Sashe 59
Halin Yau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Zuwa Gombe, ko yanzu kina iya tafiya, sai dai idan ina da hakki akan ki, ba za ki ga alheri a yayin tafiyar da dawowar ba in sha Allah".
Ya ja dogon tsaki yana fadin shashar yarinya da bata san mutunci da kyautatawa ba".
Ya sake jan dogon tsaki ya fice, ya barta tana kukan ita yake yi wa baki da mugun fata?.
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️
18/04
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*SADAUKAWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
75_77
Hannu ta 'dora aka ta dinga kuka,tana fadin "Hasbunallahi wa ni'imal wakil".
Har akayi azahar tana zaune inda take, ba abin da tasa a bakinta, duk da ga tiren abincin nan a gabanta, ba idonta kawai ba, hatta fuskar ta kumbura ta aune sosai saboda kuka, ta fada ta yi zuru zuru, ta dinga lissafin adadin rikicinsu, aduk fa'dan da zasu yi ita take janyowa, ta sake tuno adadin alherinsa hatta iyayenta bai huta da yi musu alheri ba, tun kafin ma ya aureta.
Ta sake tuna duk laifin da take ganin ya mata cikin biyu ne, ko dai kawai zuciyarta ta raya mata ya Mata kaza a matsayin musgunawa, sai wadda 'kawayenta zasu ce ya yi a makaranta, ko ya mayar da ita Bagidajiya, alhalin ita tasan yadda yake girmamata yake girmama dukkan ra'ayin ta, amma sai tunanin ta ya bace ta biye musu.
Ta tuna yadda yake tsananin son su zauna lafiya, su rayu cikin walwala da mutuntata juna, sai gashi yau da bakinsa yana la'antar zaman lafiya, yana fa'din bai yafe mata ba, idan ta zauna lafiya da shi.
Idan ta yi wadannan tunaninka sai ta rushe da kuka, tana yi tana cewa "wallahi da gaske na gane gaskiya".
'Kiran sallah ya sa ta tashi, ta yi alwallah ta yi sallah, ruwan Lipton kawai ta sha.
Tana zaune har dare! sallah ke tayar da ita, gefe kuma tana tunanin Jawad, da ya nan da ya debe mata kewa, yau kwanansa uku a gidan Samira, tunda suna hutu.
Akan idonta ya dawo, kusan a guje ta sha gabansa tana kuka, tana cewa "Dan Allah ka yi ha'kuri, ya girgiza da ganin yadda fuskarta ta koma a yini 'daya kacal, ta so bashi tausayi amma da ya tuna haka take idan tana son abu, da zarar ta samu muradinta kuma za ta sake kirkiro wata matsalar.
Ya dubeta ya ce "Ba ki fara kuka ba, sai burina na raba Safina da gararanba a titi ya cika"
Ta kalleshi a razane, bai damu ba ya ce "babban burina ta zame mini amarya, na tabbatar zan sami nutsuwa da ita, ki adana hawayenki zuwa wannan lokacin".
A gurin ta yi fa'duwar yan bori tana kuka tamkar yarinya har da tirza 'kafa irin yadda Jawad ya ke yi.
tsaki ya mata yana fadin "Ba kuka ba ko bubburwa za ki yi bai dame ni ba". Ya shige ya rufe kofarsa.
Washagari daga sallar asuba bai dawo gidan ba, hankalin ta ya tashi ba ka'dan ba, ta kalli agogo ta ga har karfe uku ta tabbatar yana shago tunda yau lahadi.
Abin duniya ya taru, ya mata yawa, idan ta tuna kalamunsa wai son Safina ya ke yi, sai taji tamkar ta shide, ta tuno yanayin halittar su daya, ko a makaranta ana yawan fadin dirin jikin su shigen iri daya ne, da gaske za ta iya daukan hankalinsa kenan?
Hawaye ya sake goce mata, karon farko da ta fara jin tsanar Safina a ranta, tana raya ba zata kuma ganin dariyarta ba, bare ta ga fuskar zama a gidanta
Maganar ta mata ciwo fiye da zaton mai zato.
Tana zaune ta ji wayarta ta hau kuwwa, da hanzari ta dauka, ganin Hajiyar Bichi ce, tun daga muryarta Hajiyar ta gane ba ta cikin sukuni.
"A kwance kike ne Sa'a? na ji muryarki ba walwala".
Duk yadda ta ke danne kukan sai da ya subuce mata, hankalin Hajiya ya tashi ta dinga tambayar ta dalili amma ta kasa yin magana, sai kukan kawai.
Dai dai lokacin kuma Mk na zaune dakin Hajiya yana cin alalan gwangwani da ya ji lafiyayyen manja da yaji.
Ta kashe wayarta ta zubawa Mk ido, tana jin takaicinsa na kamata, a kausashe tace "mai ya hada ka da Sa'a?"
A nutse ya ajiye cokalin hannunsa, ya kalleta yace "Me tace na yi mata?"
Ranta ya sake baci ta ce " Na tambaye ka, ka amsa mini da tambaya! Na lura da kai, ka mayar da ni shashar uwa, duk sadda ka sami matsala da matarka sai ka tattaro ka dawo da kwanon abincinka wurina saboda ka zubar mini da mutunci a idon yarinya, amma zan gyara".
Ya yi sukuri dan yasan gaskiya ta fada, yana yin hakan. A raunane yace "Hajiya ni fa ba abin da ya ha'damu, kinsan kuma yadda nake son 'dan'danon girkinki, dan na yi aure shikenan sai bazan ci ba?".
Ido kawai ta kafe shi da shi, tun yana murmushi har ya fara shafa 'keyarsa, yana jin kallon na shiga jikinsa, yana tuna lokutan baya na 'kuruciya, idan Hajiya ta musu irin wannan kallon take suke shiga hankalin su, saboda yadda ya 'kunshi abubuwa da yawa ba sai ta yi magana ba .
"Tashi ka kaini gidan, na ji ba'asin kukan da take ta faman yi, wa ya sani ma ko dukan ta ka yi".
"Haba Hajiya! Kinsan dai ban samu tarbiyar dukan mace ba, ita kukan banza ne da ita, duk sadda zuciyarta ta raya mata, kuka take yi, da dalili ko babu".
"Mahaukaciya ce ai".
Jin amsar Hajiya yasa shi yin shiru ya lura ranta a bace yake da shi, ya mi'ke ya dauki waya da mukallin motarsa da ke gefensa ya kalleta ya ce "Allah ya huci zuciyar ki Hajiya, ina jiran ki a mota".
Kozai kozai suka tarar da ita, cikin kwanaki uku kacal gaba'daya ta lalace, karon farko da Hajiya ta ganta kaca kaca, kullum fes zata tarar da ita, haka muhallinta.
Hajiya ta ka'du kwarai da yadda ta ganta, da sauri ta isa kusa da ita, ta ri'ke ta, ita kuma ganin ta sami mai rarrashinta yasa ta kwantar da kanta a jikin Hajiyan ta dinga rera kukan tamkar mai wa'ka.
Mamaki ya kama Mk! ya coge a bakin kofa yana kallon kukan shagwaba da iskanci a wurin Sa'adah, ta masa laifi, ta kai 'kararsa.
Ya na'de hannunsa a 'kirjinsa, yana sauraren 'korafin da ta ke rattabawa Hajiya! "kuskure na masa cikin rashin sani, na yarda na yi laifi, na bashi hakuri tamkar harsena zai tsinke ya ki ha'kura, yanzu kuma sai ya fara soyayya da kawata dan ya ci mini fuska ya kuma janyo mini raini"
Cikin kuka sosai take bayanin.
Hajiya ta rasa mai za tace! ta fahimci Sa'a ba 'karamin kishi ne da ita ba, kishin nata kuma ya zarce ka'ida, amma da ta lura har da 'kuruciya a kanta, sannan dabi'a ce ta matan YAU sawa miji ido da kuma 'dorawa kai zazzafan kishi tamkar wadda aka musu busharar an janye ayar da ta bawa maza damar auren abin da ya musu da'di, daga mata biyu, uku ko hudu.
A hankali ta ce "akan yana da budurwa ki ka maida kanki haka, Ina ruwan ki? ki daina sa ido ko bibiyarsa, ba ruwan ki da abin da yake yi matu'kar bai tauye miki hakkin ki ba, idan kuma ya na 'ketare dokokin shari'a wannan kuma tsakaninsa da ubangijinsa ne".
Kan Sa'adah na 'kasa tana ta kuka, kukan kuma shi yake tayar da hankalin Hajiya.
"Wai wannan kukan na menene haka Sa'a? Kin ga kuwa yadda fuskar ki duk ta aune?"
Murya a dakushe ta amsa da cewa "ki ce ya daina mini fishi, sannan idan na dafa abincin ya dinga ci".
Kafin Hajiya ta yi magana, Mk ya yi fit yace "Ni yaro ne da za ki dinga control 'dina? Na 'ki na ci abincin na ki"
"Kin ji da kunnen ki ban isa da shi ba, dan haka ki share hawayen ki, komai da ki kasan hak'kinsa ne ki masa kar ki gaji, ubangiji ne yace ki masa biyayya, idan ya zalunce ki, ba zai barshi ba".
Ta mike tana gyara zaman Hijabin ta, ta sake cewa "Ki yi hakuri, kar ki biye masa, kinsan idan tururuwa ta so lalacewa fuffuka take yi, Allah ya miki albarka kin ji! Ki tashi ki yi wanka ki ji da'din jikin ki".
Ta juya ta fita ba tare da tabi ta kan Mk ba, da ya bita a baya yana cewa "Hajiya! ko kula shi bata yi ba ta yi ba, a waje juyin duniya akan ta shiga motarsa ya kaita, kamar yadda ya kawota, ta 'ki bude baki ta masa magana bare ta amince, haka ya dinga bin ta har titi, ta tari adaidaita sahu tana shiga, shima ya yi wuf ya fa'da, har suka isa Na'ibawa ba abin da ya ke yi sai tunanin mai zai yiwa Sa'adah ya huce.
Ba zai iya tuna lokacin da Hajiya ta masa irin wannan fishin ba.
Suna isa ta sau'ko ta wuce gida, ya tsaya ya biya kudin, sannan ya bita cikin gidan
Yana isa ya tarar da ita zaune a tsakar gidan, bata shiga dakinta ba tabbacin ba zata saurare shi ba.
Ya tsugunna, ya dinga bata ha'kuri, ya dade yana fama, kafin ta ce "Nunawa ka yi fa ban isa na zartar da abu a kanka ba, ganin na isa ne yasa ta ce na yi maka magana, kai kuma ka bata amsa da ta ke nufin ban isa ba, dan haka duk ranar da Sa'a ta fara ganina ba 'kima kar ka ga laifin ta".
Ya yi shiru yana ayyana wai su mata haka suke ne? manya da yaransu sun iya kacaccala magana, su juya ta, komin gaskiyar ka sai sun nuna su ka zalinta ko ka ketawa haddi?
Kan dole ya ce "Ki yi hakuri Hajiya Dan Allah! sannan ina tabbatar miki da ikon Allah ba macen da zan zauna da ita alhalin bata ganin girman ki".
"Fatana ki huce, ki yafe mini bacin ran da na sanya ki".
Ya ja dogon tsaki yana fadin shashar yarinya da bata san mutunci da kyautatawa ba".
Ya sake jan dogon tsaki ya fice, ya barta tana kukan ita yake yi wa baki da mugun fata?.
SURAYYA DAHIRU
✍️✍️
18/04
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️
____________(✪)______________
https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*SADAUKAWA GA*
*SADIK ABUBAKAR*.
75_77
Hannu ta 'dora aka ta dinga kuka,tana fadin "Hasbunallahi wa ni'imal wakil".
Har akayi azahar tana zaune inda take, ba abin da tasa a bakinta, duk da ga tiren abincin nan a gabanta, ba idonta kawai ba, hatta fuskar ta kumbura ta aune sosai saboda kuka, ta fada ta yi zuru zuru, ta dinga lissafin adadin rikicinsu, aduk fa'dan da zasu yi ita take janyowa, ta sake tuno adadin alherinsa hatta iyayenta bai huta da yi musu alheri ba, tun kafin ma ya aureta.
Ta sake tuna duk laifin da take ganin ya mata cikin biyu ne, ko dai kawai zuciyarta ta raya mata ya Mata kaza a matsayin musgunawa, sai wadda 'kawayenta zasu ce ya yi a makaranta, ko ya mayar da ita Bagidajiya, alhalin ita tasan yadda yake girmamata yake girmama dukkan ra'ayin ta, amma sai tunanin ta ya bace ta biye musu.
Ta tuna yadda yake tsananin son su zauna lafiya, su rayu cikin walwala da mutuntata juna, sai gashi yau da bakinsa yana la'antar zaman lafiya, yana fa'din bai yafe mata ba, idan ta zauna lafiya da shi.
Idan ta yi wadannan tunaninka sai ta rushe da kuka, tana yi tana cewa "wallahi da gaske na gane gaskiya".
'Kiran sallah ya sa ta tashi, ta yi alwallah ta yi sallah, ruwan Lipton kawai ta sha.
Tana zaune har dare! sallah ke tayar da ita, gefe kuma tana tunanin Jawad, da ya nan da ya debe mata kewa, yau kwanansa uku a gidan Samira, tunda suna hutu.
Akan idonta ya dawo, kusan a guje ta sha gabansa tana kuka, tana cewa "Dan Allah ka yi ha'kuri, ya girgiza da ganin yadda fuskarta ta koma a yini 'daya kacal, ta so bashi tausayi amma da ya tuna haka take idan tana son abu, da zarar ta samu muradinta kuma za ta sake kirkiro wata matsalar.
Ya dubeta ya ce "Ba ki fara kuka ba, sai burina na raba Safina da gararanba a titi ya cika"
Ta kalleshi a razane, bai damu ba ya ce "babban burina ta zame mini amarya, na tabbatar zan sami nutsuwa da ita, ki adana hawayenki zuwa wannan lokacin".
A gurin ta yi fa'duwar yan bori tana kuka tamkar yarinya har da tirza 'kafa irin yadda Jawad ya ke yi.
tsaki ya mata yana fadin "Ba kuka ba ko bubburwa za ki yi bai dame ni ba". Ya shige ya rufe kofarsa.
Washagari daga sallar asuba bai dawo gidan ba, hankalin ta ya tashi ba ka'dan ba, ta kalli agogo ta ga har karfe uku ta tabbatar yana shago tunda yau lahadi.
Abin duniya ya taru, ya mata yawa, idan ta tuna kalamunsa wai son Safina ya ke yi, sai taji tamkar ta shide, ta tuno yanayin halittar su daya, ko a makaranta ana yawan fadin dirin jikin su shigen iri daya ne, da gaske za ta iya daukan hankalinsa kenan?
Hawaye ya sake goce mata, karon farko da ta fara jin tsanar Safina a ranta, tana raya ba zata kuma ganin dariyarta ba, bare ta ga fuskar zama a gidanta
Maganar ta mata ciwo fiye da zaton mai zato.
Tana zaune ta ji wayarta ta hau kuwwa, da hanzari ta dauka, ganin Hajiyar Bichi ce, tun daga muryarta Hajiyar ta gane ba ta cikin sukuni.
"A kwance kike ne Sa'a? na ji muryarki ba walwala".
Duk yadda ta ke danne kukan sai da ya subuce mata, hankalin Hajiya ya tashi ta dinga tambayar ta dalili amma ta kasa yin magana, sai kukan kawai.
Dai dai lokacin kuma Mk na zaune dakin Hajiya yana cin alalan gwangwani da ya ji lafiyayyen manja da yaji.
Ta kashe wayarta ta zubawa Mk ido, tana jin takaicinsa na kamata, a kausashe tace "mai ya hada ka da Sa'a?"
A nutse ya ajiye cokalin hannunsa, ya kalleta yace "Me tace na yi mata?"
Ranta ya sake baci ta ce " Na tambaye ka, ka amsa mini da tambaya! Na lura da kai, ka mayar da ni shashar uwa, duk sadda ka sami matsala da matarka sai ka tattaro ka dawo da kwanon abincinka wurina saboda ka zubar mini da mutunci a idon yarinya, amma zan gyara".
Ya yi sukuri dan yasan gaskiya ta fada, yana yin hakan. A raunane yace "Hajiya ni fa ba abin da ya ha'damu, kinsan kuma yadda nake son 'dan'danon girkinki, dan na yi aure shikenan sai bazan ci ba?".
Ido kawai ta kafe shi da shi, tun yana murmushi har ya fara shafa 'keyarsa, yana jin kallon na shiga jikinsa, yana tuna lokutan baya na 'kuruciya, idan Hajiya ta musu irin wannan kallon take suke shiga hankalin su, saboda yadda ya 'kunshi abubuwa da yawa ba sai ta yi magana ba .
"Tashi ka kaini gidan, na ji ba'asin kukan da take ta faman yi, wa ya sani ma ko dukan ta ka yi".
"Haba Hajiya! Kinsan dai ban samu tarbiyar dukan mace ba, ita kukan banza ne da ita, duk sadda zuciyarta ta raya mata, kuka take yi, da dalili ko babu".
"Mahaukaciya ce ai".
Jin amsar Hajiya yasa shi yin shiru ya lura ranta a bace yake da shi, ya mi'ke ya dauki waya da mukallin motarsa da ke gefensa ya kalleta ya ce "Allah ya huci zuciyar ki Hajiya, ina jiran ki a mota".
Kozai kozai suka tarar da ita, cikin kwanaki uku kacal gaba'daya ta lalace, karon farko da Hajiya ta ganta kaca kaca, kullum fes zata tarar da ita, haka muhallinta.
Hajiya ta ka'du kwarai da yadda ta ganta, da sauri ta isa kusa da ita, ta ri'ke ta, ita kuma ganin ta sami mai rarrashinta yasa ta kwantar da kanta a jikin Hajiyan ta dinga rera kukan tamkar mai wa'ka.
Mamaki ya kama Mk! ya coge a bakin kofa yana kallon kukan shagwaba da iskanci a wurin Sa'adah, ta masa laifi, ta kai 'kararsa.
Ya na'de hannunsa a 'kirjinsa, yana sauraren 'korafin da ta ke rattabawa Hajiya! "kuskure na masa cikin rashin sani, na yarda na yi laifi, na bashi hakuri tamkar harsena zai tsinke ya ki ha'kura, yanzu kuma sai ya fara soyayya da kawata dan ya ci mini fuska ya kuma janyo mini raini"
Cikin kuka sosai take bayanin.
Hajiya ta rasa mai za tace! ta fahimci Sa'a ba 'karamin kishi ne da ita ba, kishin nata kuma ya zarce ka'ida, amma da ta lura har da 'kuruciya a kanta, sannan dabi'a ce ta matan YAU sawa miji ido da kuma 'dorawa kai zazzafan kishi tamkar wadda aka musu busharar an janye ayar da ta bawa maza damar auren abin da ya musu da'di, daga mata biyu, uku ko hudu.
A hankali ta ce "akan yana da budurwa ki ka maida kanki haka, Ina ruwan ki? ki daina sa ido ko bibiyarsa, ba ruwan ki da abin da yake yi matu'kar bai tauye miki hakkin ki ba, idan kuma ya na 'ketare dokokin shari'a wannan kuma tsakaninsa da ubangijinsa ne".
Kan Sa'adah na 'kasa tana ta kuka, kukan kuma shi yake tayar da hankalin Hajiya.
"Wai wannan kukan na menene haka Sa'a? Kin ga kuwa yadda fuskar ki duk ta aune?"
Murya a dakushe ta amsa da cewa "ki ce ya daina mini fishi, sannan idan na dafa abincin ya dinga ci".
Kafin Hajiya ta yi magana, Mk ya yi fit yace "Ni yaro ne da za ki dinga control 'dina? Na 'ki na ci abincin na ki"
"Kin ji da kunnen ki ban isa da shi ba, dan haka ki share hawayen ki, komai da ki kasan hak'kinsa ne ki masa kar ki gaji, ubangiji ne yace ki masa biyayya, idan ya zalunce ki, ba zai barshi ba".
Ta mike tana gyara zaman Hijabin ta, ta sake cewa "Ki yi hakuri, kar ki biye masa, kinsan idan tururuwa ta so lalacewa fuffuka take yi, Allah ya miki albarka kin ji! Ki tashi ki yi wanka ki ji da'din jikin ki".
Ta juya ta fita ba tare da tabi ta kan Mk ba, da ya bita a baya yana cewa "Hajiya! ko kula shi bata yi ba ta yi ba, a waje juyin duniya akan ta shiga motarsa ya kaita, kamar yadda ya kawota, ta 'ki bude baki ta masa magana bare ta amince, haka ya dinga bin ta har titi, ta tari adaidaita sahu tana shiga, shima ya yi wuf ya fa'da, har suka isa Na'ibawa ba abin da ya ke yi sai tunanin mai zai yiwa Sa'adah ya huce.
Ba zai iya tuna lokacin da Hajiya ta masa irin wannan fishin ba.
Suna isa ta sau'ko ta wuce gida, ya tsaya ya biya kudin, sannan ya bita cikin gidan
Yana isa ya tarar da ita zaune a tsakar gidan, bata shiga dakinta ba tabbacin ba zata saurare shi ba.
Ya tsugunna, ya dinga bata ha'kuri, ya dade yana fama, kafin ta ce "Nunawa ka yi fa ban isa na zartar da abu a kanka ba, ganin na isa ne yasa ta ce na yi maka magana, kai kuma ka bata amsa da ta ke nufin ban isa ba, dan haka duk ranar da Sa'a ta fara ganina ba 'kima kar ka ga laifin ta".
Ya yi shiru yana ayyana wai su mata haka suke ne? manya da yaransu sun iya kacaccala magana, su juya ta, komin gaskiyar ka sai sun nuna su ka zalinta ko ka ketawa haddi?
Kan dole ya ce "Ki yi hakuri Hajiya Dan Allah! sannan ina tabbatar miki da ikon Allah ba macen da zan zauna da ita alhalin bata ganin girman ki".
"Fatana ki huce, ki yafe mini bacin ran da na sanya ki".