Sashe 30
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
45-46
Tana shiga zauren gidan ta fito da hijab ta sanya, sukuku ta shiga gidan. A tsakar gidan ta sami iyayenta. Tsoron da ke cikin zuciyarta ya sake bayyana a fuskarta da jikinta.
Baffa ne kawai ya amsa sallamar, da 'kyar ta tsugunna ta gaishe shi, ya amsa ba sakin fuska, ya kalle ta fuska ba wasa ya ce, "Daga ina ki ke?"
Cikin rawar murya irin ta rashin gaskiya ta ce, "Zainab na raka gidan yayarta kuma sai da na tambayi Inna."
A kufule Inna ta ce, "Tabbas kin tambaye ni amma ce mini kika yi ba za ku dade ba, don haka na gode miki da cika al'kawari."
Ganin yadda ran Inna ya baci sosai sai shi kuma ya sassauta, ya mata nasiha tare da cewa, "yarinyar kirki in dai ta san kanta, killace kanta take yi a gida, bai kamata dare ya riske ta a waje ba."
Har ya sallame ta sai kuma ya ce, "Yawwa dama zan fada miki, aurenki bayan sallah za a yi, nan da wata uku kenan.
Bayan haka kuma na sanar da iyayen yaron cewar kar ya yi lefe, ni ma kuma ba zan wahalar da kaina wurin saya masa kayan daki ba, ke zan ba shi ina kuma da yakinin na miki tarbiyar da zai sami nutsuwa da ke. Uwarki kuma ta koya miki yadda zai yi alfahari da ke a matsayin uwar yayansa. Haka na yi wa Sumayya har yau din nan da ta kai shekaru goma a dakinta ban taba jin ance mini ga wani abu na kaico daga gare ta ba, mijinta kullum kara girmama mu yake yi, Ina fatan ki yi koyi da ita, Tashi ki je."
Ta mike ta wuce dakinta cikin wani irin yanayi, tana zuwa ta fadi kasa ta fara kuka kasa-kasa, tana jin karshen tozarci an yi mata.
Ta ya ya za a dinga hada Sumayya da ita, ai ba lokacin su daya ba, sannan ba iyayen mijinsu daya ba, a wannan zamanin ma an kai yarinya da kayan daki idan ba na alfarma ba ne, dangin miji suna yi wa yarinyar izgili da habaici, to ina kuma ita da za a kai ta tsurarta? Wanne irin raini da kaskanci za a janyo mata? Ba'kin cikinta ya ninku ta rasa inda za ta tsoma ranta.
Ashe shi yasa MK yake mata gadara da isa, saboda an nuna masa sadaka za a ba shi an dauke masa lefe? Shima kuma kar ya sa rai za a je a yi masa jere. Ba ta san lokacin da ta bude murya ta dinga zunduma ihu ba.
Daga Inna har Baffa a kidime suka mike suna rige-rigen isa dakinta a tuninsu wani abin tsoro ne a dakin, ko maciji ko kunama ta harbeta.
Sai dai ganin ta ras illah kukan da ta bare baki tana yin sa tamkar yarinya yar karama yasa suka yi cirko-cirko! Baffa ne ya ce, "Mene ne ya saki wannan ihun sai ka ce wacce ba ta zuwa Islamiyya, ba za ki ambaci Allah ba! Sai ki cika mana kunne da kuka har da ihu?"
Cikin kuka sosai ta ce, "Ka taimake ni Baffa! kar ka kai ni ba kayan daki wallahi gori za a yi mini, ko a yi ta zunden sadaka ta ka bayar." Ta karasa cikin gunjin kuka.
A zuciye Inna ta ce, "Watau ke ba za ki bi shi ba, sai shi ne zai bi ra'ayinki, ke kullum sai an yi artabu da ke? Kin taba ganin wanda ya bi iyayensa bai ci ribar rayuwarsa ba? Ashe ba za ki koyi da yayar ki ba?"
Ta sake kara sautin kukan ta ce, "Ai samun irin mijinta da yan'uwansa sai an tona a wannan lokacin, sannan kuma ni da ita akwai banbanci."
Takaicin ta ya kama Inna ta ce, "Banbanci kuwa a bayyane, ita ta yarda duk talaucinmu, mu ne iyayenta, za mu yi iko a kanta ba tare da ta ga gidadancinmu ba, sannan karatu kadan ta yi amma mai cike da ladabi da biyayya, in sha Allah Ubangiji ba zai kunyata ta ba."
Tana fadin hakan ta fita ta bar su da Baffa.
"Iyah!" Ya kira ta da muryar da bai saba mata irin ta ba, tunda shi kullum a cikin lallashi da tausasawa yake mata magana.
"Na riga da na zartar da maganar nan a gaban Mutari da iyayensa, ba zan koma na ce na fasa ba. Ko a fuska kika nunawa yaron nan tsarina bai miki ba, ki tabbatar kin nuna ban isa da ke ba, ba kuma zan sake yin iko akan ki ba."
Ya na rufe baki ya juya shi ma ya fice abinsa, sai ji ta yi kukan ya tsaya mata cak!
Amma wani irin ba'kin ciki take ji ya shake mata wuya da zuciya. Da 'kyar ta fita ta yi alwala ta yi sallar Maghrib da Isha wanda ba nutsuwa a cikinsu.
Da rarrafe ta isa kan shimfidarta, hawaye na bin fuskarta, ta ya ya za a mata irin wannan auren sai ka ce mutanen da? Ai ko shi Baffan da zai auri Innarsu, ya mata hidima, ita ma kuma da kayan dakinta aka kawo masa ita har yanzu gadonta na aure ne a dakin, duk kuwa da auren zumunci aka musu, shekaru kusan talatin. Amma sai ita a wannan lokacin za a mata irin wannan auren, kuka ya sake balle mata.😭
Tsawon lokaci tana kuka har kanta ya fara ciwo, a ranar dai ba ta yi wani cikakken barci ba, ba ta tuna matsalarta da MK ba sai da Asuba.
Tana idar da sallah ta ciro wayarta a caji ta lalubo lambar MK ta kira, har ta katse bai dauka ba, ta kira ya fi sau biyar amma bai amsa ba. ta ja wani dogon tsaki tana furta "Sai ka yi ta yi."
Ta kwanta ta yi shiru, amma sai ta kasa hakuri, ta sake kiran sa, nan ma bai dauka ba, ta yi ta kira har ta gaji, takaici ya sa ta yi jifa da wayar.
Har rana ta fito tana kwance ta ki fita, fishi sosai take yi, ga idanuwanta sun kunbura saboda tsabar kuka.
Inna kuwa ko ta kanta ba ta bi ba, ta yi dukkan ayyukanta, ta yi abin karin kumallo suka karya da Baffa amma ba ta nemi Iyah ba bare ta ba ta.
Sai da Baffa zai fita ne ya tsaya bakin kofar dakinta ya kira ta. Ta fito sanye da hijabi duk fuskar ta a kumbure, ta tsugunna ta gaishe shi, ya kalle ta cike da kulawa ya ce, "Iyata yau ban ji motsin ki ba ga shi har zan fita, kin san idan ban gan ki ba yini zan yi ba kuzari".
Ta sake yin kasa da kanta hawaye na cika mata ido, "maza fito ki yi wanka, ki sami abinci ki ci idan zan dawo zan taho miki da indomie har da Sadine na gwangwani, da ma kwanaki kin ce mini indominki ta 'kare, yau zan sayo miki ki ajiye a dakinki har da madara."
Cikin kuka ta ce, "Na gode"
Ya tafi yana jin kukan ta har cikin ransa, ya na raya yadda Sumayya ta zarta ta biyayya da gudun zuciya amma Iyah tafi shiga ransa matu'ka da gaske.
Ko da ta koma dakin sai ta sake dasa sabon kuka mai cike da kururuwa, yin sa take iya karfinta, fishin da MK ya dauka ya sake dagula mata lissafi.
Tun Inna na danne bacin ran ihun da Sa'adah ta cika mata kunne da shi, har ta kasa jurewa.
Don haka ta shiga 'daki ta samo wani danko mai kauri ta nada a hannunta, ta nufi dakinta, tana shiga kuwa ba bata lokaci ta shiga zabga matata ko ina, da iyakacin karfinta, da kyar Sa'adah ta kwace ta fice a guje, ta nufi hanyar zaure ta tsaya tana kuka sosai.
Ta dade kafin ta dawo gidan, tana rabe-rabe, Inna ta kalle ta rai a bace ta ce, " Idan kin san za ki ta sani a gaba kina mini kukan iyashege ki juya ki tafi duk inda za ki shiga, watau ni kika raina? Kin ga Baffanku ya fita shine za ki 'bude mini wannan ja'irin bakin naki da bai iya komai ba sai 'kulla karya da munafunci kina mini ihu. Wai har kin yi wayon da yafi nawa, ni za ki yiwa karyar Zainab za ki raka unguwa? Ashe da wannan shedanun kawayen naki masu yi wa Babba kallon raini kuka fita, har kin yi lalacewar da za ki shiga gaban motar namiji ya kawo ki har kofar gidanku, ki fito akan idon jama'a, oh ni Salamatu wacce irin yarinya nake tare da ita ne haka?"
Ta Fadi hakan tare da tafa hannu tana salati.
"Wai kuma don ki bata ni a gunsa shi ne zaki ce nasan zaki fita, to don uwarki daga yau kika kuskura kika ce mini za ki fita da sunan zuwa unguwa wallahi sai jikin ki ya fa'da miki. Na daina raga miki tunda ke rarrashi baya bi da ke, kafin nan kafin ki bar gidan nan sai na miki tabbuna ba ma tabo ba. Tunda nake da Baffanku bai taba ganin kasawa ta ba sai akan ki, jiya da daddare ba abin da bai fada mini ba, bayan an tabbatar masa a mota aka kawo ki."
45-46
Tana shiga zauren gidan ta fito da hijab ta sanya, sukuku ta shiga gidan. A tsakar gidan ta sami iyayenta. Tsoron da ke cikin zuciyarta ya sake bayyana a fuskarta da jikinta.
Baffa ne kawai ya amsa sallamar, da 'kyar ta tsugunna ta gaishe shi, ya amsa ba sakin fuska, ya kalle ta fuska ba wasa ya ce, "Daga ina ki ke?"
Cikin rawar murya irin ta rashin gaskiya ta ce, "Zainab na raka gidan yayarta kuma sai da na tambayi Inna."
A kufule Inna ta ce, "Tabbas kin tambaye ni amma ce mini kika yi ba za ku dade ba, don haka na gode miki da cika al'kawari."
Ganin yadda ran Inna ya baci sosai sai shi kuma ya sassauta, ya mata nasiha tare da cewa, "yarinyar kirki in dai ta san kanta, killace kanta take yi a gida, bai kamata dare ya riske ta a waje ba."
Har ya sallame ta sai kuma ya ce, "Yawwa dama zan fada miki, aurenki bayan sallah za a yi, nan da wata uku kenan.
Bayan haka kuma na sanar da iyayen yaron cewar kar ya yi lefe, ni ma kuma ba zan wahalar da kaina wurin saya masa kayan daki ba, ke zan ba shi ina kuma da yakinin na miki tarbiyar da zai sami nutsuwa da ke. Uwarki kuma ta koya miki yadda zai yi alfahari da ke a matsayin uwar yayansa. Haka na yi wa Sumayya har yau din nan da ta kai shekaru goma a dakinta ban taba jin ance mini ga wani abu na kaico daga gare ta ba, mijinta kullum kara girmama mu yake yi, Ina fatan ki yi koyi da ita, Tashi ki je."
Ta mike ta wuce dakinta cikin wani irin yanayi, tana zuwa ta fadi kasa ta fara kuka kasa-kasa, tana jin karshen tozarci an yi mata.
Ta ya ya za a dinga hada Sumayya da ita, ai ba lokacin su daya ba, sannan ba iyayen mijinsu daya ba, a wannan zamanin ma an kai yarinya da kayan daki idan ba na alfarma ba ne, dangin miji suna yi wa yarinyar izgili da habaici, to ina kuma ita da za a kai ta tsurarta? Wanne irin raini da kaskanci za a janyo mata? Ba'kin cikinta ya ninku ta rasa inda za ta tsoma ranta.
Ashe shi yasa MK yake mata gadara da isa, saboda an nuna masa sadaka za a ba shi an dauke masa lefe? Shima kuma kar ya sa rai za a je a yi masa jere. Ba ta san lokacin da ta bude murya ta dinga zunduma ihu ba.
Daga Inna har Baffa a kidime suka mike suna rige-rigen isa dakinta a tuninsu wani abin tsoro ne a dakin, ko maciji ko kunama ta harbeta.
Sai dai ganin ta ras illah kukan da ta bare baki tana yin sa tamkar yarinya yar karama yasa suka yi cirko-cirko! Baffa ne ya ce, "Mene ne ya saki wannan ihun sai ka ce wacce ba ta zuwa Islamiyya, ba za ki ambaci Allah ba! Sai ki cika mana kunne da kuka har da ihu?"
Cikin kuka sosai ta ce, "Ka taimake ni Baffa! kar ka kai ni ba kayan daki wallahi gori za a yi mini, ko a yi ta zunden sadaka ta ka bayar." Ta karasa cikin gunjin kuka.
A zuciye Inna ta ce, "Watau ke ba za ki bi shi ba, sai shi ne zai bi ra'ayinki, ke kullum sai an yi artabu da ke? Kin taba ganin wanda ya bi iyayensa bai ci ribar rayuwarsa ba? Ashe ba za ki koyi da yayar ki ba?"
Ta sake kara sautin kukan ta ce, "Ai samun irin mijinta da yan'uwansa sai an tona a wannan lokacin, sannan kuma ni da ita akwai banbanci."
Takaicin ta ya kama Inna ta ce, "Banbanci kuwa a bayyane, ita ta yarda duk talaucinmu, mu ne iyayenta, za mu yi iko a kanta ba tare da ta ga gidadancinmu ba, sannan karatu kadan ta yi amma mai cike da ladabi da biyayya, in sha Allah Ubangiji ba zai kunyata ta ba."
Tana fadin hakan ta fita ta bar su da Baffa.
"Iyah!" Ya kira ta da muryar da bai saba mata irin ta ba, tunda shi kullum a cikin lallashi da tausasawa yake mata magana.
"Na riga da na zartar da maganar nan a gaban Mutari da iyayensa, ba zan koma na ce na fasa ba. Ko a fuska kika nunawa yaron nan tsarina bai miki ba, ki tabbatar kin nuna ban isa da ke ba, ba kuma zan sake yin iko akan ki ba."
Ya na rufe baki ya juya shi ma ya fice abinsa, sai ji ta yi kukan ya tsaya mata cak!
Amma wani irin ba'kin ciki take ji ya shake mata wuya da zuciya. Da 'kyar ta fita ta yi alwala ta yi sallar Maghrib da Isha wanda ba nutsuwa a cikinsu.
Da rarrafe ta isa kan shimfidarta, hawaye na bin fuskarta, ta ya ya za a mata irin wannan auren sai ka ce mutanen da? Ai ko shi Baffan da zai auri Innarsu, ya mata hidima, ita ma kuma da kayan dakinta aka kawo masa ita har yanzu gadonta na aure ne a dakin, duk kuwa da auren zumunci aka musu, shekaru kusan talatin. Amma sai ita a wannan lokacin za a mata irin wannan auren, kuka ya sake balle mata.😭
Tsawon lokaci tana kuka har kanta ya fara ciwo, a ranar dai ba ta yi wani cikakken barci ba, ba ta tuna matsalarta da MK ba sai da Asuba.
Tana idar da sallah ta ciro wayarta a caji ta lalubo lambar MK ta kira, har ta katse bai dauka ba, ta kira ya fi sau biyar amma bai amsa ba. ta ja wani dogon tsaki tana furta "Sai ka yi ta yi."
Ta kwanta ta yi shiru, amma sai ta kasa hakuri, ta sake kiran sa, nan ma bai dauka ba, ta yi ta kira har ta gaji, takaici ya sa ta yi jifa da wayar.
Har rana ta fito tana kwance ta ki fita, fishi sosai take yi, ga idanuwanta sun kunbura saboda tsabar kuka.
Inna kuwa ko ta kanta ba ta bi ba, ta yi dukkan ayyukanta, ta yi abin karin kumallo suka karya da Baffa amma ba ta nemi Iyah ba bare ta ba ta.
Sai da Baffa zai fita ne ya tsaya bakin kofar dakinta ya kira ta. Ta fito sanye da hijabi duk fuskar ta a kumbure, ta tsugunna ta gaishe shi, ya kalle ta cike da kulawa ya ce, "Iyata yau ban ji motsin ki ba ga shi har zan fita, kin san idan ban gan ki ba yini zan yi ba kuzari".
Ta sake yin kasa da kanta hawaye na cika mata ido, "maza fito ki yi wanka, ki sami abinci ki ci idan zan dawo zan taho miki da indomie har da Sadine na gwangwani, da ma kwanaki kin ce mini indominki ta 'kare, yau zan sayo miki ki ajiye a dakinki har da madara."
Cikin kuka ta ce, "Na gode"
Ya tafi yana jin kukan ta har cikin ransa, ya na raya yadda Sumayya ta zarta ta biyayya da gudun zuciya amma Iyah tafi shiga ransa matu'ka da gaske.
Ko da ta koma dakin sai ta sake dasa sabon kuka mai cike da kururuwa, yin sa take iya karfinta, fishin da MK ya dauka ya sake dagula mata lissafi.
Tun Inna na danne bacin ran ihun da Sa'adah ta cika mata kunne da shi, har ta kasa jurewa.
Don haka ta shiga 'daki ta samo wani danko mai kauri ta nada a hannunta, ta nufi dakinta, tana shiga kuwa ba bata lokaci ta shiga zabga matata ko ina, da iyakacin karfinta, da kyar Sa'adah ta kwace ta fice a guje, ta nufi hanyar zaure ta tsaya tana kuka sosai.
Ta dade kafin ta dawo gidan, tana rabe-rabe, Inna ta kalle ta rai a bace ta ce, " Idan kin san za ki ta sani a gaba kina mini kukan iyashege ki juya ki tafi duk inda za ki shiga, watau ni kika raina? Kin ga Baffanku ya fita shine za ki 'bude mini wannan ja'irin bakin naki da bai iya komai ba sai 'kulla karya da munafunci kina mini ihu. Wai har kin yi wayon da yafi nawa, ni za ki yiwa karyar Zainab za ki raka unguwa? Ashe da wannan shedanun kawayen naki masu yi wa Babba kallon raini kuka fita, har kin yi lalacewar da za ki shiga gaban motar namiji ya kawo ki har kofar gidanku, ki fito akan idon jama'a, oh ni Salamatu wacce irin yarinya nake tare da ita ne haka?"
Ta Fadi hakan tare da tafa hannu tana salati.
"Wai kuma don ki bata ni a gunsa shi ne zaki ce nasan zaki fita, to don uwarki daga yau kika kuskura kika ce mini za ki fita da sunan zuwa unguwa wallahi sai jikin ki ya fa'da miki. Na daina raga miki tunda ke rarrashi baya bi da ke, kafin nan kafin ki bar gidan nan sai na miki tabbuna ba ma tabo ba. Tunda nake da Baffanku bai taba ganin kasawa ta ba sai akan ki, jiya da daddare ba abin da bai fada mini ba, bayan an tabbatar masa a mota aka kawo ki."