Sashe 9
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yanayin jikinta irin tauraruwar wasan kwaikwayon nan ce Hafsat Barauniya, duk da Hafsar ta fi ta shekaru, ta kuma fita hasken fata, kasancewar Sa'adah mai duhu ce, ba kuma ta yarda ta shafa man da zai canja mata launin kalarta ba,
illa tana 'batar da kud'a'de masu yawa wurin siyan tsadadden man dake fitowa da ainihin kalarta, ta goge ta yi tas da ita, ta yadda ko mace sai kin yi sha'awar launinta shi yasa idan akwai tambayar da a rana ana mata ya kai sau biyar, ita ce wanne mai ki ke shafawa, wanne mai ki ke amfani da shi? wani lokacin ta fa'da, wani lokacin kuma ta yi murmushi wushiryarta ta sake 'kawata ta tace "Vaseline"
Tana tsaye jikin Shoe Rack (ma'adanar takalman)ta ta fito da wani Tom's blue, Innarta ta shigo ta kalle ta ta ce, "To 'dawisu sarkin ado a wannan daren kike wannan kwallliyar anya Iya baza ki rage wannan 'kyale-'kyalen ba? Shi yasa ai da yawa mazan suna son zuwa gunki amma gani suke kin fi 'karfin su"
"Inna tunda ba ni na fa'da ba ai shi kenan, idan mutum da gaske son nawa yake ya zo mana idan mun daidaita ai zan aure shi ne"
"Yanzun kuma mai za ki yi da takalmi, da na ga kina gogewa? Na san dabi'ar ki ce ca'ba kwalliya ba sai za ki fita ba, amma wannan takalmi ai na fita ne, kuma kin san ba inda za ki a wannan daren"
"Kai Inna don Allah!" Ta fa'da cike da shagwaba, "Ni fa ba fita zan yi ba, ba'ko zan yi"
"Kin fa'da wa Baffanku za ki yi Ba'ko?"
Kai tsaye ta ce, "Na fada masa kafin ya tafi sallar Isha"
"Shi kenan amma don Allah Iya ki daina bata wa mutum lokaci kina kuma karbe mishi abin hannunsa alhalin kin san ba auren sa za ki yi ba,
yaudara ba kyau. Alhaji Mamman din nan ni ban ga laifinsa ba, mutum mai mutunci mai nagarta ga shi babba ne ya mallaki hankalinsa amma kina tasa 'kafa kina shure shi, kuma kina kar'be mai dukiya"
"In sha Allah, Inna ko mai ya kusa zuwa 'karshe, ki 'kara 'kaimi wurin yi mini addua"
Dadi ya kama uwar tata kusan yau ne Sa'adah ta bude baki ta yi magana mai kyau akan aure.
Nan da nan ta hau fa'din,
"Addu'a kam ai kullum yin ta nake, mantawa na ke da ko mai sai ke idan ina addu'a, Allah ya miki zabin alheri"
Ta fita tana sake cewa, "Ba abin da ke raina irin in gan ki a 'dakinki kin nutsu wuri daya"
Har sai da ta yi sallar Isha sannan ya mata waya ya iso. Fararen kujerun da ta tanada saboda zuwan wanda tabawa izini, ta 'diba ta fita dasu zauren gidan nasu da ke da yalwar fili, tana zuwa shi ma yana 'karasa shigowa, da sauri ya karbe kujerun yana cewa "Ai da kin sani kin jira na zo na 'debo, wannan ba aikin uwargidanmu ba ne"
Dariya ta yi, "Za ka fara ko?"
Shi ma dariyar ya yi, "Zan fara fa'din gaskiya ba"
komawa ta yi ta ha'do mishi ruwa (pure water) da kuma kunun ayan da Inna ke yi akan faranti tare da Tumbler, ta ajiye mishi tare da cewa "Ga ruwa"
Ya yi godiya ita kuma ta hau gaishe shi tare da tambayar iyalinshi, ya ba ta amsa da cewa, "Ai ta yi fishi da ke tace rabon da ki taka mata tun barkan haihuwar Kausar,
ga Kausar tana gudu ko Ina."
Ta ce, "Hidimar makaranta ce ta 'boye ni amma yanzu kam na gama za ta gan ni, a ba ta ha'kuri"
Sai da ya bude ruwa ya sha sannan ya yi gyaran murya ya ce, "Zuwan fa na mussaman ne, tare da albishir din abin da muka dade muna nema ya samu, takanas MK ya same ni ya ce mini ya kira ki, amma kin kashe mishi waya haka ne?"
Kai tsaye ta ce "E ai ban san shi ba ne"
"Ban gane ba ki san shi ba ne"?
"To bai gabatar da kansa ba,
ya fara maganganun da ban fahimce su ba".
Shiru ya yi tare da cewa
"Amma ba ki da lambarsa ne?"
"Ban da ita"
"Ba ki da ita?" Ya tambaye ta cike da mamaki.
"E!" Kawai tace ta ja bakinta ta tsuke.
Kamar zai bar maganar sai kuma ya ce, "Amma aikin haddace a kanki"
Nan ma ta ce, "Na manta"
Ya yi dariya, "Sa'adah wai yaushe kika cire mu a ranki har haka ne?"
Murmushi ta yi ta ce, "A lokacin da na fahimci ba komai ne idan ka rasa yake dawo maka ba, ba kuma komai ne kake so yake zama alheri ba"
Da sauri Dr. 'Karfi ya ce, "To mu dai alheri ne kuma mun dawo mu sake daukar ki a karo na biyu."
"Amma bai kama ta, ya manta cewar aure ya 'kare a tsakanin mu ba?"
Ta fa'da cikin 'daure fuska.
Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•
17-18.
" A a ban sani ba bai kuma fa'da mini ba."
'Karfi ya fa'da cikin yanayi na rashin gamsuwa, tare da zuba mata ido yana ta a uziya saboda yadda shaidan ke 'kawata mishi ita, ya riga ya binne wannan abin a ransa har abada ba zai yi tarayya da MK akan mace ba, macen da ya tabbatar amininshi yana mata son da bai yi wa kansa ba.
Ya numfasa ya 'kira sunanta,
"Sa'adah karki wahalar da ku, da ke da Mukhtar kuna son junanku, nan duniya ba abin da zai kankare wannan son, dole za a sami matsala a cikin zamantakewar aure, muhimmi shine ayi afuwa, a yafe, a kuma manta, amma ba za a iya kaucewa matsalar ba. ko wani sabon auren kipka yi komai jin da'din da za ki riska sai kin tarar da matsala"
Ya nisa sannan ya sake fa'din,
"Ina tabbatar miki kuma a yanzu ne ya fi dacewa ki koma dakinki, ba a wancan lokacin da ke kadai kike son komawar ba, yanzu da shi ya bukaci hakan da kansa za ki fi 'kima, ki fi daraja"
Sunkuyar da kai 'kasa ta yi hawaye na cika idonta, amma ba ta ce komai ba, ganin yadda jikinta ya yi sanyi, hakan ya 'kwarara guiwar 'Karfi.
Ya sake kur'bar ruwa ya ce, "Kar ki bari wannan damar ta kubuce miki, ina tabbatar miki, MK bai so wata mace kamar ki ba, kar ki bari rudin 'kawaye da zuciya su sake rudar ki a karo na biyu, wai ya yi aure, ko kaza da kaza, da duk abin da zai sake dagula miki lissafi.
Ki sa a ranki cewar ko kuna tare zai auri Farida! tunda an rubuta a cikin littafin 'kaddararshi cewar matarshi ce, mu gode Allah da ya kasance rabuwa ku ka yi, ba mutuwa kika yi ba, kin san akwai rabon da ke kashe mutum".
Hawayen da ta ke tattalawa ya zubo akan lallausar fuskarta, ta ce, "Ai ni sai daga baya na gano dama auren ya 'kallafa rai zai yi shi yasa ya yi ta zungurata, komai 'kankantar laifi sai ya juya shi ya zama garma, ashe dama akwai abin da ya 'kudure, to ya aureta hankalinshi ya kwanta, ni ma kuma ai bai jini a gadon asibitin mahaukata ba, bai kuma ji labarin auren nashi ya zama ajalina ba"
Kuka ya so kubuce mata saboda haka ta yi shiru sai rishin kukan kawai. Sai da ta nisa sannan ta sake dorawa da cewa, "Ni kuma nan duniya ban ga mai zai mini na ga farin shi ba"
Ta fada cikin dakewa da shanye kukan dake son kunyata ta. Jikin Mahmoud ya sake yin sanyi, ya yi shiru cikin rashin abin cewa.
Tsawon mintuna biyar kowa ya yi shiru a tsakaninsu sai fama suke da tunanin zuci.
Shudewar yan mintuna kafin ya ce, "Ni fa ba tone-tone za mu yi da ke ba, dukkanku, kowa da irin nashi laifin amma kin sani, laifin ki ya fi yawa"
Cikin takaici ta ce, "Baban Dadi tunda laifina yafi yawa, ai ya sake ni ya auro wacce ba za ta yi kuskure ba, wacce son da ake mata zai sa ayi ta mata uzirin ri'ke igiyar aurenta da kyau, sai dai a nuna mata kurenta cikin ladaftarwar da shari'a ta tanadar, shi yasa ni ma da na gane ba son nawa ake ba, kuma duk ni ce mai laifin sai na dau hukuncin da macen da ta san ciwon kanta za ta dauka don ta tsira daga ba'kin cikin namiji".
Shiru Mahmoud ya yi mata ya lura kishin Farida ne ya ke cinta shi yasa take ta furzar da magana, don haka ya 'kyale ta, at least dai za ta sami sau'kin ciwon dake addabar zuciyarta.
Sai da ta yi shiru don kanta, sannan yace"Ki yi ha'kuri, ki bi komai a sannu, ban hana ki nuna bacin ranki ba, amma kar ki wuce gona da iri, saboda kin san kema kin mishi laifin da sai da ya yi jinya bayan rabuwarku, tunda har ya sau'ko, to fa kar ki wuce makadi, ina fada miki wannan maganar ne a matsayin yayanki"
Ya dan numfasa, kana ya zarce da fadin, "Lamarin aure yanzu sai ha'kuri ba Perfect Marriage, kowanne aure da irin nashi 'kalubalen, duk abin da aka ce ibada ne, to fa sai an yi hakuri".
Ya mi'ke yana cewa, "Zan wuce, ki saurari zuwanmu!"
Hannu yasa a aljihunsa ya fito da yan dari biyar guda ashirin ya zuba kan kujerar daya tashi, da sauri ta ce, "Don Allah ka bar su, kullum a cikin hidima kake "
Murmushi ya yi yana cewa,
"Wannan kudin zance ne, ina fatan dai za a karbe mu da dukkannin raunin mu, kasancewar mu Malaman makaranta masu sadaukarwa, ba ma su satar kudin jama'a ba"
Ta san sarai inda maganar shi ta dosa, da Alhaji Mamman ya ke, tunda ya sha ganin ta da shi, wanda 'karara yake taya amininsa kishi.
illa tana 'batar da kud'a'de masu yawa wurin siyan tsadadden man dake fitowa da ainihin kalarta, ta goge ta yi tas da ita, ta yadda ko mace sai kin yi sha'awar launinta shi yasa idan akwai tambayar da a rana ana mata ya kai sau biyar, ita ce wanne mai ki ke shafawa, wanne mai ki ke amfani da shi? wani lokacin ta fa'da, wani lokacin kuma ta yi murmushi wushiryarta ta sake 'kawata ta tace "Vaseline"
Tana tsaye jikin Shoe Rack (ma'adanar takalman)ta ta fito da wani Tom's blue, Innarta ta shigo ta kalle ta ta ce, "To 'dawisu sarkin ado a wannan daren kike wannan kwallliyar anya Iya baza ki rage wannan 'kyale-'kyalen ba? Shi yasa ai da yawa mazan suna son zuwa gunki amma gani suke kin fi 'karfin su"
"Inna tunda ba ni na fa'da ba ai shi kenan, idan mutum da gaske son nawa yake ya zo mana idan mun daidaita ai zan aure shi ne"
"Yanzun kuma mai za ki yi da takalmi, da na ga kina gogewa? Na san dabi'ar ki ce ca'ba kwalliya ba sai za ki fita ba, amma wannan takalmi ai na fita ne, kuma kin san ba inda za ki a wannan daren"
"Kai Inna don Allah!" Ta fa'da cike da shagwaba, "Ni fa ba fita zan yi ba, ba'ko zan yi"
"Kin fa'da wa Baffanku za ki yi Ba'ko?"
Kai tsaye ta ce, "Na fada masa kafin ya tafi sallar Isha"
"Shi kenan amma don Allah Iya ki daina bata wa mutum lokaci kina kuma karbe mishi abin hannunsa alhalin kin san ba auren sa za ki yi ba,
yaudara ba kyau. Alhaji Mamman din nan ni ban ga laifinsa ba, mutum mai mutunci mai nagarta ga shi babba ne ya mallaki hankalinsa amma kina tasa 'kafa kina shure shi, kuma kina kar'be mai dukiya"
"In sha Allah, Inna ko mai ya kusa zuwa 'karshe, ki 'kara 'kaimi wurin yi mini addua"
Dadi ya kama uwar tata kusan yau ne Sa'adah ta bude baki ta yi magana mai kyau akan aure.
Nan da nan ta hau fa'din,
"Addu'a kam ai kullum yin ta nake, mantawa na ke da ko mai sai ke idan ina addu'a, Allah ya miki zabin alheri"
Ta fita tana sake cewa, "Ba abin da ke raina irin in gan ki a 'dakinki kin nutsu wuri daya"
Har sai da ta yi sallar Isha sannan ya mata waya ya iso. Fararen kujerun da ta tanada saboda zuwan wanda tabawa izini, ta 'diba ta fita dasu zauren gidan nasu da ke da yalwar fili, tana zuwa shi ma yana 'karasa shigowa, da sauri ya karbe kujerun yana cewa "Ai da kin sani kin jira na zo na 'debo, wannan ba aikin uwargidanmu ba ne"
Dariya ta yi, "Za ka fara ko?"
Shi ma dariyar ya yi, "Zan fara fa'din gaskiya ba"
komawa ta yi ta ha'do mishi ruwa (pure water) da kuma kunun ayan da Inna ke yi akan faranti tare da Tumbler, ta ajiye mishi tare da cewa "Ga ruwa"
Ya yi godiya ita kuma ta hau gaishe shi tare da tambayar iyalinshi, ya ba ta amsa da cewa, "Ai ta yi fishi da ke tace rabon da ki taka mata tun barkan haihuwar Kausar,
ga Kausar tana gudu ko Ina."
Ta ce, "Hidimar makaranta ce ta 'boye ni amma yanzu kam na gama za ta gan ni, a ba ta ha'kuri"
Sai da ya bude ruwa ya sha sannan ya yi gyaran murya ya ce, "Zuwan fa na mussaman ne, tare da albishir din abin da muka dade muna nema ya samu, takanas MK ya same ni ya ce mini ya kira ki, amma kin kashe mishi waya haka ne?"
Kai tsaye ta ce "E ai ban san shi ba ne"
"Ban gane ba ki san shi ba ne"?
"To bai gabatar da kansa ba,
ya fara maganganun da ban fahimce su ba".
Shiru ya yi tare da cewa
"Amma ba ki da lambarsa ne?"
"Ban da ita"
"Ba ki da ita?" Ya tambaye ta cike da mamaki.
"E!" Kawai tace ta ja bakinta ta tsuke.
Kamar zai bar maganar sai kuma ya ce, "Amma aikin haddace a kanki"
Nan ma ta ce, "Na manta"
Ya yi dariya, "Sa'adah wai yaushe kika cire mu a ranki har haka ne?"
Murmushi ta yi ta ce, "A lokacin da na fahimci ba komai ne idan ka rasa yake dawo maka ba, ba kuma komai ne kake so yake zama alheri ba"
Da sauri Dr. 'Karfi ya ce, "To mu dai alheri ne kuma mun dawo mu sake daukar ki a karo na biyu."
"Amma bai kama ta, ya manta cewar aure ya 'kare a tsakanin mu ba?"
Ta fa'da cikin 'daure fuska.
Alkalamin
SURAYYA DAHIRU
✍🏼✍🏼
🌺 *HALIN YAU*! 🌺
•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•
17-18.
" A a ban sani ba bai kuma fa'da mini ba."
'Karfi ya fa'da cikin yanayi na rashin gamsuwa, tare da zuba mata ido yana ta a uziya saboda yadda shaidan ke 'kawata mishi ita, ya riga ya binne wannan abin a ransa har abada ba zai yi tarayya da MK akan mace ba, macen da ya tabbatar amininshi yana mata son da bai yi wa kansa ba.
Ya numfasa ya 'kira sunanta,
"Sa'adah karki wahalar da ku, da ke da Mukhtar kuna son junanku, nan duniya ba abin da zai kankare wannan son, dole za a sami matsala a cikin zamantakewar aure, muhimmi shine ayi afuwa, a yafe, a kuma manta, amma ba za a iya kaucewa matsalar ba. ko wani sabon auren kipka yi komai jin da'din da za ki riska sai kin tarar da matsala"
Ya nisa sannan ya sake fa'din,
"Ina tabbatar miki kuma a yanzu ne ya fi dacewa ki koma dakinki, ba a wancan lokacin da ke kadai kike son komawar ba, yanzu da shi ya bukaci hakan da kansa za ki fi 'kima, ki fi daraja"
Sunkuyar da kai 'kasa ta yi hawaye na cika idonta, amma ba ta ce komai ba, ganin yadda jikinta ya yi sanyi, hakan ya 'kwarara guiwar 'Karfi.
Ya sake kur'bar ruwa ya ce, "Kar ki bari wannan damar ta kubuce miki, ina tabbatar miki, MK bai so wata mace kamar ki ba, kar ki bari rudin 'kawaye da zuciya su sake rudar ki a karo na biyu, wai ya yi aure, ko kaza da kaza, da duk abin da zai sake dagula miki lissafi.
Ki sa a ranki cewar ko kuna tare zai auri Farida! tunda an rubuta a cikin littafin 'kaddararshi cewar matarshi ce, mu gode Allah da ya kasance rabuwa ku ka yi, ba mutuwa kika yi ba, kin san akwai rabon da ke kashe mutum".
Hawayen da ta ke tattalawa ya zubo akan lallausar fuskarta, ta ce, "Ai ni sai daga baya na gano dama auren ya 'kallafa rai zai yi shi yasa ya yi ta zungurata, komai 'kankantar laifi sai ya juya shi ya zama garma, ashe dama akwai abin da ya 'kudure, to ya aureta hankalinshi ya kwanta, ni ma kuma ai bai jini a gadon asibitin mahaukata ba, bai kuma ji labarin auren nashi ya zama ajalina ba"
Kuka ya so kubuce mata saboda haka ta yi shiru sai rishin kukan kawai. Sai da ta nisa sannan ta sake dorawa da cewa, "Ni kuma nan duniya ban ga mai zai mini na ga farin shi ba"
Ta fada cikin dakewa da shanye kukan dake son kunyata ta. Jikin Mahmoud ya sake yin sanyi, ya yi shiru cikin rashin abin cewa.
Tsawon mintuna biyar kowa ya yi shiru a tsakaninsu sai fama suke da tunanin zuci.
Shudewar yan mintuna kafin ya ce, "Ni fa ba tone-tone za mu yi da ke ba, dukkanku, kowa da irin nashi laifin amma kin sani, laifin ki ya fi yawa"
Cikin takaici ta ce, "Baban Dadi tunda laifina yafi yawa, ai ya sake ni ya auro wacce ba za ta yi kuskure ba, wacce son da ake mata zai sa ayi ta mata uzirin ri'ke igiyar aurenta da kyau, sai dai a nuna mata kurenta cikin ladaftarwar da shari'a ta tanadar, shi yasa ni ma da na gane ba son nawa ake ba, kuma duk ni ce mai laifin sai na dau hukuncin da macen da ta san ciwon kanta za ta dauka don ta tsira daga ba'kin cikin namiji".
Shiru Mahmoud ya yi mata ya lura kishin Farida ne ya ke cinta shi yasa take ta furzar da magana, don haka ya 'kyale ta, at least dai za ta sami sau'kin ciwon dake addabar zuciyarta.
Sai da ta yi shiru don kanta, sannan yace"Ki yi ha'kuri, ki bi komai a sannu, ban hana ki nuna bacin ranki ba, amma kar ki wuce gona da iri, saboda kin san kema kin mishi laifin da sai da ya yi jinya bayan rabuwarku, tunda har ya sau'ko, to fa kar ki wuce makadi, ina fada miki wannan maganar ne a matsayin yayanki"
Ya dan numfasa, kana ya zarce da fadin, "Lamarin aure yanzu sai ha'kuri ba Perfect Marriage, kowanne aure da irin nashi 'kalubalen, duk abin da aka ce ibada ne, to fa sai an yi hakuri".
Ya mi'ke yana cewa, "Zan wuce, ki saurari zuwanmu!"
Hannu yasa a aljihunsa ya fito da yan dari biyar guda ashirin ya zuba kan kujerar daya tashi, da sauri ta ce, "Don Allah ka bar su, kullum a cikin hidima kake "
Murmushi ya yi yana cewa,
"Wannan kudin zance ne, ina fatan dai za a karbe mu da dukkannin raunin mu, kasancewar mu Malaman makaranta masu sadaukarwa, ba ma su satar kudin jama'a ba"
Ta san sarai inda maganar shi ta dosa, da Alhaji Mamman ya ke, tunda ya sha ganin ta da shi, wanda 'karara yake taya amininsa kishi.