad ya je ya kwana, ko gidan Hajiyar Bichi yanzu ya'ki kwana ta dinga yi masa gorin tunda yana ganin uwarsa, shiyasa yanzu baya nemanta tamkar ba shine yake kuka idan ance ba zai kwana a wurinta ba.
Haka hutunsa na sati uku ya qare, Farida da Mk suka mayar da shi.
Sa'adah har ta shirya Mk ya murje idonsa ya ce ta zauna a gida ba zata je ba da Farida zasu tafi.
Har sun shiga mota ya kasa tafiya ya kalli Farida ya ce a minutes please.
Ya nufi side din Sa'a ya tarar da ita zaune a falo ko mayafin bata cire ba.
Ya ru'ko hannuta ya ce "Na kasa tafiya sabaoda baki mana addu'a ba".
Ba tare da ta kalle shi ba ta ce "Ku dawo lafiya".
Ya kirata a tausashe, ta dago suka zubawa juna ido.
"Fishi ki ka yi ko?"
Ta kasa cewa komai.
"Ki yi hakuri! Na sani kina son zuwa, amma tunda da ita muka saba kai shi da zuwa visiting bai kamata yanzu na canja ba, zata dinga jin damuwar rashin haihuwarta, sannan kema wahala zaki yi, tausayin ki nake ji".
Ba walwala a fuskarta ta ce "Na fahimta, sai kun dawo".
Ya yi sukuri ya numfasa ya ce "Then smile".
Ta tura masa baki gaba tabbacin ba maganar murmushi.
Ya dara ka'dan ya ce "Akan 'dan fari kike wannan fishin, ke ko alkunya baki iya ba?"
Ai kuwa nan da nan tasa hannunta ta rufe fuskarta tana fa'din"Bana so Malam " a shagwabe.
Yasa hannu ya bude fusakr sai ta runtse idanuwanta tana murmushi murmurshi, kunya, kunya.
Da haka ya lallaba ya tafi suka rabu k'alau.
Zuwa yanzu hankalin iyaye, da dangin ma'auratan ya kwanta.
Haka Mk yana iyakacin kokarinsa na kamatan adalci na gaskiya a gidansa.
Amma idan ya kebe da Sa'a baya iya mallakar kansa.
Ta bangaren matan nasa sun gamsu Mijjinsu ba munafikin namiji bane, sai dai kowacce tana ganin yana fifita yar'uwarta.
Farida har zuciyarta ta gamsu yana yi mata adalci, amma ta san yafi son Sa'adah, Dan haka take zargin yafi walwala da kuzari ranar girkin Sa'a.
Sa'adah kuwa gani take yi, Mk tsoron Farida yake yi, mussaman yadda yake tirsasa Jawad sai ya zauna a wurinta, sannan yafi fita unguwa da Farida akanta.
Kawai hakuri take ta yi, dan kar ace itace babba sannan itace mai yawan korafi.
A haka rannan sun je gaida Hajiyar Bichi da bata jin da'di, da kyar Mk ya shawo kan Iyah ta yarda su tafi tare, dan kuwa da tace ya tafi da Faridan ita zata je daga baya.
Zuwa wannan lokacin cikinta wata bakwai, ta yi wani irin girma, fuskarta ta fara aunewa, haka baki da hanci tabbacin yadda cikin Jawad ya mayar da ita haka ma wannan zai yi mata.
Farida ta yi matu'kar mamakin yadda ta ga Sa'adah da tsohon ciki, tunda ba kasafai suke haduwa ba.
Wani irin kishi ya shaketa, amma sai ta yi ta addu'a tana namen tsari da yin jayayya a hukuncin Ubangiji.
Kai tsaye Sa'a bayan mota ta shiga, matu'kar zasu fita tare dukkansu, ta sallamawa Farida gaban mota, wanda hakan na matu'kar yiwa Mk da'di.
Duk yadda take boyen cikin sai da Hajiya ta gane Sa'a ta kusa sauka tabbacin da ciki ta tare, tunda basu cika wata hudu da tariyar ba.
Sun dawo gida, maimakon Farida tabi Mk zuwa side dinta, sai kawai ta bi Sa'adah akan ta baata dambun da ta yi, tunda ta ga ta kaiwa Hajiya.
Suka shiga, kamshin wurin yana matu'kar birge Farida amma ba zata iya tambayar wanne irin spices ne mai bada wannan kamshin mai kamawa ba, ga turaren wuta sai kamshin ya hadu ya ba da wani irin kamshi mai kwantar da zuciya.
Duk da cewa side din Farida shima kamshi na mussaman yake yi, amma kamshin wurin Sa'a yafi kwanta mata a rai ko dan kishi ne oho.
Sa'adah ta zauna tana haki, ta ce shiga ki dauko muku ya nan a cikin warmer.
Ta shiga kicin din tana kallon komai, kayan tsilla tsilla amma kuma unique.
Ta fito ta ce "Na gode sosai Gogel".
Takaici ya kama Sa'adah wato Farida ba zata daina yi mata izgili cikin dabara ba.
Ta tuna sunan garin su Farida Torondi, Amma bata ta'ba kiranta da hakan ba, ta tuna yadda yan set dinsu suke ce mata Taller saboda tsayinta, amma ita bata fa'da mata hakan ba.
Ta sake tuna yadda ko Farida bata fa'da a gaban Jawad sai dai Anti! Amma shine ita zata dinga ce mata Gogel, ta tuno har a asibiti ta yi mata kashedi, amma saboda tsokana sai ta sake fa'da.
Ta yi tsaki tana tunanin abin da zata yi mata idan ta sake.
Ai kuwa washagari zata fita wurin aiki ta leko ta kawo mata dish dinta.
Suka gaisa lafiya Lau ta kai kicin ta ajiye mata.
Zata fita ta kalli yadda Sa'a ta zama gari guda.
Ta ce "Gogel indai ba twins bane a cikinki, gaskiya kin kusa sauka, sai dai kuma na ga sai yanzu ne muke shirin four months a gidan nan".
Kafin ta rufe baki Sa'a ta yun'kura ta ce "Idan zaki iya tuna kwanakin da kika yi ba kya ganinsa da rana, ba ya cin abincin ki da rana, to sune kwanakin da aka samu cikin, shi ya yi abinsa bayan an shafa fatiha ba wai shege bane".
Nan da nan Farida ta muzanta ta ce "me ya kawo wannan maganar kuma Gogel?"
Ai kuwa Sa'a ta ce "Tsugudidinki da tsokanarki, ta nunata da yatsa ta ce "Taller ki fita a idona tun muna shaida juna".
Ga mamakin Farida sai ta ji Sunan da Sa'adah ta kirata da shi na Taller ya yi mata zafi ba ka'dan ba.
Idonta ya ciko da 'kwallah ta ce "Sa'adah daga wasa?"
Daidai lokacin Mk ya shigo!
Sa'adah ta ce "ke Kika san wannan, to bana son wasan indai irin wannan ne".
Ai kuwa Farida ta hau hawaye.
Sa'a tana kallonta bata yi mamakin hawayen data fara dan ta ga mijinta ba, da'din abin dai bata isa tasa ya daketa ba.
Ai kuwa Mk ya nemi jin ba'asin kukanta, ta ce Ba komai".
Ta juya ta fita, shima ya bi bayanta, bai yarda ta fita da damuwa ba, sai da yaga ta saki ranta, da kansa ya bude mata kofar mota ta shiga ta zauna, ya rankwafa ta windo yana cewa "drive with care please".
Yayin da zuciyar Sa'a tamkar ta fashe saboda duk tana hangensu ta windo.
Sai da Farida ta tafi sannan ya koma wurin Sa'a ya sameta, ya dinga yi mata sababi akan ta zo wurinta ne zata wulakantata har ta sakata kuka, har yana fa'din ke baki san halin Farida da son raha ba, ki dinga jin tausayinta mana".
Ba'kin cikinsa yana neman kassarata.
Ta hadiye kukan ta ce "Ai yanzu na gama ganeka, ita bata laifi, komai ta yi daidai ne, kome take so haka zaka yi mata, saboda ita din Babanta zai siya mata kowanne irin miji".
Ai kuwa ya hassalo yana fa'din "wulakanci ki ya tashi ba? Ni kika fa'dawa wannan maganar?"
Ta kasa magana saboda a yanzu shakkarsa take ji sosai, ba kamar da ba, hawaye ya balle mata.
"Ta ce ta zo har 'dakina ta tsokane ni, bayan ka san har fa'da maka na yi akan ka yi mata togaciya, amma ba bincike ba komai, ka bi bayanta, ka rarrasheta, ni kuma ka zo kana mini jidali".
"Jikinsa ya yi sanyi, fishinsa ya sauka, ya isa gareta da nufin rungumeta, ta goce ta ce "Tun bamu je ko ina ba kana son sai na gaza".
Ya sassauta murya ya ce "Tausayinta nake ji, bata da lafiya sosai, bata samu haihuwa ba, sannan na fi son wata akanta, fa'da mini dan Allah bata cancanci a ririta farin-cikinta ba?"
Ta zuba masa ido ta ce "Ban son wannan tausayin da ka tsananta akanta, ina jin fargabar abin da nake gani a idanuwanka akan lamarinta".
"Ni meyasa baka jin tausayi na irin haka?"
Ba ja in ja ya ce "Ina tsananin sonki Ubangiji ne shaida, kina da cikakkiyar lafiya, Ubangiji ya hore miki, kina haihuwa Ubangiji ya arzurtaki, Ubangiji ya arzurtaki da mahaifin da ba kowanne 'da ne yake samun irinsa ba.
Fa'da mini ta inda baki kereta ba".
Ya ru'ko ta, tana cigaba da kuka tana cewa "Allah ka bawa Farida haihuwa ko wannan tausayin da yake neman zame mini barazana ya yi sau'ki".
Haka ya lallabata.
Haka da Farida ta dawo, ya ja kunnanta da cewa "da bakin ki, kin ta'ba cemin kina fakar idon mutane kina tsokanarta, to ki bari tunda bata so, Nima bana so, ki kiyaye bana son muna samun sabani".
Ta tsiri fishi! Ya tattara ya watsa da ita, ya shareta, dake bame yawan fishin bace da kanta kuma ta dawo hanya.
Haka rayuwar take gudana yau fari gobe tsumma kowa ha'kuri yake yi da abin da rayuwa ta zaba masa.
A haka Allah ya sauki Sa'adah lafiya! Ta haifi danta lafiyayye mai kama da Jawad sak, kenan Mk shima ya biyo.
Kwananta'daya a asibiti aka sallamota bayan an tabbatar da lafiyarta da ta jariri.
Tana zaune a dakinta ta tsurawa jaririn ido tana ayyana abubuwa masu yawa, bai zo da wuri ba a lokacin da Mk ya matsu ta haihu, haka bai yarda ya fito a jikin Farida ba, bai kuma fito a jikin wani namijin ba, tabbas kudurar Ubangiji yawa ne da ita, duk tsawon shekarun nan sai da ya jira ya fito ta tsatsonsu a lokacin da ba a yi zato ba, Wannan ka'dai ya isa aya ga mai hankali.
A sanyaye ya jiyo Jawad ya ce "sorry Mami na daina, zan dinga zama, har sai na yi wanka na karya.
Ya hango ta mika masa yatsa tana cewa "promise".
Wato ya miko nasa yatsar su K'ulla al'kawari.
Sai suka tuno masa da rayuwarsu ta baya.
Wannan hutun ba inda Jawad ya je ya kwana, ko gidan Hajiyar Bichi yanzu ya'ki kwana ta dinga yi masa gorin tunda yana ganin uwarsa, shiyasa yanzu baya nemanta tamkar ba shine yake kuka idan ance ba zai kwana a wurinta ba.
Haka hutunsa na sati uku ya qare, Farida da Mk suka mayar da shi.
Sa'adah har ta shirya Mk ya murje idonsa ya ce ta zauna a gida ba zata je ba da Farida zasu tafi.
Har sun shiga mota ya kasa tafiya ya kalli Farida ya ce a minutes please.
Ya nufi side din Sa'a ya tarar da ita zaune a falo ko mayafin bata cire ba.
Ya ru'ko hannuta ya ce "Na kasa tafiya sabaoda baki mana addu'a ba".
Ba tare da ta kalle shi ba ta ce "Ku dawo lafiya".
Ya kirata a tausashe, ta dago suka zubawa juna ido.
"Fishi ki ka yi ko?"
Ta kasa cewa komai.
"Ki yi hakuri! Na sani kina son zuwa, amma tunda da ita muka saba kai shi da zuwa visiting bai kamata yanzu na canja ba, zata dinga jin damuwar rashin haihuwarta, sannan kema wahala zaki yi, tausayin ki nake ji".
Ba walwala a fuskarta ta ce "Na fahimta, sai kun dawo".
Ya yi sukuri ya numfasa ya ce "Then smile".
Ta tura masa baki gaba tabbacin ba maganar murmushi.
Ya dara ka'dan ya ce "Akan 'dan fari kike wannan fishin, ke ko alkunya baki iya ba?"
Ai kuwa nan da nan tasa hannunta ta rufe fuskarta tana fa'din"Bana so Malam " a shagwabe.
Yasa hannu ya bude fusakr sai ta runtse idanuwanta tana murmushi murmurshi, kunya, kunya.
Da haka ya lallaba ya tafi suka rabu k'alau.
Zuwa yanzu hankalin iyaye, da dangin ma'auratan ya kwanta.
Haka Mk yana iyakacin kokarinsa na kamatan adalci na gaskiya a gidansa.
Amma idan ya kebe da Sa'a baya iya mallakar kansa.
Ta bangaren matan nasa sun gamsu Mijjinsu ba munafikin namiji bane, sai dai kowacce tana ganin yana fifita yar'uwarta.
Farida har zuciyarta ta gamsu yana yi mata adalci, amma ta san yafi son Sa'adah, Dan haka take zargin yafi walwala da kuzari ranar girkin Sa'a.
Sa'adah kuwa gani take yi, Mk tsoron Farida yake yi, mussaman yadda yake tirsasa Jawad sai ya zauna a wurinta, sannan yafi fita unguwa da Farida akanta.
Kawai hakuri take ta yi, dan kar ace itace babba sannan itace mai yawan korafi.
A haka rannan sun je gaida Hajiyar Bichi da bata jin da'di, da kyar Mk ya shawo kan Iyah ta yarda su tafi tare, dan kuwa da tace ya tafi da Faridan ita zata je daga baya.
Zuwa wannan lokacin cikinta wata bakwai, ta yi wani irin girma, fuskarta ta fara aunewa, haka baki da hanci tabbacin yadda cikin Jawad ya mayar da ita haka ma wannan zai yi mata.
Farida ta yi matu'kar mamakin yadda ta ga Sa'adah da tsohon ciki, tunda ba kasafai suke haduwa ba.
Wani irin kishi ya shaketa, amma sai ta yi ta addu'a tana namen tsari da yin jayayya a hukuncin Ubangiji.
Kai tsaye Sa'a bayan mota ta shiga, matu'kar zasu fita tare dukkansu, ta sallamawa Farida gaban mota, wanda hakan na matu'kar yiwa Mk da'di.
Duk yadda take boyen cikin sai da Hajiya ta gane Sa'a ta kusa sauka tabbacin da ciki ta tare, tunda basu cika wata hudu da tariyar ba.
Sun dawo gida, maimakon Farida tabi Mk zuwa side dinta, sai kawai ta bi Sa'adah akan ta baata dambun da ta yi, tunda ta ga ta kaiwa Hajiya.
Suka shiga, kamshin wurin yana matu'kar birge Farida amma ba zata iya tambayar wanne irin spices ne mai bada wannan kamshin mai kamawa ba, ga turaren wuta sai kamshin ya hadu ya ba da wani irin kamshi mai kwantar da zuciya.
Duk da cewa side din Farida shima kamshi na mussaman yake yi, amma kamshin wurin Sa'a yafi kwanta mata a rai ko dan kishi ne oho.
Sa'adah ta zauna tana haki, ta ce shiga ki dauko muku ya nan a cikin warmer.
Ta shiga kicin din tana kallon komai, kayan tsilla tsilla amma kuma unique.
Ta fito ta ce "Na gode sosai Gogel".
Takaici ya kama Sa'adah wato Farida ba zata daina yi mata izgili cikin dabara ba.
Ta tuna sunan garin su Farida Torondi, Amma bata ta'ba kiranta da hakan ba, ta tuna yadda yan set dinsu suke ce mata Taller saboda tsayinta, amma ita bata fa'da mata hakan ba.
Ta sake tuna yadda ko Farida bata fa'da a gaban Jawad sai dai Anti! Amma shine ita zata dinga ce mata Gogel, ta tuno har a asibiti ta yi mata kashedi, amma saboda tsokana sai ta sake fa'da.
Ta yi tsaki tana tunanin abin da zata yi mata idan ta sake.
Ai kuwa washagari zata fita wurin aiki ta leko ta kawo mata dish dinta.
Suka gaisa lafiya Lau ta kai kicin ta ajiye mata.
Zata fita ta kalli yadda Sa'a ta zama gari guda.
Ta ce "Gogel indai ba twins bane a cikinki, gaskiya kin kusa sauka, sai dai kuma na ga sai yanzu ne muke shirin four months a gidan nan".
Kafin ta rufe baki Sa'a ta yun'kura ta ce "Idan zaki iya tuna kwanakin da kika yi ba kya ganinsa da rana, ba ya cin abincin ki da rana, to sune kwanakin da aka samu cikin, shi ya yi abinsa bayan an shafa fatiha ba wai shege bane".
Nan da nan Farida ta muzanta ta ce "me ya kawo wannan maganar kuma Gogel?"
Ai kuwa Sa'a ta ce "Tsugudidinki da tsokanarki, ta nunata da yatsa ta ce "Taller ki fita a idona tun muna shaida juna".
Ga mamakin Farida sai ta ji Sunan da Sa'adah ta kirata da shi na Taller ya yi mata zafi ba ka'dan ba.
Idonta ya ciko da 'kwallah ta ce "Sa'adah daga wasa?"
Daidai lokacin Mk ya shigo!
Sa'adah ta ce "ke Kika san wannan, to bana son wasan indai irin wannan ne".
Ai kuwa Farida ta hau hawaye.
Sa'a tana kallonta bata yi mamakin hawayen data fara dan ta ga mijinta ba, da'din abin dai bata isa tasa ya daketa ba.
Ai kuwa Mk ya nemi jin ba'asin kukanta, ta ce Ba komai".
Ta juya ta fita, shima ya bi bayanta, bai yarda ta fita da damuwa ba, sai da yaga ta saki ranta, da kansa ya bude mata kofar mota ta shiga ta zauna, ya rankwafa ta windo yana cewa "drive with care please".
Yayin da zuciyar Sa'a tamkar ta fashe saboda duk tana hangensu ta windo.
Sai da Farida ta tafi sannan ya koma wurin Sa'a ya sameta, ya dinga yi mata sababi akan ta zo wurinta ne zata wulakantata har ta sakata kuka, har yana fa'din ke baki san halin Farida da son raha ba, ki dinga jin tausayinta mana".
Ba'kin cikinsa yana neman kassarata.
Ta hadiye kukan ta ce "Ai yanzu na gama ganeka, ita bata laifi, komai ta yi daidai ne, kome take so haka zaka yi mata, saboda ita din Babanta zai siya mata kowanne irin miji".
Ai kuwa ya hassalo yana fa'din "wulakanci ki ya tashi ba? Ni kika fa'dawa wannan maganar?"
Ta kasa magana saboda a yanzu shakkarsa take ji sosai, ba kamar da ba, hawaye ya balle mata.
"Ta ce ta zo har 'dakina ta tsokane ni, bayan ka san har fa'da maka na yi akan ka yi mata togaciya, amma ba bincike ba komai, ka bi bayanta, ka rarrasheta, ni kuma ka zo kana mini jidali".
"Jikinsa ya yi sanyi, fishinsa ya sauka, ya isa gareta da nufin rungumeta, ta goce ta ce "Tun bamu je ko ina ba kana son sai na gaza".
Ya sassauta murya ya ce "Tausayinta nake ji, bata da lafiya sosai, bata samu haihuwa ba, sannan na fi son wata akanta, fa'da mini dan Allah bata cancanci a ririta farin-cikinta ba?"
Ta zuba masa ido ta ce "Ban son wannan tausayin da ka tsananta akanta, ina jin fargabar abin da nake gani a idanuwanka akan lamarinta".
"Ni meyasa baka jin tausayi na irin haka?"
Ba ja in ja ya ce "Ina tsananin sonki Ubangiji ne shaida, kina da cikakkiyar lafiya, Ubangiji ya hore miki, kina haihuwa Ubangiji ya arzurtaki, Ubangiji ya arzurtaki da mahaifin da ba kowanne 'da ne yake samun irinsa ba.
Fa'da mini ta inda baki kereta ba".
Ya ru'ko ta, tana cigaba da kuka tana cewa "Allah ka bawa Farida haihuwa ko wannan tausayin da yake neman zame mini barazana ya yi sau'ki".
Haka ya lallabata.
Haka da Farida ta dawo, ya ja kunnanta da cewa "da bakin ki, kin ta'ba cemin kina fakar idon mutane kina tsokanarta, to ki bari tunda bata so, Nima bana so, ki kiyaye bana son muna samun sabani".
Ta tsiri fishi! Ya tattara ya watsa da ita, ya shareta, dake bame yawan fishin bace da kanta kuma ta dawo hanya.
Haka rayuwar take gudana yau fari gobe tsumma kowa ha'kuri yake yi da abin da rayuwa ta zaba masa.
A haka Allah ya sauki Sa'adah lafiya! Ta haifi danta lafiyayye mai kama da Jawad sak, kenan Mk shima ya biyo.
Kwananta'daya a asibiti aka sallamota bayan an tabbatar da lafiyarta da ta jariri.
Tana zaune a dakinta ta tsurawa jaririn ido tana ayyana abubuwa masu yawa, bai zo da wuri ba a lokacin da Mk ya matsu ta haihu, haka bai yarda ya fito a jikin Farida ba, bai kuma fito a jikin wani namijin ba, tabbas kudurar Ubangiji yawa ne da ita, duk tsawon shekarun nan sai da ya jira ya fito ta tsatsonsu a lokacin da ba a yi zato ba, Wannan ka'dai ya isa aya ga mai hankali.