Sashe 109
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai daf da magariba suka samu kansu, a gurguje ya yi wanka ya wuce masallaci, yana jinjinawa duk Namiji da yake da mace sama da guda, yake kuma tsaye dan ya yi adalci.
Sai da ya dawo ya fa'da mata Sa'adah zata tare ranar juma'ah mai zuwa, ita kuma zata tare juma'a ta sama.
A ranta ta ji ita ya kamata ta fara tarewa, tunda itace suke tare, bai kamata ace ita zata je ta tarar da Sa'adah ba, shikuma ya yi hakan ne dan ya tabbatar da Sa'a ce uwargida ba dan wani abin ba.
Amma sai ta ce "Allah ya Sanya alkhairi".
Ranar laraba aka gama shirya komai na bangaren Sa'adah! duk inda tsari da haduwa wurinta ya kai, a ko ina kuwa, ba kananun kuda'de aka fitar ba.
A ranar dai ta laraba Sa'a na zaune a tsakar gidansu ba hijabi a jikinta adalilin Inna ta je unguwa, ba zato ta ji sallamar Innar a tsakar gidan.
Gabanta ya yanke ya fa'di, ta hau dube duben Hijabinta ashe a 'daki ta barshi.
Zabura da waige-waigen da take yi ne ya ja hankalin Innah ta tsura mata ido, take ta gano abubuwa masu yawa da suka sauya a tare da Iyah.
Kirjinta ya matu'kar cika, sannan ta yi fari ta 'dashe tamkar mai shafa man bleaching, sanin da Innah ta yi duk kwalliyar Sa'a bata yarda ta canja launin fatarta ba.
Ta kalli fuskarta tana ganin yadda ta 'danyace, alamun dai mai shigar ciki 'karara.
Dabas Innah ta zauna tana hirji.
Ta jima tana kokawa da numfashi, sannan ta ce "mafarkina ne zai tabbata Iyah, ko kuwa yanzun ma mafarkin nake yi?"
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
*NA*
*SURAYYA DAHIRU*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
113-114.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*PROLOGUE*.
*Masoyan FARIDA*!
*Team FARIDA na so na ambato sunanku, sai na gane yawanku ba zai bari ba, Farida tana sonku, tana yaba muku, Ta ce na ce muku son so Fisabidillahi*.🥰
*MARUBUTA*
*Hajiya Saliha A.A Zaria*
*Hajiya Hafsat Sodangi*.
*Hajiya Maimuna Beli*
*Aunty Sumayya Takori*.
*Hajiya Zulaihatu Sani Kagara*
*SADIK ABUBAKAR*.
*Fadila lami'do*.
*Binta Abbale*.
*Hassana 'Danlarabawa*
*Maman Mama*.
*Ayusha Muhd*
*Kulsum Baffah Azare*
*Umm Azghar*.
*Gidan Iko*
*Asiyah(asi beauty)*
*Aisha jos*
*Hafsat Bature*
*Rabi'atu Shitu*
*Aysha Dansabo*.
*Da dukkan yan kungiyar lafazi writers da ma sauran marubuta gaba'daya*
*Ina godiya sosai tare da fatan alheri.* *Allah ya 'kara Basira.*
*Da* matu'kar kunya Sa'a ta ce "wanne irin mafarki kike magana Innah?"
"Kul kika yi mini iya-shege Iyah! Ai kin san dai mai nake nufi, mike tsaye na ganki soasai".
Ta 'ki mikewa sai 'boye jikinta da take yi.
Salati sosai Inna take tana cewa Ni dama na da'de ina mamakin yadda aka yi kika sauko har kina nuna zakuwar ki akan ki tare, dan munafunci har kina cemin wai saboda ra'ayina zaki ha'kura ki tare ko ba kayan daki, ashe ke kin tare ma kawai ankara ne ban yi ba.
To yanzu sai ki fa'da mini lokacin da kuka kunsa cikin dan asan ko auren na ku bai yiwu ba."
Da rawar murya Sa'a ta ce haba Innah yanzu sai ki yi tunanin zan iya yin wannan ta'asar?".
"To ina zan sani tunda daga ke har Muutar din ba mutunci ne da ku ba , bare kunya.
Wato shiyasa kullum sai kin san yadda Kika 'kirkiro fita, ko dai da sunan zuwa gurin aiki, ko wani uzzirin da ba za'a hana ki fita ba? Oh ina zaune anmayar da ni garmaho, ko a dakin nan kuka yi abin da kuka yi?"
Kuka Sa'adah ta saka, tana jin wata irin kunya tamkar ta tsaga kasa ta shige.
Ta kasa magana, tana jin haushin Mk da ya janyo mata wannan muzantar a idon uwarta.
Ana cikin hakan Baffah ya shigo ya ce "me ya samu uwata take kuka har da hawaye ne?"
"Kukan iskanci take yi, ba dama ta yi ba dai-dai ba, ayi magana sai ta bare ja'irin bakinta ta yi kuka tamkar yarinya kankanuwa."
"Me ta yi da ba zaki iya hakuri zuwa jibi ta tafi dakinta, itama hankalinta ya kwanta ba?"
"Hmmm! ciki ne da ita, daga na tambayeta yaushe suka yi cikin dan asan matsayin aurensu shine take wannan gunshekin kukan tamkar na daketa ne, ke kam wallahi kin ji kunya, ba dan ni na haife ki ba, da tuni ki ba'kanta ni a idon duniya".
Kunyar da Sa'a take ciki ta sake nunkuwa, dan haka ta sake 'kara sautin kukanta dan ta kawar da su daga sake kunyata ta.
Aikuwa dai Baffah ya ce "To ai a hankali zaki bita, ni na gasgata Iyah ba zata kunyatamu ba, ba ta yi shashanci a 'karancin shekarunta ba bare a yanzu da ta yi hankali, na kuma shaida Mutari ba zai ha'ince ni ba".
Wani irin farin-ciki ya kama Sa'adah tana gasgata Mk da ya ce Baffah Babansa ne ba nata ba.
Innah bata gasgata ta ba, amma Baffah ya shaideta ba zata yi Zina ba, haka ya shaidi Mukhtar ba zai lalata masa 'yah ba.
Kuma hasashen Baffah shine gaskiya.
Kawai Innah mafarkin da ta yi ne, yake sata wasiwasi.
Ya sassauta murya ya ce "Yi shiru ki mini bayani"
Ta kasa cewa komai saboda tsananin kunyar da ta tsinci kanta a ciki.
Ya juya ya fita yana cewa yanzu nan na hango shi ya zo unguwar bari na ji daga bakinsa.
Ganin Baffah ya fita! Ya saka Inna cigaba da sababinta, "munafukar banza, kika dinga cika bakin ba kya sonsa, kika yaudarar da ni da cewa ba zaki tare babu kayan daki ba, ashe kina zagayewa kuna abin da ranku ya so, saboda tsananin fitina da rashin kunya"
Daga ganin yadda kika aune, ansan ciki ya kwana biyu a jikinki, yo ina ganin HALIN YAU ni Salamatu!".
Sa'a ba baki sai kuka.
Baffah kuwa shagonsa ya 'kira Mk.
Cikin nutsuwa sosai ya ce "Mutari ka ce mini jibi juma'a Iya zata tare?"
Kai tsaye ya ce "Eh Baffah".
Ya numfasa ya ce "yanzu na shiga gidan na ji wani irin al'amari da ban fahimice shi ba, na tarar da Iyah da gyatumarsu a halin 'bacin rai saboda ta fahimci tana da juna biyu".
Mk ya mi'ke da sauri , zuciyar Baffa ta buga a tunaninsa kaduwa ya yi da jin maganar saboda ba shi da alaka da cikin.
Da azama Baffah ya ce "Ina zaka? Nutsu ka saurare ni, baka da alaka da cikin da yake jikinta ne?"
Ya koma ya zauna ba kunya ya ce"Haba Baffah! Ni fa zaburar da na yi, zuwa zan yi na fahimtar da Innah ta daina yi mata fa'da, Ni zata yiwa, tunda nine Babba! Domin na san kai zaka shedi ne ba zan yi lalata da jininka ba! Amma sai na ji kana tambayar ko bani da alaqa da al'amarin.
Kawai ayi ha'kuri Baffah! Abin da za a kallah a samu nutsuwa matatace, na kuma shaida akan ka'ida komai ya faru".
Hankali Baffah ya kwanta sosai ya ce "To Allah ya rufa asiri".
Mk ya mi'ke yana cewa "Yau ba doguwar hira Baffah na ji kunya ba ka'dan ba".
Murmushi Baffah ya yi tare da cewa "ja'iri da kana jin kunya da baka yi abin da ka yi ba".
Ya rufe shago ya koma gidan ya tarar har lokacin Innah na zubawa Sa'a sababi da gorin ta ji kunya, ta yi ciki a gida. Ita kuma sai kuka take yi tana jin takaicin abin da Mk ya janyo mata.
Baffah ya ce "Mayar da wukar ki Salamatu! Bata hanyar banza suka same shi ba, ni dama ina da kyakkawan Ya'kini a ziciyata baza suyi hakan ba".
Takaici ya kama Inna ta shige daki ta barshi da Iyah, tana Jin irin rarrashinta da yake yi, tamkar ba abin ayi mata kashedi ta yi ba.
Ranar juma'ah Mk da kansa ya zo ya dauki Sa'adah! A mota sai kuka take yi.
Sai da suka zo kofar famfo ya ce "Fisabidillahi kukan nan na menene? Na ro'ki karki bata mini Rai".
Tara saura suka isa, taga irin daular da aka shirya mata, ta rungumo shi tana ta fa'din thank you Malam"!.
Ya ce "ki yi hakuri ban samu damar yi miki lefe ba wannan karon ma, ki bini bashi, idan komai ya dai-daita zan yi Miki"
Kwana suka yi cikin farin-ciki mai yawa ha'din kai da soyayyar da Sa'a ta nunawa Mk yasa ya dinga hawaye ba tare da ya san yana yi ba.
Da sassafe ta tashi ta shirya masa irin kunun gyadan da tasan yana so tare da wainar rogo mai dadin gaske.
Ya tashi ya ganta ta yi wanka ta shirya cikin doguwar rigar shaddar da ta karbeta, cikin jikinta ya' kara mata kyau da yarinta.
Ya dinga kallonta, a zuciyarsa sai faman godiya ga ubangiji yake yi.
Ta ce "wannan kallon fa? Ka tashi ka yi wanka ka zo mu karya ni wallahi yunwa nake ji".
Ya diro daga gadon yana cewa "zo muje ki tayani wankan".
"Ni na riga dana shirya dan Allah ka yi sauri ka fito".
Ya wuce toilet din yana cewa to 'Ranki ya da'de".
Cikin kwanaki ukun da ya yi a gidanta wadda shari'a ta bashi, ba karamin soyayya ya nuna mata ba, ba irin rawar jikin da bai mata, shekarun bakwai din da suka shafe cikin tashin hankali da ba'kin ciki sai da ya wanke musu a cikin kwanakin, har Sa'adah take mamakin maganar Innah da tace idan ta yarda da shi kafin ta tare, ba zai yi 'dokinta ba.
Ga mamakin Mk ranar da zai koma wurin Farida yini ya yi cikin zullumin kada Sa'a ta botsare, amma har 'karfe shida na yammaci ta biye shi suna ta harkar arziki.
Da zai tafi, ya rungumeta ya ce" idan na yi sallah zan wuce gidan Hajiya, zan kaita unguwa wata'kila kafin na dawo kin yi barci".
Ta ce "ba damuwa ma hadu da safe".
Da'di ya kama shi, ya dinga kissing 'dinta.
Suka rabu 'kalau, yana murnar addu'ar da yake yi mata na samun sau'kin kishi ya fara ganin tasirinta.
Sai da ya dawo ya fa'da mata Sa'adah zata tare ranar juma'ah mai zuwa, ita kuma zata tare juma'a ta sama.
A ranta ta ji ita ya kamata ta fara tarewa, tunda itace suke tare, bai kamata ace ita zata je ta tarar da Sa'adah ba, shikuma ya yi hakan ne dan ya tabbatar da Sa'a ce uwargida ba dan wani abin ba.
Amma sai ta ce "Allah ya Sanya alkhairi".
Ranar laraba aka gama shirya komai na bangaren Sa'adah! duk inda tsari da haduwa wurinta ya kai, a ko ina kuwa, ba kananun kuda'de aka fitar ba.
A ranar dai ta laraba Sa'a na zaune a tsakar gidansu ba hijabi a jikinta adalilin Inna ta je unguwa, ba zato ta ji sallamar Innar a tsakar gidan.
Gabanta ya yanke ya fa'di, ta hau dube duben Hijabinta ashe a 'daki ta barshi.
Zabura da waige-waigen da take yi ne ya ja hankalin Innah ta tsura mata ido, take ta gano abubuwa masu yawa da suka sauya a tare da Iyah.
Kirjinta ya matu'kar cika, sannan ta yi fari ta 'dashe tamkar mai shafa man bleaching, sanin da Innah ta yi duk kwalliyar Sa'a bata yarda ta canja launin fatarta ba.
Ta kalli fuskarta tana ganin yadda ta 'danyace, alamun dai mai shigar ciki 'karara.
Dabas Innah ta zauna tana hirji.
Ta jima tana kokawa da numfashi, sannan ta ce "mafarkina ne zai tabbata Iyah, ko kuwa yanzun ma mafarkin nake yi?"
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️.
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
*NA*
*SURAYYA DAHIRU*.
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
113-114.
*SADAUKARWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
*PROLOGUE*.
*Masoyan FARIDA*!
*Team FARIDA na so na ambato sunanku, sai na gane yawanku ba zai bari ba, Farida tana sonku, tana yaba muku, Ta ce na ce muku son so Fisabidillahi*.🥰
*MARUBUTA*
*Hajiya Saliha A.A Zaria*
*Hajiya Hafsat Sodangi*.
*Hajiya Maimuna Beli*
*Aunty Sumayya Takori*.
*Hajiya Zulaihatu Sani Kagara*
*SADIK ABUBAKAR*.
*Fadila lami'do*.
*Binta Abbale*.
*Hassana 'Danlarabawa*
*Maman Mama*.
*Ayusha Muhd*
*Kulsum Baffah Azare*
*Umm Azghar*.
*Gidan Iko*
*Asiyah(asi beauty)*
*Aisha jos*
*Hafsat Bature*
*Rabi'atu Shitu*
*Aysha Dansabo*.
*Da dukkan yan kungiyar lafazi writers da ma sauran marubuta gaba'daya*
*Ina godiya sosai tare da fatan alheri.* *Allah ya 'kara Basira.*
*Da* matu'kar kunya Sa'a ta ce "wanne irin mafarki kike magana Innah?"
"Kul kika yi mini iya-shege Iyah! Ai kin san dai mai nake nufi, mike tsaye na ganki soasai".
Ta 'ki mikewa sai 'boye jikinta da take yi.
Salati sosai Inna take tana cewa Ni dama na da'de ina mamakin yadda aka yi kika sauko har kina nuna zakuwar ki akan ki tare, dan munafunci har kina cemin wai saboda ra'ayina zaki ha'kura ki tare ko ba kayan daki, ashe ke kin tare ma kawai ankara ne ban yi ba.
To yanzu sai ki fa'da mini lokacin da kuka kunsa cikin dan asan ko auren na ku bai yiwu ba."
Da rawar murya Sa'a ta ce haba Innah yanzu sai ki yi tunanin zan iya yin wannan ta'asar?".
"To ina zan sani tunda daga ke har Muutar din ba mutunci ne da ku ba , bare kunya.
Wato shiyasa kullum sai kin san yadda Kika 'kirkiro fita, ko dai da sunan zuwa gurin aiki, ko wani uzzirin da ba za'a hana ki fita ba? Oh ina zaune anmayar da ni garmaho, ko a dakin nan kuka yi abin da kuka yi?"
Kuka Sa'adah ta saka, tana jin wata irin kunya tamkar ta tsaga kasa ta shige.
Ta kasa magana, tana jin haushin Mk da ya janyo mata wannan muzantar a idon uwarta.
Ana cikin hakan Baffah ya shigo ya ce "me ya samu uwata take kuka har da hawaye ne?"
"Kukan iskanci take yi, ba dama ta yi ba dai-dai ba, ayi magana sai ta bare ja'irin bakinta ta yi kuka tamkar yarinya kankanuwa."
"Me ta yi da ba zaki iya hakuri zuwa jibi ta tafi dakinta, itama hankalinta ya kwanta ba?"
"Hmmm! ciki ne da ita, daga na tambayeta yaushe suka yi cikin dan asan matsayin aurensu shine take wannan gunshekin kukan tamkar na daketa ne, ke kam wallahi kin ji kunya, ba dan ni na haife ki ba, da tuni ki ba'kanta ni a idon duniya".
Kunyar da Sa'a take ciki ta sake nunkuwa, dan haka ta sake 'kara sautin kukanta dan ta kawar da su daga sake kunyata ta.
Aikuwa dai Baffah ya ce "To ai a hankali zaki bita, ni na gasgata Iyah ba zata kunyatamu ba, ba ta yi shashanci a 'karancin shekarunta ba bare a yanzu da ta yi hankali, na kuma shaida Mutari ba zai ha'ince ni ba".
Wani irin farin-ciki ya kama Sa'adah tana gasgata Mk da ya ce Baffah Babansa ne ba nata ba.
Innah bata gasgata ta ba, amma Baffah ya shaideta ba zata yi Zina ba, haka ya shaidi Mukhtar ba zai lalata masa 'yah ba.
Kuma hasashen Baffah shine gaskiya.
Kawai Innah mafarkin da ta yi ne, yake sata wasiwasi.
Ya sassauta murya ya ce "Yi shiru ki mini bayani"
Ta kasa cewa komai saboda tsananin kunyar da ta tsinci kanta a ciki.
Ya juya ya fita yana cewa yanzu nan na hango shi ya zo unguwar bari na ji daga bakinsa.
Ganin Baffah ya fita! Ya saka Inna cigaba da sababinta, "munafukar banza, kika dinga cika bakin ba kya sonsa, kika yaudarar da ni da cewa ba zaki tare babu kayan daki ba, ashe kina zagayewa kuna abin da ranku ya so, saboda tsananin fitina da rashin kunya"
Daga ganin yadda kika aune, ansan ciki ya kwana biyu a jikinki, yo ina ganin HALIN YAU ni Salamatu!".
Sa'a ba baki sai kuka.
Baffah kuwa shagonsa ya 'kira Mk.
Cikin nutsuwa sosai ya ce "Mutari ka ce mini jibi juma'a Iya zata tare?"
Kai tsaye ya ce "Eh Baffah".
Ya numfasa ya ce "yanzu na shiga gidan na ji wani irin al'amari da ban fahimice shi ba, na tarar da Iyah da gyatumarsu a halin 'bacin rai saboda ta fahimci tana da juna biyu".
Mk ya mi'ke da sauri , zuciyar Baffa ta buga a tunaninsa kaduwa ya yi da jin maganar saboda ba shi da alaka da cikin.
Da azama Baffah ya ce "Ina zaka? Nutsu ka saurare ni, baka da alaka da cikin da yake jikinta ne?"
Ya koma ya zauna ba kunya ya ce"Haba Baffah! Ni fa zaburar da na yi, zuwa zan yi na fahimtar da Innah ta daina yi mata fa'da, Ni zata yiwa, tunda nine Babba! Domin na san kai zaka shedi ne ba zan yi lalata da jininka ba! Amma sai na ji kana tambayar ko bani da alaqa da al'amarin.
Kawai ayi ha'kuri Baffah! Abin da za a kallah a samu nutsuwa matatace, na kuma shaida akan ka'ida komai ya faru".
Hankali Baffah ya kwanta sosai ya ce "To Allah ya rufa asiri".
Mk ya mi'ke yana cewa "Yau ba doguwar hira Baffah na ji kunya ba ka'dan ba".
Murmushi Baffah ya yi tare da cewa "ja'iri da kana jin kunya da baka yi abin da ka yi ba".
Ya rufe shago ya koma gidan ya tarar har lokacin Innah na zubawa Sa'a sababi da gorin ta ji kunya, ta yi ciki a gida. Ita kuma sai kuka take yi tana jin takaicin abin da Mk ya janyo mata.
Baffah ya ce "Mayar da wukar ki Salamatu! Bata hanyar banza suka same shi ba, ni dama ina da kyakkawan Ya'kini a ziciyata baza suyi hakan ba".
Takaici ya kama Inna ta shige daki ta barshi da Iyah, tana Jin irin rarrashinta da yake yi, tamkar ba abin ayi mata kashedi ta yi ba.
Ranar juma'ah Mk da kansa ya zo ya dauki Sa'adah! A mota sai kuka take yi.
Sai da suka zo kofar famfo ya ce "Fisabidillahi kukan nan na menene? Na ro'ki karki bata mini Rai".
Tara saura suka isa, taga irin daular da aka shirya mata, ta rungumo shi tana ta fa'din thank you Malam"!.
Ya ce "ki yi hakuri ban samu damar yi miki lefe ba wannan karon ma, ki bini bashi, idan komai ya dai-daita zan yi Miki"
Kwana suka yi cikin farin-ciki mai yawa ha'din kai da soyayyar da Sa'a ta nunawa Mk yasa ya dinga hawaye ba tare da ya san yana yi ba.
Da sassafe ta tashi ta shirya masa irin kunun gyadan da tasan yana so tare da wainar rogo mai dadin gaske.
Ya tashi ya ganta ta yi wanka ta shirya cikin doguwar rigar shaddar da ta karbeta, cikin jikinta ya' kara mata kyau da yarinta.
Ya dinga kallonta, a zuciyarsa sai faman godiya ga ubangiji yake yi.
Ta ce "wannan kallon fa? Ka tashi ka yi wanka ka zo mu karya ni wallahi yunwa nake ji".
Ya diro daga gadon yana cewa "zo muje ki tayani wankan".
"Ni na riga dana shirya dan Allah ka yi sauri ka fito".
Ya wuce toilet din yana cewa to 'Ranki ya da'de".
Cikin kwanaki ukun da ya yi a gidanta wadda shari'a ta bashi, ba karamin soyayya ya nuna mata ba, ba irin rawar jikin da bai mata, shekarun bakwai din da suka shafe cikin tashin hankali da ba'kin ciki sai da ya wanke musu a cikin kwanakin, har Sa'adah take mamakin maganar Innah da tace idan ta yarda da shi kafin ta tare, ba zai yi 'dokinta ba.
Ga mamakin Mk ranar da zai koma wurin Farida yini ya yi cikin zullumin kada Sa'a ta botsare, amma har 'karfe shida na yammaci ta biye shi suna ta harkar arziki.
Da zai tafi, ya rungumeta ya ce" idan na yi sallah zan wuce gidan Hajiya, zan kaita unguwa wata'kila kafin na dawo kin yi barci".
Ta ce "ba damuwa ma hadu da safe".
Da'di ya kama shi, ya dinga kissing 'dinta.
Suka rabu 'kalau, yana murnar addu'ar da yake yi mata na samun sau'kin kishi ya fara ganin tasirinta.